< Markus 1 >

1 Farkon bishara game da Yesu Kiristi, Ɗan Allah.
The beginning of the gospel of Jesus Christ, Son of God.
2 An rubuta a cikin littafin annabi Ishaya cewa, “Zan aika da ɗan aikena yă sha gabanka, wanda zai shirya hanyarka,”
As it is written in Isaiah the Prophet, "Behold, I send my messenger before thee, who shall prepare thy way:"
3 “muryar mai kira a hamada tana cewa, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.’”
"The voice of one proclaiming in the wilderness, Prepare a way for the Lord, make for him a straight passage:"
4 Ta haka Yohanna ya zo, yana baftisma a yankin hamada, yana kuma wa’azin baftismar tuba don gafarar zunubai.
thus came John immersing in the wilderness, and publishing the immersion of reformation for the remission of sins.
5 Dukan ƙauyukan Yahudiya da dukan mutanen Urushalima suka fiffito zuwa wurinsa. Suna furta zunubansu, ya kuwa yi musu baftisma a Kogin Urdun.
And all the country of Judea, and the inhabitants of Jerusalem, resorted to him, and were immersed by him in the river Jordan, confessing their sins.
6 Yohanna ya sa tufafin gashin raƙumi, ya kuma yi ɗamara da fata. Abincinsa fāri ne da kuma zumar jeji.
Now John's clothing was of camel's hair, tied around his waist with a leather girdle: and he lived upon locusts and wild honey.
7 Wannan kuwa shi ne saƙonsa, “A bayana, wanda ya fi ni iko yana zuwa, ban kuwa isa in sunkuya in kunce igiyar takalmansa ba.
And he proclaimed, saying, One mightier than I comes after me, whose shoe-latchet I am unworthy to stoop down and untie.
8 Ina muku baftisma da ruwa, amma shi zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”
I, indeed, have immersed you in water; but he will immerse you in the Holy Spirit.
9 A lokacin, Yesu ya zo daga Nazaret na Galili, Yohanna kuwa ya yi masa baftisma a Urdun.
At that time Jesus came from Nazareth of Galilee to the Jordan, and was immersed by John.
10 Da Yesu yana fitowa daga ruwan, sai ya ga sama ya buɗe, Ruhu kuma yana saukowa a kansa kamar kurciya.
As soon as he arose out of the water, he saw the sky part asunder, and the Spirit descend upon him like a dove.
11 Sai murya ta fito daga sama ta ce, “Kai ne Ɗana, wanda nake ƙauna, da kai kuma nake fari ciki ƙwarai.”
And a voice from heaven, which said, Thou art my Son, the beloved, in whom I delight.
12 Nan da nan, sai Ruhu ya kai shi cikin hamada,
Immediately after this, the spirit conveyed him into the wilderness;
13 ya kuma kasance a hamada kwana arba’in, Shaiɗan yana gwada shi. Yana tare da namomin jeji, mala’iku kuma suka yi masa hidima.
and he continued in the wilderness forty days tempted by Satan; and was among the wild beasts; and the heavenly messengers ministered to him.
14 Bayan da aka sa Yohanna a kurkuku, sai Yesu ya shigo cikin Galili, yana shelar bisharar Allah.
But after John's imprisonment, Jesus went to Galilee, proclaiming the good tidings of the Reign of God.
15 Yana cewa, “Lokaci ya yi. Mulkin Allah ya yi kusa. Ku tuba, ku gaskata bishara!”
The time, he said, is accomplished, the Reign of God approaches; reform, and believe the good tidings.
16 Yayinda Yesu yake tafiya a gaɓar Tekun Galili, sai ya ga Siman da ɗan’uwansa Andarawus, suna jefa abin kamun kifi a cikin tafkin, domin su masunta ne.
Then walking by the sea of Galilee, he saw Simon, and Andrew, Simon's brother, casting a drag net into the sea, for they were fishers.
17 Yesu ya ce, “Ku zo, ku bi ni, ni kuwa zan mai da ku masuntan mutane.”
Jesus said to them, Come with me, and I will cause you to be fishers of men.
18 Nan da nan, suka bar abin kamun kifinsu, suka bi shi.
Immediately they left their nets, and followed him.
19 Da ya yi gaba kaɗan, sai ya ga Yaƙub ɗan Zebedi, da ɗan’uwansa Yohanna a cikin jirgin ruwa, suna gyaran abin kamun kifinsu.
Passing on a little, and seeing James, son of Zebedee, with John his brother, who were mending their nets in a bark,
20 Ba da ɓata lokaci ba, ya kira su, sai suka bar mahaifinsu Zebedi a cikin jirgin ruwan, tare da’yan haya, suka kuwa bi shi.
he immediately called them; and leaving their father Zebedee in the bark with the hired servants, they accompanied him.
21 Suka tafi Kafarnahum. Da ranar Asabbaci ta kewayo, sai Yesu ya shiga majami’a ya fara koyarwa.
And they went to Capernaum; and on the Sabbath he repaired directly to the synagogue, and instructed the people,
22 Mutane suka yi mamakin koyarwarsa, domin ya koyar da su kamar wanda yake da iko, ba kamar malaman dokoki ba.
who were filled with admiration at his manner of teaching; for he taught as one having authority, and not as the scribes.
