< Malaki 4 >

1 “Tabbatacce rana tana zuwa; za tă yi ƙuna kamar wutar maƙera. Dukan masu girman kai da kowane mai aikata mugunta zai zama ciyawa, wannan rana mai zuwa za tă ƙone su. Babu saiwa ko reshen da za a bar musu,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Watch out! The day is coming—it burns like an oven—when the proud and the wicked will be burned like straw. When that day comes they will be completely burned up, root and branch, says the Lord Almighty.
2 Amma ku da kuke girmama sunana, ranar adalci za tă fito tare da warkarwa a fikafikanta. Za ku kuwa fita kuna tsalle kamar’yan maruƙan da aka sake daga garke.
But for those who have reverence for me, the sun of God's salvation will rise with healing in its wings, and you will be set free, leaping like calves released from their stalls.
3 Sa’an nan za ku tattake mugaye; za su zama toka a ƙarƙashin tafin ƙafafunku a ranar da zan aikata waɗannan abubuwa, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
You will trample the wicked as ashes under your feet on the day when I take action, says the Lord Almighty.
4 “Ku tuna da dokar bawana Musa, ƙa’idodi da dokokin da na ba shi a Horeb domin dukan Isra’ila.
Remember the law of Moses my servant that I commanded him and all Israel to follow—all the instructions and ceremonies I gave on Mount Sinai.
5 “Ga shi, zan aika muku da annabi Iliya kafin babbar ranan nan mai banrazana ta Ubangiji tă zo.
Look! I am going to send Elijah the prophet before the day of the Lord arrives, the great and terrifying day.
6 Zai juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, zukatan’ya’ya kuma ga iyayensu; in ba haka ba zan bugi ƙasar da hallaka gaba ɗaya.”
He will restore harmony between parents and children, and if that does not happen, I will come and strike the land with a curse.

< Malaki 4 >