< Malaki 3 >
1 “Duba, zan aika manzona, wanda zai shirya hanya a gabana. Sa’an nan a farat ɗaya Ubangiji wanda kuke nema zai zo haikalinsa. Manzon alkawari, wanda kuke sa zuciya kuwa zai zo,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Voici que moi j’envoie mon ange, et il préparera la voie devant ma face. Et aussitôt viendra dans son temple le dominateur que vous cherchez, et l’ange de l’alliance que vous désirez. Voici qu’il vient, dit le Seigneur des armées;
2 Amma wa zai jure wa ranar zuwansa? Wa zai iya tsaya sa’ad da ya bayyana? Gama zai zama kamar wuta mai tace ƙarfe, ko sabulu mai wanki.
Et qui pourra penser au jour de son avènement, et qui en soutiendra la vue? Car il sera comme un feu qui fond les métaux, et comme une herbe de foulons.
3 Zai zama kamar mai tace azurfa da mai tsarkaketa; zai tsabtacce Lawiyawa, yă kuma tace su kamar zinariya da azurfa. Sa’an nan Ubangiji zai sami mutanen da za su kawo hadayu a cikin adalci.
Et il sera assis fondant et épurant l’argent; et il purifiera les fils de Lévi, et il les roulera comme l’or et l’argent, et ils offriront au Seigneur des sacrifices dans la justice.
4 Hadayun Yahuda da na Urushalima za su zama yardajje ga Ubangiji, za su zama kamar a kwanakin da suka wuce, kamar a shekarun baya.
Et le sacrifice de Juda et de Jérusalem sera agréable au Seigneur, comme aux jours des siècles passés, et comme dans les années anciennes.
5 “Ta haka zan zo kusa da ku don in yi hukunci. Zan hanzarta ba da shaida a kan masu yin sihiri, da mazinata da masu shaidar zur. Zan ba da shaida a kan waɗanda suke zaluntar ma’aikata a kan albashinsu, da waɗanda suke ƙwarar gwauraye da marayu, suna kuma hana baƙi samun adalci, ba sa ma tsorona,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Et je viendrai à vous en jugement, et je serai un témoin empressé contre les magiciens, les adultères et les parjures, et ceux qui commettent des injustices dans le salaire du mercenaire, envers les veuves et les orphelins, et qui oppriment l’étranger, et qui ne m’ont pas craint, dit le Seigneur des armées.
6 “Ni Ubangiji ba na canjawa. Shi ya sa ku zuriyar Yaƙub, ba a hallaka ku ƙaƙaf ba.
Car je suis le Seigneur, et je ne change point; et vous, fils de Jacob, vous n’avez pas été consumés.
7 Tun zamanin kakanninku, kun juye wa ƙa’idodina baya, ba ku kuma kiyaye su ba. Ku komo gare ni, ni kuma zan koma gare ku,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya za mu koma gare ka?’
Car dès les jours de vos pères, vous vous êtes écartés de mes lois, vous ne les avez pas gardées. Revenez à moi, et je reviendrai à vous, dit le Seigneur des armées. Et vous avez dit: Comment reviendrons-nous?
8 “Mutum zai iya yi wa Allah fashi ne? Duk da haka kun yi mini fashi. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya muka yi maka fashi?’ “A wajen zakka da hadayu.
Un homme affligera-t-il Dieu? car vous m’avez outragé, et vous avez dit: En quoi vous avons-nous outragé? Dans les dîmes et les prémices.
9 Kuna ƙarƙashin la’ana, dukan al’ummarku, domin kuna yin mini fashi.
Et vous avez été maudits dans la pénurie, et vous m’outragez, vous, la nation entière.
10 Ku kawo dukan zakka cikin gidan ajiya, don a kasance da abinci a gidana. Ku gwada ni a wannan ku ga, ko ba zan buɗe taskokin sama in zubo muku albarka mai yawa, wadda har ba za ku rasa wurin sa ta ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Apportez toute la dîme dans mon grenier, et qu’il y ait de la nourriture dans ma maison, et éprouvez-moi en cela, dit le Seigneur: vous verrez si je n’ouvre pas les sources du ciel, et si je ne répands pas sur vous la bénédiction jusqu’à l’abondance.
11 Zan hana ƙwari su cinye hatsinku. Kuringar inabi a gonakinku kuma ba za su zubar da’ya’yansu kafin su nuna ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Et je menacerai en votre faveur l’insecte dévorant, et il ne détruira pas le fruit de votre terre; et la vigne ne sera pas stérile dans les champs, dit le Seigneur des armées.
12 “Sa’an nan dukan al’ummai za su ce da ku masu albarka, gama ƙasarku za tă yi daɗin zama,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Et toutes les nations vous diront bien heureux: car vous serez vous-mêmes une terre délicieuse, dit le Seigneur des armées.
13 “Kun faɗi mugayen abubuwa a kaina,” in ji Ubangiji. “Duk da haka kuka ce, ‘Me muka faɗa a kanka?’
Vos paroles ont pris de la force contre moi, dit le Seigneur.
14 “Kun ce, ‘Ba amfani a bauta wa Allah. Wanda amfani muka samu ta wurin kiyaye umarnansa muna yawo kamar masu makoki a gaban Ubangiji Maɗaukaki?
Et vous avez dit: Qu’avons-nous dit contre vous? Vous avez dit: Vain est celui qui sert Dieu; et quel a été notre avantage pour avoir gardé ses préceptes et pour avoir marché tristes devant le Seigneur des armées?
15 A ganinmu, masu girman kai suna jin daɗi. Masu aikata mugunta kuwa ba arziki kaɗai suka yi ba, amma sukan gwada Allah da mugayen ayyukansu, su kuwa zauna lafiya.’”
Maintenant donc nous disons heureux les arrogants, puisqu’ils se sont établis en commettant l’impiété, et ils ont tenté Dieu, et ils ont été sauvés.
16 Sa’an nan waɗanda suke tsoron Ubangiji suka yi magana da juna, Ubangiji kuwa ya kasa kunne ya kuma ji. A gabansa aka rubuta a littafin tarihi waɗanda suke tsoron Ubangiji, suna kuma girmama sunansa.
Alors ceux qui craignent le Seigneur ont parlé chacun avec son prochain; et le Seigneur a été attentif, et il a écouté; et il a été écrit un livre de souvenir devant lui pour ceux qui craignent le Seigneur et qui méditent son nom.
17 “A ranar da na shirya ajiyayyen mallakata, za su zama nawa,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan ji kansu kamar yadda mahaifi cikin tausayi yakan ji kan ɗansa wanda yake masa hidima.
Et ils seront, dit le Seigneur, mon bien particulier, au jour auquel j’agirai; et je les épargnerai comme un père épargne son fils qui le sert.
18 Za ku kuma ga bambanci tsakanin masu adalci da mugaye, tsakanin waɗanda suke wa Allah hidima da kuma waɗanda ba sa yi.
Et vous vous convertirez, et vous verrez la différence qu’il y a entre le juste et l’impie, et entre celui qui sert Dieu et celui qui ne le sert pas.