23 Nan take, sai wani mutum mai mugun ruhu a majami’arsu, ya ɗaga murya ya ce,
Now there was in their synagogue a man possessed with an unclean spirit, who cried out,
24 “Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne don ka hallaka mu? Na san wane ne kai, Mai Tsarki nan na Allah!”
Ah! Jesus of Nazareth, what hast thou to do with us? Art thou come to destroy us? I know who thou art, the Holy One of God.
25 Yesu ya tsawata masa ya ce, “Yi shiru! Fita daga cikinsa!”
Jesus rebuking him, said, Be silent, and come out of him.
26 Sai mugun ruhun ya jijjiga mutumin da ƙarfi, ya fita daga jikinsa da ihu.
Then the unclean spirit threw him into convulsions; and, raising loud cried, came out of him:
27 Dukan mutane suka yi mamaki, suna tambayar juna suna cewa, “Mene ne haka? Tabɗi! Yau ga sabuwar koyarwa kuma da iko! Yana ma ba wa mugayen ruhohi umarni, suna kuma yin masa biyayya.”
at which they were all so amazed, that they asked one another, What does this mean? For he commands with authority even the unclean spirits, and they obey him.
28 Labari game da shi ya bazu nan da nan ko’ina a dukan yankin Galili.
And thenceforth his fame spread through all the region of Galilee.
29 Da suka bar majami’ar, sai suka tafi gidan su Siman da Andarawus, tare da Yaƙub da Yohanna.
As soon as they were come out of the synagogue, they went with James and John into the house of Simon and Andrew,
30 Surukar Siman tana kwance da zazzaɓi, sai suka gaya wa Yesu game da ita.
where Simon's wife's mother lay sick of a fever, of which they immediately acquainted Jesus.
31 Sai ya je wajenta, ya kama hannunta, ya ɗaga ta. Zazzaɓin kuwa ya sāke ta, ta kuma yi musu hidima.
And he came, and taking her by the hand, raised her; instantly the fever left her, and she entertained them.
32 A wannan yamma, bayan fāɗuwar rana, mutane suka kawo wa Yesu dukan marasa lafiya, da masu aljanu.
In the evening, after sunset, they brought to him all the sick, and the demoniacs;
33 Duk garin ya taru a ƙofar gidan.
the whole city being assembled at the door.
34 Yesu kuwa ya warkar da marasa lafiya da yawa da suke da cututtuka iri-iri. Ya kuma fitar da aljanu da yawa, amma bai yarda aljanun suka yi magana ba, don sun san wane ne shi.
And he healed many persons affected with various diseases, and expelled many demons, whom he permitted not to speak, because they knew him.
35 Da sassafe, tun da sauran duhu, Yesu ya tashi, ya bar gida, ya tafi wani wurin da ba kowa, a can ya yi addu’a.
On the morrow, having risen before dawn, he went out, and retired to a solitary place, and prayed there.
36 Siman da abokansa suka fita nemansa.
And Simon and his company went in quest of him,
37 Da suka same shi, sai suka ce, “Kowa yana nemanka!”
and having found him, said to him, Every person seeks you.
38 Yesu ya amsa ya ce, “Mu je wani wuri dabam, zuwa ƙauyukan da suke kusa, don in yi wa’azi a can ma. Wannan shi ne dalilin zuwana.”
Jesus said, Let us go to the neighboring boroughs, to make proclamation there also: for I came out with this design.
39 Sai ya tafi ko’ina a Galili, yana wa’azi a majami’unsu, yana kuma fitar da aljanu.
Accordingly he proclaimed in their synagogues throughout all Galilee, and expelled demons.
40 Wani mutum mai kuturta ya zo wurinsa, ya durƙusa ya roƙe shi ya ce, “In kana so, za ka iya tsabtacce ni.”
And a leper came to him, and on his knees entreated him, saying, If you will, you can cleanse me.
41 Cike da tausayi, sai Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka tsabtacce!”
Jesus had compassion, and stretching out his hand and touching him, said, I will, be you clean.
42 Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi, ya kuma warke.
This he had no sooner uttered, than the leprosy departed from the man, and he was cleansed.
43 Yesu ya sallame shi nan take, da gargaɗi mai ƙarfi cewa,
Then Jesus strictly charging him, and dismissing him,
44 “Ka lura kada ka gaya wa kowa wannan. Amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayun da Musa ya umarta saboda tsarkakewarka, don yă zama shaida gare su.”
said, See you tell nothing of this to any man; but go, show yourself to the priest; and offer for your cleansing the things prescribed by Moses, that it may be notified to the people.
45 A maimakon haka, sai ya fita, ya fara magana a sake, yana baza labarin. Saboda haka, Yesu bai ƙara iya shiga cikin gari a fili ba, sai dai ya kasance a wuraren da ba kowa. Duk da haka, mutane suka yi ta zuwa wurinsa daga ko’ina.
But the man, as soon as he was gone, began to blaze this story, talking openly everywhere, insomuch that Jesus could no longer publicly appear in the city; but remained without in solitary places, whither the people resorted to him from all parts.

< Markus 1 >