< Markus 1 >
1 Farkon bishara game da Yesu Kiristi, Ɗan Allah.
The beginning of the gospel of JESUS CHRIST the Son of GOD.
2 An rubuta a cikin littafin annabi Ishaya cewa, “Zan aika da ɗan aikena yă sha gabanka, wanda zai shirya hanyarka,”
As it is written in the prophets, "Behold, I send my messenger before thy face, who shall prepare thy way before thee:"
3 “muryar mai kira a hamada tana cewa, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.’”
and again, "The voice of one crying in the wilderness, Prepare ye the way of the Lord, make his paths straight:" accordingly John came baptizing in the wilderness,
4 Ta haka Yohanna ya zo, yana baftisma a yankin hamada, yana kuma wa’azin baftismar tuba don gafarar zunubai.
and preaching the baptism of repentance in order to the remission of sins;
5 Dukan ƙauyukan Yahudiya da dukan mutanen Urushalima suka fiffito zuwa wurinsa. Suna furta zunubansu, ya kuwa yi musu baftisma a Kogin Urdun.
and all the country of Judea, and those of Jerusalem, went out to him, and were all baptized by him in the river Jordan, confessing their sins.
6 Yohanna ya sa tufafin gashin raƙumi, ya kuma yi ɗamara da fata. Abincinsa fāri ne da kuma zumar jeji.
And John was clothed with camels hair, and a leathern girdle about his loins, and he lived upon locusts and wild honey: and he preached,
7 Wannan kuwa shi ne saƙonsa, “A bayana, wanda ya fi ni iko yana zuwa, ban kuwa isa in sunkuya in kunce igiyar takalmansa ba.
saying, There cometh after me one mightier than I, the latchet of whose shoes I am not worthy to stoop and unloose.
8 Ina muku baftisma da ruwa, amma shi zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”
I indeed have baptized you with water, but He will baptize you with the holy Spirit.
9 A lokacin, Yesu ya zo daga Nazaret na Galili, Yohanna kuwa ya yi masa baftisma a Urdun.
And in those days Jesus came from Nazareth of Galilee, and was baptized by John in Jordan:
10 Da Yesu yana fitowa daga ruwan, sai ya ga sama ya buɗe, Ruhu kuma yana saukowa a kansa kamar kurciya.
and as soon as He came up from the water, he saw the heavens opened, and the Spirit like a dove descending upon Him.
11 Sai murya ta fito daga sama ta ce, “Kai ne Ɗana, wanda nake ƙauna, da kai kuma nake fari ciki ƙwarai.”
And there was a voice from heaven, saying, This is my beloved Son, in whom I am well pleased.
12 Nan da nan, sai Ruhu ya kai shi cikin hamada,
And immediately the Spirit taketh Him out into the wilderness:
13 ya kuma kasance a hamada kwana arba’in, Shaiɗan yana gwada shi. Yana tare da namomin jeji, mala’iku kuma suka yi masa hidima.
and He was there in the wilderness forty days tempted by Satan, and among the wild beasts: and angels ministred unto Him.
14 Bayan da aka sa Yohanna a kurkuku, sai Yesu ya shigo cikin Galili, yana shelar bisharar Allah.
Now after John was cast into prison, Jesus came into Galilee, preaching the gospel of the kingdom of God,
15 Yana cewa, “Lokaci ya yi. Mulkin Allah ya yi kusa. Ku tuba, ku gaskata bishara!”
and saying, The time is fulfilled, and the kingdom of God is at hand: repent, and believe the gospel.
16 Yayinda Yesu yake tafiya a gaɓar Tekun Galili, sai ya ga Siman da ɗan’uwansa Andarawus, suna jefa abin kamun kifi a cikin tafkin, domin su masunta ne.
And as He was walking by the sea of Galilee, He saw Simon and Andrew his brother, casting a net into the sea,
17 Yesu ya ce, “Ku zo, ku bi ni, ni kuwa zan mai da ku masuntan mutane.”
(for they were fishermen, ) and Jesus said unto them, Come after me, and I will make you fishers of men:
18 Nan da nan, suka bar abin kamun kifinsu, suka bi shi.
and immediately they left their nets and followed Him.
19 Da ya yi gaba kaɗan, sai ya ga Yaƙub ɗan Zebedi, da ɗan’uwansa Yohanna a cikin jirgin ruwa, suna gyaran abin kamun kifinsu.
And going a little farther, He saw James the son of Zebedee, and John his brother, in a ship, mending their nets, and immediately called them likewise:
20 Ba da ɓata lokaci ba, ya kira su, sai suka bar mahaifinsu Zebedi a cikin jirgin ruwan, tare da’yan haya, suka kuwa bi shi.
and they left their father Zebedee in the ship with the men he had hired, and went along with Him.
21 Suka tafi Kafarnahum. Da ranar Asabbaci ta kewayo, sai Yesu ya shiga majami’a ya fara koyarwa.
And they went into Capernaum: and going directly into the synagogue on the sabbath, He taught the people: and they were astonished at his doctrine;
22 Mutane suka yi mamakin koyarwarsa, domin ya koyar da su kamar wanda yake da iko, ba kamar malaman dokoki ba.
for He taught them as one that had authority, and not as the scribes.
