< Markus 1 >

1 Farkon bishara game da Yesu Kiristi, Ɗan Allah.
Počátek evangelium Ježíše Krista, Syna Božího;
2 An rubuta a cikin littafin annabi Ishaya cewa, “Zan aika da ɗan aikena yă sha gabanka, wanda zai shirya hanyarka,”
Jakož psáno jest v prorocích: Aj, já posílám anděla svého před tváří tvou, kterýž připraví cestu tvou před tebou.
3 “muryar mai kira a hamada tana cewa, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.’”
Hlas volajícího na poušti: Připravujte cestu Páně, přímé čiňte stezky jeho.
4 Ta haka Yohanna ya zo, yana baftisma a yankin hamada, yana kuma wa’azin baftismar tuba don gafarar zunubai.
Křtil Jan na poušti, a kázal křest pokání na odpuštění hříchů.
5 Dukan ƙauyukan Yahudiya da dukan mutanen Urushalima suka fiffito zuwa wurinsa. Suna furta zunubansu, ya kuwa yi musu baftisma a Kogin Urdun.
I vycházela k němu všecka krajina Judská i Jeruzalémští, a křtěni byli od něho všickni v Jordáně řece, vyznávajíce hříchy své.
6 Yohanna ya sa tufafin gashin raƙumi, ya kuma yi ɗamara da fata. Abincinsa fāri ne da kuma zumar jeji.
Byl pak Jan odín srstmi velbloudovými, a pás kožený na bedrách jeho, a jídal kobylky a med lesní.
7 Wannan kuwa shi ne saƙonsa, “A bayana, wanda ya fi ni iko yana zuwa, ban kuwa isa in sunkuya in kunce igiyar takalmansa ba.
A kázal, řka: Jde za mnou silnější nežli já, kterémuž nejsem hoden, sehna se, rozvázati řeménka u obuvi jeho.
8 Ina muku baftisma da ruwa, amma shi zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”
Já zajisté křtil jsem vás vodou, ale onť vás křtíti bude Duchem svatým.
9 A lokacin, Yesu ya zo daga Nazaret na Galili, Yohanna kuwa ya yi masa baftisma a Urdun.
I stalo se v těch dnech, přišel Ježíš z Nazarétu Galilejského, a pokřtěn jest od Jana v Jordáně.
10 Da Yesu yana fitowa daga ruwan, sai ya ga sama ya buɗe, Ruhu kuma yana saukowa a kansa kamar kurciya.
A hned vystoupiv z vody, uzřel nebesa otevřená a Ducha jako holubici sstupujícího na něj.
11 Sai murya ta fito daga sama ta ce, “Kai ne Ɗana, wanda nake ƙauna, da kai kuma nake fari ciki ƙwarai.”
A hlas stal se s nebe: Ty jsi ten můj milý Syn, v němž mi se dobře zalíbilo.
12 Nan da nan, sai Ruhu ya kai shi cikin hamada,
A i hned ho Duch vypudil na poušť.
13 ya kuma kasance a hamada kwana arba’in, Shaiɗan yana gwada shi. Yana tare da namomin jeji, mala’iku kuma suka yi masa hidima.
I byl tam na poušti čtyřidceti dnů, a pokoušín byl od satana; a byl s zvěří, a andělé přisluhovali jemu.
14 Bayan da aka sa Yohanna a kurkuku, sai Yesu ya shigo cikin Galili, yana shelar bisharar Allah.
Když pak byl vsazen Jan, přišel Ježíš do Galilee, káže evangelium království Božího,
15 Yana cewa, “Lokaci ya yi. Mulkin Allah ya yi kusa. Ku tuba, ku gaskata bishara!”
A pravě: Že se naplnil čas, a přiblížilo se království Boží. Čiňte pokání, a věřte evangelium.
16 Yayinda Yesu yake tafiya a gaɓar Tekun Galili, sai ya ga Siman da ɗan’uwansa Andarawus, suna jefa abin kamun kifi a cikin tafkin, domin su masunta ne.
A chodě podlé moře Galilejského, uzřel Šimona a Ondřeje bratra jeho, ani pouštějí síti do moře, (nebo rybáři byli.)
17 Yesu ya ce, “Ku zo, ku bi ni, ni kuwa zan mai da ku masuntan mutane.”
I řekl jim Ježíš: Poďte za mnou, a učiním vás rybáře lidí.
18 Nan da nan, suka bar abin kamun kifinsu, suka bi shi.
A hned opustivše síti své, šli za ním.
19 Da ya yi gaba kaɗan, sai ya ga Yaƙub ɗan Zebedi, da ɗan’uwansa Yohanna a cikin jirgin ruwa, suna gyaran abin kamun kifinsu.
A poodšed odtud maličko, uzřel Jakuba syna Zebedeova, a Jana bratra jeho, ani na lodí tvrdí síti.
20 Ba da ɓata lokaci ba, ya kira su, sai suka bar mahaifinsu Zebedi a cikin jirgin ruwan, tare da’yan haya, suka kuwa bi shi.
A hned povolal jich. A oni opustivše otce svého Zebedea na lodí s pacholky, šli za ním.
21 Suka tafi Kafarnahum. Da ranar Asabbaci ta kewayo, sai Yesu ya shiga majami’a ya fara koyarwa.
I vešli do Kafarnaum. A hned v sobotu šed do školy, učil.
22 Mutane suka yi mamakin koyarwarsa, domin ya koyar da su kamar wanda yake da iko, ba kamar malaman dokoki ba.
I divili se náramně učení jeho; nebo učil je, jako moc maje, a ne jako zákonníci.
