< Malaki 3 >

1 “Duba, zan aika manzona, wanda zai shirya hanya a gabana. Sa’an nan a farat ɗaya Ubangiji wanda kuke nema zai zo haikalinsa. Manzon alkawari, wanda kuke sa zuciya kuwa zai zo,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Behold, I will send my messenger, And he shall prepare the way before me; And the Lord, whom ye seek, shall suddenly come to his temple; And the messenger of the covenant, whom ye desire, Behold, he shall come, saith Jehovah of hosts.
2 Amma wa zai jure wa ranar zuwansa? Wa zai iya tsaya sa’ad da ya bayyana? Gama zai zama kamar wuta mai tace ƙarfe, ko sabulu mai wanki.
But who shall abide the day of his coming? And who shall stand when he appeareth? For he shall be like the fire of the refiner, And like the soap of the fuller.
3 Zai zama kamar mai tace azurfa da mai tsarkaketa; zai tsabtacce Lawiyawa, yă kuma tace su kamar zinariya da azurfa. Sa’an nan Ubangiji zai sami mutanen da za su kawo hadayu a cikin adalci.
And he shall sit as a refiner and purifier of silver, And he shall purify the sons of Levi, And shall refine them as gold and silver, That, being holy to Jehovah, they may bring an offering in righteousness.
4 Hadayun Yahuda da na Urushalima za su zama yardajje ga Ubangiji, za su zama kamar a kwanakin da suka wuce, kamar a shekarun baya.
Then shall the offering of Judah and Jerusalem be pleasing to Jehovah, As in the days of old, And as in former years.
5 “Ta haka zan zo kusa da ku don in yi hukunci. Zan hanzarta ba da shaida a kan masu yin sihiri, da mazinata da masu shaidar zur. Zan ba da shaida a kan waɗanda suke zaluntar ma’aikata a kan albashinsu, da waɗanda suke ƙwarar gwauraye da marayu, suna kuma hana baƙi samun adalci, ba sa ma tsorona,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
And I will come near to you to judgment; And I will be a swift witness Against sorcerers, and against adulterers, and against false swearers, And against those who defraud the hireling of his hire, And oppress the widow and the fatherless, And turn aside the stranger from his right, And fear not me, saith Jehovah of hosts.
6 “Ni Ubangiji ba na canjawa. Shi ya sa ku zuriyar Yaƙub, ba a hallaka ku ƙaƙaf ba.
For I am Jehovah; I change not; Therefore, ye sons of Jacob, are ye not consumed.
7 Tun zamanin kakanninku, kun juye wa ƙa’idodina baya, ba ku kuma kiyaye su ba. Ku komo gare ni, ni kuma zan koma gare ku,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya za mu koma gare ka?’
From the days of your fathers have ye turned aside from my statutes, And have not kept them; Return to me, and I will return to you, Saith Jehovah of hosts. But ye say, “Wherein shall we return?”
8 “Mutum zai iya yi wa Allah fashi ne? Duk da haka kun yi mini fashi. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya muka yi maka fashi?’ “A wajen zakka da hadayu.
Shall a man rob God, That ye have robbed me? But ye say, “Wherein have we robbed thee?” In tithes and offerings.
9 Kuna ƙarƙashin la’ana, dukan al’ummarku, domin kuna yin mini fashi.
Ye are cursed with a curse, For ye have robbed me, even this whole nation.
10 Ku kawo dukan zakka cikin gidan ajiya, don a kasance da abinci a gidana. Ku gwada ni a wannan ku ga, ko ba zan buɗe taskokin sama in zubo muku albarka mai yawa, wadda har ba za ku rasa wurin sa ta ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Bring ye all the tithes into the storehouse, That there be food in my house; And try me now in this, Saith Jehovah of hosts, Whether I will not open to you the windows of heaven, And pour out upon you a blessing, until there is none left.
11 Zan hana ƙwari su cinye hatsinku. Kuringar inabi a gonakinku kuma ba za su zubar da’ya’yansu kafin su nuna ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
And I will rebuke for you the devourer, And he shall not destroy the fruits of your ground, Nor shall your vine be barren in the field, Saith Jehovah of hosts.
12 “Sa’an nan dukan al’ummai za su ce da ku masu albarka, gama ƙasarku za tă yi daɗin zama,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
And all nations shall call you blessed; For ye shall be a delightful land, Saith Jehovah of hosts.
13 “Kun faɗi mugayen abubuwa a kaina,” in ji Ubangiji. “Duk da haka kuka ce, ‘Me muka faɗa a kanka?’
Your words have been bold against me, saith Jehovah; Yet ye say, “What have we spoken against thee?”
14 “Kun ce, ‘Ba amfani a bauta wa Allah. Wanda amfani muka samu ta wurin kiyaye umarnansa muna yawo kamar masu makoki a gaban Ubangiji Maɗaukaki?
Ye have said, “It is a vain thing to serve God”; And, “What profit is it that we have kept his ordinances, And that we have walked mournfully before Jehovah of hosts?
15 A ganinmu, masu girman kai suna jin daɗi. Masu aikata mugunta kuwa ba arziki kaɗai suka yi ba, amma sukan gwada Allah da mugayen ayyukansu, su kuwa zauna lafiya.’”
Therefore we call the proud happy; Yea, they that do wickedness are built up; Yea, they tempt God, and are delivered.”
16 Sa’an nan waɗanda suke tsoron Ubangiji suka yi magana da juna, Ubangiji kuwa ya kasa kunne ya kuma ji. A gabansa aka rubuta a littafin tarihi waɗanda suke tsoron Ubangiji, suna kuma girmama sunansa.
Then they that feared Jehovah spake to one another, And Jehovah gave ear and heard; And a book of remembrance was written before him, For them that feared Jehovah, And that thought upon his name.
17 “A ranar da na shirya ajiyayyen mallakata, za su zama nawa,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan ji kansu kamar yadda mahaifi cikin tausayi yakan ji kan ɗansa wanda yake masa hidima.
And they shall be to me, saith Jehovah of hosts, In the day which I appoint, as my own possession; And I will spare them, As a father spareth his own son that serveth him.
18 Za ku kuma ga bambanci tsakanin masu adalci da mugaye, tsakanin waɗanda suke wa Allah hidima da kuma waɗanda ba sa yi.
Then shall ye return and see What is the difference between the righteous and the wicked, Between him who serveth God And him who serveth him not.

< Malaki 3 >