< Malaki 1 >

1 Annabci, wannan ita ce maganar Ubangiji ga Isra’ila ta wurin Malaki.
Breme Gospodove besede Izraelu, po Malahiju.
2 “Na ƙaunace ku, in ji Ubangiji. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya ka ƙaunace mu?’ “Isuwa ba ɗan’uwan Yaƙub ba ne?” In ji Ubangiji. “Duk da haka na ƙaunaci Yaƙub,
»Ljubil sem vas, « govori Gospod. Vendar pravite: »V čem si nas ljubil?« » Mar ni bil Ezav Jakobov brat?« govori Gospod, »vendar sem ljubil Jakoba,
3 amma na ƙi Isuwa, na kuma mai da ƙasarsa da take kan duwatsu kango, na ba da gādonsa ga dilolin hamada.”
Ezava pa sovražil ter opustošil njegove gore in njegovo dediščino za zmaje divjine.«
4 Edom zai iya cewa, “Ko da yake an ragargaza mu, ai, za mu sāke gina kufanmu.” Amma ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Za su iya gini, amma zan rushe. Za a ce da su Muguwar Ƙasa, mutane da kullum suke a ƙarƙashi fushin Ubangiji.
Kakor govori Edóm: »Obubožani smo, toda vrnili se bomo in pozidali zapuščene kraje, « tako govori Gospod nad bojevniki: »Gradili bodo, toda jaz bom rušil. Imenovali jih bodo: ›Meja zlobnosti‹ in ›Ljudstvo, zoper katero ima Gospod ogorčenje na veke.‹«
5 Za ku ga wannan da idanunku ku kuma ce, ‘Ubangiji da girma yake, har gaba da iyakokin Isra’ila ma!’
Vaše oči bodo videle in rekli boste: » Gospod bo poveličan prek Izraelove meje.«
6 “Ɗa yakan girmama mahaifinsa, bawa kuma yakan girmama maigidansa. In ni mahaifi ne, ina girman da ya dace da ni? In ni maigida ne, ina girman da ya dace da ni?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Ku firistoci, ku ne kuka rena sunana. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya muka rena sunanka?’
»Sin časti svojega očeta in služabnik svojega gospodarja. Če sem jaz potem oče, kje je moja čast? In če sem jaz gospodar, kje je moj strah?« govori Gospod nad bojevniki, »vam, oh duhovniki, ki prezirate moje ime. Vi pa pravite: ›V čem smo prezirali tvoje ime?‹
7 “Kun ajiye abinci mai ƙazanta a kan bagadena. “Sai kuka ce, ‘Yaya muka ƙazantar da kai?’ “Ta wurin cewa teburin Ubangiji abin reni ne.
Na mojem oltarju ste darovali oskrunjen kruh, vi pa pravite: ›V čem smo te oskrunili?‹ V tem, da pravite: › Gospodova miza je zaničevanja vredna.‹
8 Sa’ad da kuka kawo makauniyar dabba don ku miƙa mini hadaya, wannan daidai ne? Sa’ad da kuka miƙa gurguwar dabba ko marar lafiya, wannan daidai ne? Ku gwada ba wa gwamnanku irin wannan ku gani! Kuna gani zai ji daɗinku? Zai karɓe ku ne?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
In če darujete slepo za žrtev, mar ni to zlo? In če darujete hromo in bolno, mar ni to zlo? Daruj to sedaj svojemu voditelju; ali bo zadovoljen s teboj, ali sprejme tvojo osebo?« govori Gospod nad bojevniki.
9 “To, firistoci yanzu ku gwada ku roƙi Allah yă yi mana alheri. Da irin hadayun nan a hannuwanku ne zai ji ku?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
»In sedaj vas prosim, rotite Boga, da nam bo milostljiv. To je bilo z vašimi sredstvi. Mar bo cenil vaše osebe?« govori Gospod nad bojevniki.
10 “Kash, da ma wani daga cikinku ya rufe ƙofofin haikali don kada ku shiga, ku hura wuta marar amfani a bisa bagadena! Ba na jin daɗinku, ba zan kuwa karɓi hadaya daga hannuwanku ba” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
»Kdo je tam, celo med vami, da bi zaman zaprl vrata? Niti na mojem oltarju ognja ne netite zaman. Nobenega zadovoljstva nimam z vami, « govori Gospod nad bojevniki, »niti ne bom sprejel daritve iz vaše roke.
11 Sunana zai zama mai girma a cikin al’ummai, daga fitowar rana har zuwa fāɗuwarta. A kowane wuri za a miƙa wa sunana turare da tsabtacciyar hadaya domin sunana zai zama mai girma a cikin al’ummai, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Kajti od sončnega vzhoda, celo do zahajanja istega bo moje ime veliko med pogani in na vsakem kraju bo mojemu imenu darovano kadilo in čista daritev, kajti moje ime bo veliko med pogani, « govori Gospod nad bojevniki.
12 “Amma kun ƙazantar da sunana ta wurin cewa ‘Teburin Ubangiji ya ƙazantu,’ kuka kuma yi magana a kan abincinsa kuna cewa, ‘Abin reni ne.’
»Toda vi ste to oskrunili v tem, ko pravite: › Gospodova miza je oskrunjena; in njen sad, celó njegova jed, je zaničevanja vredna.‹
13 Kun kuma ce, ‘Mun gaji da irin wannan wahala!’ Kuna hura mini hancin reni,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Sa’ad da kuka kawo raunannu, gurguntattun dabbobi, ko kuma dabbobi masu fama da cuta, kuka kuma miƙa su hadaya, kuna gani zan karɓi wannan daga gare ku?” In ji Ubangiji.
Pravite tudi: ›Glej, kakšna težava je to!‹ In vi ste nad tem vihali nos, « govori Gospod nad bojevniki, »in privedli to, kar je bilo raztrgano in hromo in bolno. Tako daritev ste privedli. Mar naj bi to sprejel iz vaše roke?« govori Gospod.
14 “La’ananne ne macucin da yake da lafiyayyiyar dabba namiji a garkensa wadda ya yi alkawari zai bayar, amma sai ya miƙa hadayar dabba mai aibi ga Ubangiji. Gama ni babban sarki ne, za a kuma ji tsoron sunana a cikin al’ummai,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Toda preklet bodi slepar, ki ima v svojem tropu samca, pa prisega in žrtvuje Gospodu pokvarjeno stvar, kajti jaz sem velik Kralj, « govori Gospod nad bojevniki, »in moje ime je grozno med pogani.«

< Malaki 1 >