23 Nan take, sai wani mutum mai mugun ruhu a majami’arsu, ya ɗaga murya ya ce,
I byl v škole jejich člověk, maje ducha nečistého. Kterýž zvolal,
24 “Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne don ka hallaka mu? Na san wane ne kai, Mai Tsarki nan na Allah!”
Řka: Ach, což jest tobě do nás, Ježíši Nazaretský? Přišel jsi zatratiti nás. Znám tě, kdo jsi, že ten Svatý Boží.
25 Yesu ya tsawata masa ya ce, “Yi shiru! Fita daga cikinsa!”
I přimluvil mu Ježíš, řka: Umlkniž a vyjdi z něho.
26 Sai mugun ruhun ya jijjiga mutumin da ƙarfi, ya fita daga jikinsa da ihu.
I polomcovav jím duch nečistý a křiče hlasem velikým, vyšel z něho.
27 Dukan mutane suka yi mamaki, suna tambayar juna suna cewa, “Mene ne haka? Tabɗi! Yau ga sabuwar koyarwa kuma da iko! Yana ma ba wa mugayen ruhohi umarni, suna kuma yin masa biyayya.”
I lekli se všickni, tak že se tázali mezi sebou, řkouce: I co jest toto? Jakéž toto nové učení, že mocně i těm duchům nečistým rozkazuje, a poslouchají ho?
28 Labari game da shi ya bazu nan da nan ko’ina a dukan yankin Galili.
I roznesla se pověst o něm hned po vší krajině Galilejské.
29 Da suka bar majami’ar, sai suka tafi gidan su Siman da Andarawus, tare da Yaƙub da Yohanna.
A hned vyšedše ze školy, přišli do domu Šimonova a Ondřejova s Jakubem a s Janem.
30 Surukar Siman tana kwance da zazzaɓi, sai suka gaya wa Yesu game da ita.
Šimonova pak svegruše ležela, majíc zimnici. A hned jemu pověděli o ní.
31 Sai ya je wajenta, ya kama hannunta, ya ɗaga ta. Zazzaɓin kuwa ya sāke ta, ta kuma yi musu hidima.
A přistoupiv, pozdvihl jí, ujav ji za ruku její, a hned přestala jí zimnice. I posluhovala jim.
32 A wannan yamma, bayan fāɗuwar rana, mutane suka kawo wa Yesu dukan marasa lafiya, da masu aljanu.
Večer pak při západu slunce, nosili k němu všecky nemocné i ďábelníky.
33 Duk garin ya taru a ƙofar gidan.
A bylo se všecko město zběhlo ke dveřím.
34 Yesu kuwa ya warkar da marasa lafiya da yawa da suke da cututtuka iri-iri. Ya kuma fitar da aljanu da yawa, amma bai yarda aljanun suka yi magana ba, don sun san wane ne shi.
I uzdravoval mnohé ztrápené rozličnými neduhy, a ďábelství mnohá vymítal, a nedopouštěl mluviti ďáblům; nebo znali ho.
35 Da sassafe, tun da sauran duhu, Yesu ya tashi, ya bar gida, ya tafi wani wurin da ba kowa, a can ya yi addu’a.
A přede dnem velmi ráno vstav, vyšel a odšel na pusté místo, a tam se modlil.
36 Siman da abokansa suka fita nemansa.
I šli za ním Šimon i ti, kteříž s ním byli.
37 Da suka same shi, sai suka ce, “Kowa yana nemanka!”
A nalezše jej, řekli jemu: Všickni tě hledají.
38 Yesu ya amsa ya ce, “Mu je wani wuri dabam, zuwa ƙauyukan da suke kusa, don in yi wa’azi a can ma. Wannan shi ne dalilin zuwana.”
I dí jim: Poďmež do okolních městeček, abych i tam kázal. Nebo na to jsem přišel.
39 Sai ya tafi ko’ina a Galili, yana wa’azi a majami’unsu, yana kuma fitar da aljanu.
I kázal v školách jejich ve vší Galilei, a ďábelství vymítal.
40 Wani mutum mai kuturta ya zo wurinsa, ya durƙusa ya roƙe shi ya ce, “In kana so, za ka iya tsabtacce ni.”
Tedy přišel k němu malomocný, prose ho, a klekna před ním, řekl jemu: Chceš-li, můžeš mne očistiti.
41 Cike da tausayi, sai Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka tsabtacce!”
Ježíš pak slitovav se, vztáhl ruku, dotekl se ho a řekl jemu: Chci, buď čist.
42 Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi, ya kuma warke.
A když to řekl, hned odstoupilo od něho malomocenství, a očištěn jest.
43 Yesu ya sallame shi nan take, da gargaɗi mai ƙarfi cewa,
I zapověděv mu přísně, hned ho odbyl,
44 “Ka lura kada ka gaya wa kowa wannan. Amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayun da Musa ya umarta saboda tsarkakewarka, don yă zama shaida gare su.”
A řekl mu: Viziž, abys žádnému nic nepravil. Ale jdi, ukaž se knězi, a obětuj za očištění své to, což přikázal Mojžíš, na svědectví proti nim.
45 A maimakon haka, sai ya fita, ya fara magana a sake, yana baza labarin. Saboda haka, Yesu bai ƙara iya shiga cikin gari a fili ba, sai dai ya kasance a wuraren da ba kowa. Duk da haka, mutane suka yi ta zuwa wurinsa daga ko’ina.
On pak vyšed, počal vypravovati mnoho a ohlašovati tu věc, tak že již nemohl Ježíš do města zjevně vjíti, ale vně na místech pustých byl. I scházeli se k němu odevšad.

< Markus 1 >