23 Nan take, sai wani mutum mai mugun ruhu a majami’arsu, ya ɗaga murya ya ce,
And there was in their synagogue a man with an impure spirit,
24 “Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne don ka hallaka mu? Na san wane ne kai, Mai Tsarki nan na Allah!”
and he cried out, saying, Let us alone, what have we to do with thee, Jesus of Nazareth? art thou come to destroy us? I know thee, who thou art, the holy one of God.
25 Yesu ya tsawata masa ya ce, “Yi shiru! Fita daga cikinsa!”
And Jesus rebuked him, saying, Be silent, and come out of him: and the impure spirit threw him into convulsions,
26 Sai mugun ruhun ya jijjiga mutumin da ƙarfi, ya fita daga jikinsa da ihu.
and roaring with a loud voice, came out of him.
27 Dukan mutane suka yi mamaki, suna tambayar juna suna cewa, “Mene ne haka? Tabɗi! Yau ga sabuwar koyarwa kuma da iko! Yana ma ba wa mugayen ruhohi umarni, suna kuma yin masa biyayya.”
And they were all amazed, so that they inquired of each other, saying, What is this, what new kind of doctrine is this? for He commands with authority even the impure spirits, and they obey Him.
28 Labari game da shi ya bazu nan da nan ko’ina a dukan yankin Galili.
And straitway his fame spread into all the country round about Galilee.
29 Da suka bar majami’ar, sai suka tafi gidan su Siman da Andarawus, tare da Yaƙub da Yohanna.
And as soon as they came out of the synagogue, they went into the house of Simon and Andrew, together with James and John.
30 Surukar Siman tana kwance da zazzaɓi, sai suka gaya wa Yesu game da ita.
And Simon's wife's mother lay sick of a fever: and they immediately told Him of her:
31 Sai ya je wajenta, ya kama hannunta, ya ɗaga ta. Zazzaɓin kuwa ya sāke ta, ta kuma yi musu hidima.
and He came to her, and taking her by the hand raised her up; and immediately the fever left her, and she waited upon them.
32 A wannan yamma, bayan fāɗuwar rana, mutane suka kawo wa Yesu dukan marasa lafiya, da masu aljanu.
And in the evening, when the sun set, they brought to Him all that were ill, and demoniacs:
33 Duk garin ya taru a ƙofar gidan.
and the whole city was gathered together at the door;
34 Yesu kuwa ya warkar da marasa lafiya da yawa da suke da cututtuka iri-iri. Ya kuma fitar da aljanu da yawa, amma bai yarda aljanun suka yi magana ba, don sun san wane ne shi.
and He healed many that were ill of various diseases, and cast out many devils, and suffered not the devils to say that they knew Him.
35 Da sassafe, tun da sauran duhu, Yesu ya tashi, ya bar gida, ya tafi wani wurin da ba kowa, a can ya yi addu’a.
And in the morning, before it was light, He rose up and went out, and retired into a solitary place, and there prayed.
36 Siman da abokansa suka fita nemansa.
And Simon, and they that were with him, went in quest of Him:
37 Da suka same shi, sai suka ce, “Kowa yana nemanka!”
and when they found Him, they said to Him, all the people are seeking for thee.
38 Yesu ya amsa ya ce, “Mu je wani wuri dabam, zuwa ƙauyukan da suke kusa, don in yi wa’azi a can ma. Wannan shi ne dalilin zuwana.”
And He saith unto them, Let us go into the neighbouring towns, that I may preach there also; for this was the end of my coming.
39 Sai ya tafi ko’ina a Galili, yana wa’azi a majami’unsu, yana kuma fitar da aljanu.
And He went preaching in their synagogues, through all Galilee, and casting out devils.
40 Wani mutum mai kuturta ya zo wurinsa, ya durƙusa ya roƙe shi ya ce, “In kana so, za ka iya tsabtacce ni.”
And there came to Him a leper, beseeching Him, and kneeling down to Him, and saying unto Him, If thou wilt, thou canst cleanse me:
41 Cike da tausayi, sai Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka tsabtacce!”
and Jesus, being moved with compassion, stretched out his hand and touched him, and saith unto Him, I will;
42 Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi, ya kuma warke.
be thou healed: and as soon as He had spoken, immediately the leprosy left him, and he was healed.
43 Yesu ya sallame shi nan take, da gargaɗi mai ƙarfi cewa,
And he gave him a strict charge, and immediately dismissed him,
44 “Ka lura kada ka gaya wa kowa wannan. Amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayun da Musa ya umarta saboda tsarkakewarka, don yă zama shaida gare su.”
and saith unto him, See thou tell no man: but go, shew thyself to the priest, and offer for thy purification what Moses has commanded, for a testimony to them.
45 A maimakon haka, sai ya fita, ya fara magana a sake, yana baza labarin. Saboda haka, Yesu bai ƙara iya shiga cikin gari a fili ba, sai dai ya kasance a wuraren da ba kowa. Duk da haka, mutane suka yi ta zuwa wurinsa daga ko’ina.
But when he was gone he began to publish it much, and to spread abroad the report: so that Jesus could no more go openly into the city, but kept out in country places: and they came to Him from all parts.