< Malaki 4 >
1 “Tabbatacce rana tana zuwa; za tă yi ƙuna kamar wutar maƙera. Dukan masu girman kai da kowane mai aikata mugunta zai zama ciyawa, wannan rana mai zuwa za tă ƙone su. Babu saiwa ko reshen da za a bar musu,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
For behold the day shall come kindled as a furnace: and all the proud, and all that do wickedly shall be stubble: and the day that cometh shall set them on fire, saith the Lord of hosts, it shall not leave them root, nor branch.
2 Amma ku da kuke girmama sunana, ranar adalci za tă fito tare da warkarwa a fikafikanta. Za ku kuwa fita kuna tsalle kamar’yan maruƙan da aka sake daga garke.
But unto you that fear my name, the Sun of justice shall arise, and health in his wings: and you shall go forth, and shall leap like calves of the herd.
3 Sa’an nan za ku tattake mugaye; za su zama toka a ƙarƙashin tafin ƙafafunku a ranar da zan aikata waɗannan abubuwa, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
And you shall tread down the wicked when they shall be ashes under the sole of your feet in the day that I do this, saith the Lord of hosts.
4 “Ku tuna da dokar bawana Musa, ƙa’idodi da dokokin da na ba shi a Horeb domin dukan Isra’ila.
Remember the law of Moses my servant, which I commanded him in Horeb for all Israel, the precepts, and judgments.
5 “Ga shi, zan aika muku da annabi Iliya kafin babbar ranan nan mai banrazana ta Ubangiji tă zo.
Behold I will send you Elias the prophet, before the coming of the great and dreadful day of the Lord.
6 Zai juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, zukatan’ya’ya kuma ga iyayensu; in ba haka ba zan bugi ƙasar da hallaka gaba ɗaya.”
And he shall turn the heart of the fathers to the children, and the heart of the children to their fathers: lest I come, and strike the earth with anathema.