< Malaki 3 >

1 “Duba, zan aika manzona, wanda zai shirya hanya a gabana. Sa’an nan a farat ɗaya Ubangiji wanda kuke nema zai zo haikalinsa. Manzon alkawari, wanda kuke sa zuciya kuwa zai zo,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Behold, I will send my messenger, and he shall prepare the way before me: and the Lord whom ye seeke, shall speedely come to his Temple: euen the messenger of the couenant whom ye desire: beholde, he shall come, sayth the Lord of hostes.
2 Amma wa zai jure wa ranar zuwansa? Wa zai iya tsaya sa’ad da ya bayyana? Gama zai zama kamar wuta mai tace ƙarfe, ko sabulu mai wanki.
But who may abide the day of his comming? and who shall endure, when he appeareth? for he is like a purging fire, and like fullers sope.
3 Zai zama kamar mai tace azurfa da mai tsarkaketa; zai tsabtacce Lawiyawa, yă kuma tace su kamar zinariya da azurfa. Sa’an nan Ubangiji zai sami mutanen da za su kawo hadayu a cikin adalci.
And he shall sit downe to trye and fine the siluer: he shall euen fine the sonnes of Leui and purifie them as golde and siluer, that they may bring offerings vnto the Lord in righteousnesse.
4 Hadayun Yahuda da na Urushalima za su zama yardajje ga Ubangiji, za su zama kamar a kwanakin da suka wuce, kamar a shekarun baya.
Then shall the offerings of Iudah and Ierusalem be acceptable vnto the Lord, as in old time and in the yeeres afore.
5 “Ta haka zan zo kusa da ku don in yi hukunci. Zan hanzarta ba da shaida a kan masu yin sihiri, da mazinata da masu shaidar zur. Zan ba da shaida a kan waɗanda suke zaluntar ma’aikata a kan albashinsu, da waɗanda suke ƙwarar gwauraye da marayu, suna kuma hana baƙi samun adalci, ba sa ma tsorona,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
And I will come neere to you to iudgement, and I will be a swift witnesse against the southsayers, and against the adulterers, and against false swearers, and against those that wrongfully keepe backe the hirelings wages, and vexe the widowe, and the fatherlesse, and oppresse the stranger, and feare not me, sayth the Lord of hostes.
6 “Ni Ubangiji ba na canjawa. Shi ya sa ku zuriyar Yaƙub, ba a hallaka ku ƙaƙaf ba.
For I am the Lord: I change not, and ye sonnes of Iaakob are not consumed.
7 Tun zamanin kakanninku, kun juye wa ƙa’idodina baya, ba ku kuma kiyaye su ba. Ku komo gare ni, ni kuma zan koma gare ku,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya za mu koma gare ka?’
From the dayes of your fathers, ye are gone away from mine ordinances, and haue not kept them: returne vnto me, and I will returne vnto you, saith the Lord of hostes: but ye saide, Wherein shall we returne?
8 “Mutum zai iya yi wa Allah fashi ne? Duk da haka kun yi mini fashi. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya muka yi maka fashi?’ “A wajen zakka da hadayu.
Will a man spoyle his gods? yet haue ye spoyled me: but ye say, Wherein haue we spoyled thee? In tithes, and offerings.
9 Kuna ƙarƙashin la’ana, dukan al’ummarku, domin kuna yin mini fashi.
Ye are cursed with a curse: for ye haue spoyled me, euen this whole nation.
10 Ku kawo dukan zakka cikin gidan ajiya, don a kasance da abinci a gidana. Ku gwada ni a wannan ku ga, ko ba zan buɗe taskokin sama in zubo muku albarka mai yawa, wadda har ba za ku rasa wurin sa ta ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Bring ye all the tythes into the storehouse that there may be meate in mine House, and proue me nowe herewith, sayeth the Lord of hostes, if I will not open the windowes of heauen vnto you, and powre you out a blessing without measure.
11 Zan hana ƙwari su cinye hatsinku. Kuringar inabi a gonakinku kuma ba za su zubar da’ya’yansu kafin su nuna ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
And I will rebuke the deuourer for your sakes, and he shall not destroy the fruite of your grounde, neither shall your vine be baren in the fielde, sayeth the Lord of hostes.
12 “Sa’an nan dukan al’ummai za su ce da ku masu albarka, gama ƙasarku za tă yi daɗin zama,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
And all nations shall call you blessed: for ye shall be a pleasant lande, sayeth the Lord of hostes.
13 “Kun faɗi mugayen abubuwa a kaina,” in ji Ubangiji. “Duk da haka kuka ce, ‘Me muka faɗa a kanka?’
Your wordes haue bene stout against me, sayeth the Lord: yet ye say, What haue we spoken against thee?
14 “Kun ce, ‘Ba amfani a bauta wa Allah. Wanda amfani muka samu ta wurin kiyaye umarnansa muna yawo kamar masu makoki a gaban Ubangiji Maɗaukaki?
Ye haue saide, It is in vaine to serue God: and what profite is it that we haue kept his commandement, and that we walked humbly before the Lord of hostes?
15 A ganinmu, masu girman kai suna jin daɗi. Masu aikata mugunta kuwa ba arziki kaɗai suka yi ba, amma sukan gwada Allah da mugayen ayyukansu, su kuwa zauna lafiya.’”
Therefore wee count the proude blessed: euen they that worke wickednesse, are set vp, and they that tempt God, yea, they are deliuered.
16 Sa’an nan waɗanda suke tsoron Ubangiji suka yi magana da juna, Ubangiji kuwa ya kasa kunne ya kuma ji. A gabansa aka rubuta a littafin tarihi waɗanda suke tsoron Ubangiji, suna kuma girmama sunansa.
Then spake they that feared the Lord, euery one to his neighbour, and the Lord hearkened and heard it, and a booke of remembrance was written before him for them that feared the Lord, and that thought vpon his Name.
17 “A ranar da na shirya ajiyayyen mallakata, za su zama nawa,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan ji kansu kamar yadda mahaifi cikin tausayi yakan ji kan ɗansa wanda yake masa hidima.
And they shall be to me, sayeth the Lord of hostes, in that day that I shall do this, for a flocke, and I will spare them, as a man spareth his owne sonne that serueth him.
18 Za ku kuma ga bambanci tsakanin masu adalci da mugaye, tsakanin waɗanda suke wa Allah hidima da kuma waɗanda ba sa yi.
Then shall you returne, and discerne betweene the righteous and wicked, betweene him that serueth God, and him that serueth him not.

< Malaki 3 >