< Malaki 3 >

1 “Duba, zan aika manzona, wanda zai shirya hanya a gabana. Sa’an nan a farat ɗaya Ubangiji wanda kuke nema zai zo haikalinsa. Manzon alkawari, wanda kuke sa zuciya kuwa zai zo,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Look! I am sending my messenger, and he will prepare the way for me. The Lord you are seeking will suddenly arrive at his Temple. The messenger of the agreement you say is so happy with you is coming, says the Lord Almighty.
2 Amma wa zai jure wa ranar zuwansa? Wa zai iya tsaya sa’ad da ya bayyana? Gama zai zama kamar wuta mai tace ƙarfe, ko sabulu mai wanki.
Who can survive the day when he comes? Who can stand before him when he appears? For he will be like a blazing furnace that refines metal, or like the strong alkali that cleanses stains.
3 Zai zama kamar mai tace azurfa da mai tsarkaketa; zai tsabtacce Lawiyawa, yă kuma tace su kamar zinariya da azurfa. Sa’an nan Ubangiji zai sami mutanen da za su kawo hadayu a cikin adalci.
He will sit down like a refiner who purifies silver; he will purify Levi's descendants and refine them like gold and silver so they can present pure offerings to the Lord.
4 Hadayun Yahuda da na Urushalima za su zama yardajje ga Ubangiji, za su zama kamar a kwanakin da suka wuce, kamar a shekarun baya.
Then the offerings of Judah and Jerusalem will please the Lord as they did in the old days, in the former years.
5 “Ta haka zan zo kusa da ku don in yi hukunci. Zan hanzarta ba da shaida a kan masu yin sihiri, da mazinata da masu shaidar zur. Zan ba da shaida a kan waɗanda suke zaluntar ma’aikata a kan albashinsu, da waɗanda suke ƙwarar gwauraye da marayu, suna kuma hana baƙi samun adalci, ba sa ma tsorona,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
I will come and put you on trial. I am ready to be a witness against those who: practice witchcraft commit adultery tell lies give false evidence cheat employees oppress widows and orphans abuse foreigners and do not respect me, says the Lord Almighty.
6 “Ni Ubangiji ba na canjawa. Shi ya sa ku zuriyar Yaƙub, ba a hallaka ku ƙaƙaf ba.
For I am the Lord, I don't change, and you haven't stopped being descendants of Jacob.
7 Tun zamanin kakanninku, kun juye wa ƙa’idodina baya, ba ku kuma kiyaye su ba. Ku komo gare ni, ni kuma zan koma gare ku,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya za mu koma gare ka?’
From the time of your forefathers onward, you have turned away from my laws and not kept them. Return to me, and I will return to you, says the Lord Almighty. But you ask, “How should we return?”
8 “Mutum zai iya yi wa Allah fashi ne? Duk da haka kun yi mini fashi. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya muka yi maka fashi?’ “A wajen zakka da hadayu.
Should people defraud God? Yet you are defrauding me! But you ask, “How have we defrauded you?” In tithes and offerings.
9 Kuna ƙarƙashin la’ana, dukan al’ummarku, domin kuna yin mini fashi.
You are under a curse, for you and the whole nation are defrauding me.
10 Ku kawo dukan zakka cikin gidan ajiya, don a kasance da abinci a gidana. Ku gwada ni a wannan ku ga, ko ba zan buɗe taskokin sama in zubo muku albarka mai yawa, wadda har ba za ku rasa wurin sa ta ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Bring the full tithe into the storehouse so that there will be food in my Temple. Put me to the test in this, says the Lord Almighty, and I will open the windows of heaven and pour out so much blessing that you won't have enough room for it.
11 Zan hana ƙwari su cinye hatsinku. Kuringar inabi a gonakinku kuma ba za su zubar da’ya’yansu kafin su nuna ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
I will prevent locusts from destroying your crops, and your vineyards will not fail to bear fruit, says the Lord Almighty.
12 “Sa’an nan dukan al’ummai za su ce da ku masu albarka, gama ƙasarku za tă yi daɗin zama,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
All nations will call you blessed because you live in such a wonderful land, says the Lord Almighty.
13 “Kun faɗi mugayen abubuwa a kaina,” in ji Ubangiji. “Duk da haka kuka ce, ‘Me muka faɗa a kanka?’
You have said hard things about me, says the Lord. But you say, “What have we said against you?”
14 “Kun ce, ‘Ba amfani a bauta wa Allah. Wanda amfani muka samu ta wurin kiyaye umarnansa muna yawo kamar masu makoki a gaban Ubangiji Maɗaukaki?
You have said, “What's the point of serving God? What benefit is there in keeping his commandments or going before the Lord Almighty with long faces?
15 A ganinmu, masu girman kai suna jin daɗi. Masu aikata mugunta kuwa ba arziki kaɗai suka yi ba, amma sukan gwada Allah da mugayen ayyukansu, su kuwa zauna lafiya.’”
From now on we'll say that the proud are blessed. Evil people do well, and nothing happens when they dare God to punish them.”
16 Sa’an nan waɗanda suke tsoron Ubangiji suka yi magana da juna, Ubangiji kuwa ya kasa kunne ya kuma ji. A gabansa aka rubuta a littafin tarihi waɗanda suke tsoron Ubangiji, suna kuma girmama sunansa.
Then those who truly respected the Lord spoke to each other, and the Lord heard what they said. A scroll of remembrance was written in his presence of those who respected the Lord and paid attention to him.
17 “A ranar da na shirya ajiyayyen mallakata, za su zama nawa,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan ji kansu kamar yadda mahaifi cikin tausayi yakan ji kan ɗansa wanda yake masa hidima.
They shall be mine, says the Lord Almighty, my prized possession on the day when I take action. I will treat them kindly, as a father treats an obedient son.
18 Za ku kuma ga bambanci tsakanin masu adalci da mugaye, tsakanin waɗanda suke wa Allah hidima da kuma waɗanda ba sa yi.
Then you will once again be able to distinguish those who do right from those who do wrong, between those who serve him and those who don't.

< Malaki 3 >