< Malaki 3 >

1 “Duba, zan aika manzona, wanda zai shirya hanya a gabana. Sa’an nan a farat ɗaya Ubangiji wanda kuke nema zai zo haikalinsa. Manzon alkawari, wanda kuke sa zuciya kuwa zai zo,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Voici, je m'en vais envoyer mon messager, et il préparera la voie devant moi, et incontinent le Seigneur que vous cherchez entrera dans son Temple, l'Ange, dis-je, de l'alliance, lequel vous souhaitez; voici, il vient, a dit l'Eternel des armées.
2 Amma wa zai jure wa ranar zuwansa? Wa zai iya tsaya sa’ad da ya bayyana? Gama zai zama kamar wuta mai tace ƙarfe, ko sabulu mai wanki.
Mais qui pourra soutenir le jour de sa venue? et qui pourra subsister quand il paraîtra? Car il sera comme le feu de celui qui raffine, et comme le savon des foulons.
3 Zai zama kamar mai tace azurfa da mai tsarkaketa; zai tsabtacce Lawiyawa, yă kuma tace su kamar zinariya da azurfa. Sa’an nan Ubangiji zai sami mutanen da za su kawo hadayu a cikin adalci.
Et il sera [assis] comme celui qui raffine et qui purifie l'argent; il nettoiera les fils de Lévi, il les épurera comme l'or et l'argent; et ils présenteront à l'Eternel une oblation suivant la justice.
4 Hadayun Yahuda da na Urushalima za su zama yardajje ga Ubangiji, za su zama kamar a kwanakin da suka wuce, kamar a shekarun baya.
L'oblation de Juda et de Jérusalem sera agréable à l'Eternel, comme dans les jours d'autrefois, et comme dans les premières années.
5 “Ta haka zan zo kusa da ku don in yi hukunci. Zan hanzarta ba da shaida a kan masu yin sihiri, da mazinata da masu shaidar zur. Zan ba da shaida a kan waɗanda suke zaluntar ma’aikata a kan albashinsu, da waɗanda suke ƙwarar gwauraye da marayu, suna kuma hana baƙi samun adalci, ba sa ma tsorona,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Je m'approcherai de vous pour faire jugement, et je serai témoin subit contre les enchanteurs, et contre les adultères, et contre ceux qui jurent faussement, et contre ceux qui fraudent le loyer du mercenaire, [qui oppriment] la veuve et l'orphelin, et qui font tort à l'étranger, et qui ne me craignent point, a dit l'Eternel des armées.
6 “Ni Ubangiji ba na canjawa. Shi ya sa ku zuriyar Yaƙub, ba a hallaka ku ƙaƙaf ba.
Parce que je [suis] l'Eternel, et que je n'ai point changé, à cause de cela, enfants de Jacob, vous n'avez point été consumés.
7 Tun zamanin kakanninku, kun juye wa ƙa’idodina baya, ba ku kuma kiyaye su ba. Ku komo gare ni, ni kuma zan koma gare ku,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya za mu koma gare ka?’
Depuis le temps de vos pères vous vous êtes détournés de mes statuts, et ne [les] avez point gardés. Retournez-vous vers moi, et je me retournerai vers vous, a dit l'Eternel des armées. Et vous dites: En quoi nous convertirons-nous?
8 “Mutum zai iya yi wa Allah fashi ne? Duk da haka kun yi mini fashi. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya muka yi maka fashi?’ “A wajen zakka da hadayu.
L'homme pillera-t-il Dieu, que vous me pilliez? Et vous dites: En quoi t'avons-nous pillé? [Vous l'avez fait] dans les dîmes et dans les offrandes.
9 Kuna ƙarƙashin la’ana, dukan al’ummarku, domin kuna yin mini fashi.
Vous êtes certainement maudits, parce que vous me pillez, [vous] toute la nation.
10 Ku kawo dukan zakka cikin gidan ajiya, don a kasance da abinci a gidana. Ku gwada ni a wannan ku ga, ko ba zan buɗe taskokin sama in zubo muku albarka mai yawa, wadda har ba za ku rasa wurin sa ta ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Apportez toutes les dîmes aux lieux ordonnés pour les garder, et qu'il y ait provision dans ma maison; et dès maintenant éprouvez-moi en ceci, a dit l'Eternel des armées, si je ne vous ouvre les canaux des cieux, et si je ne répands en votre faveur la bénédiction, en sorte que vous n'y pourrez point suffire.
11 Zan hana ƙwari su cinye hatsinku. Kuringar inabi a gonakinku kuma ba za su zubar da’ya’yansu kafin su nuna ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Et je réprimerai pour l'amour de vous le dévorateur, et il ne vous ravagera point les fruits de la terre; et vos vignes ne seront point stériles dans la campagne, a dit l'Eternel des armées.
12 “Sa’an nan dukan al’ummai za su ce da ku masu albarka, gama ƙasarku za tă yi daɗin zama,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Toutes les nations vous diront heureux, parce que vous serez un pays souhaitable, a dit l'Eternel des armées.
13 “Kun faɗi mugayen abubuwa a kaina,” in ji Ubangiji. “Duk da haka kuka ce, ‘Me muka faɗa a kanka?’
Vos paroles se sont renforcées contre moi, a dit l'Eternel; et vous dites: Qu'avons-nous donc dit contre toi?
14 “Kun ce, ‘Ba amfani a bauta wa Allah. Wanda amfani muka samu ta wurin kiyaye umarnansa muna yawo kamar masu makoki a gaban Ubangiji Maɗaukaki?
Vous avez dit: C'est en vain qu'on sert Dieu, et qu'avons-nous gagné d'avoir gardé ce qu'il a commandé de garder, et d'avoir marché en pauvre état pour l'amour de l'Eternel des armées?
15 A ganinmu, masu girman kai suna jin daɗi. Masu aikata mugunta kuwa ba arziki kaɗai suka yi ba, amma sukan gwada Allah da mugayen ayyukansu, su kuwa zauna lafiya.’”
Et maintenant nous tenons pour heureux les orgueilleux; et même ceux qui commettent la méchanceté, sont avancés, et s'ils ont tenté Dieu, ils ont été délivrés.
16 Sa’an nan waɗanda suke tsoron Ubangiji suka yi magana da juna, Ubangiji kuwa ya kasa kunne ya kuma ji. A gabansa aka rubuta a littafin tarihi waɗanda suke tsoron Ubangiji, suna kuma girmama sunansa.
Alors ceux qui craignent l'Eternel ont parlé l'un à l’autre, et l'Eternel y a été attentif, et l'a ouï, et on a écrit un livre de mémoires, devant lui; pour ceux qui craignent l'Eternel, et qui pensent à son Nom.
17 “A ranar da na shirya ajiyayyen mallakata, za su zama nawa,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan ji kansu kamar yadda mahaifi cikin tausayi yakan ji kan ɗansa wanda yake masa hidima.
Et ils seront miens, a dit l'Eternel des armées, lorsque je mettrai à part mes plus précieux joyaux, et je leur pardonnerai, ainsi que chacun pardonne à son fils qui le sert.
18 Za ku kuma ga bambanci tsakanin masu adalci da mugaye, tsakanin waɗanda suke wa Allah hidima da kuma waɗanda ba sa yi.
Convertissez-vous donc, et vous verrez [la différence qu'il y a] entre le juste et le méchant; entre celui qui sert Dieu et celui qui ne l'a point servi.

< Malaki 3 >