< Malaki 3 >

1 “Duba, zan aika manzona, wanda zai shirya hanya a gabana. Sa’an nan a farat ɗaya Ubangiji wanda kuke nema zai zo haikalinsa. Manzon alkawari, wanda kuke sa zuciya kuwa zai zo,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Behold, I send my angel, and he will prepare the way before my face. And presently the Sovereign, whom you seek, and the angel of testimony, whom you desire, will arrive at his temple. Behold, he approaches, says the Lord of hosts.
2 Amma wa zai jure wa ranar zuwansa? Wa zai iya tsaya sa’ad da ya bayyana? Gama zai zama kamar wuta mai tace ƙarfe, ko sabulu mai wanki.
And who will be able to consider the day of his advent, and who will stand firm in order to see him? For he is like a refining fire, and like the fuller’s herb.
3 Zai zama kamar mai tace azurfa da mai tsarkaketa; zai tsabtacce Lawiyawa, yă kuma tace su kamar zinariya da azurfa. Sa’an nan Ubangiji zai sami mutanen da za su kawo hadayu a cikin adalci.
And he will sit refining and cleansing the silver, and he will purge the sons of Levi, and he will gather them like gold and like silver, and they will offer sacrifices to the Lord in justice.
4 Hadayun Yahuda da na Urushalima za su zama yardajje ga Ubangiji, za su zama kamar a kwanakin da suka wuce, kamar a shekarun baya.
And the sacrifice of Judah and of Jerusalem will please the Lord, just as in the days of past generations, and as in the ancient years.
5 “Ta haka zan zo kusa da ku don in yi hukunci. Zan hanzarta ba da shaida a kan masu yin sihiri, da mazinata da masu shaidar zur. Zan ba da shaida a kan waɗanda suke zaluntar ma’aikata a kan albashinsu, da waɗanda suke ƙwarar gwauraye da marayu, suna kuma hana baƙi samun adalci, ba sa ma tsorona,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
And I will approach you in judgment, and I will be a swift witness against evil-doers, and adulterers, and perjurers, and those who cheat the hired hand in his wages, the widows and the orphans, and who oppress the traveler, and who have not feared me, says the Lord of hosts.
6 “Ni Ubangiji ba na canjawa. Shi ya sa ku zuriyar Yaƙub, ba a hallaka ku ƙaƙaf ba.
For I am the Lord, and I do not change. And you, the sons of Jacob, have not been consumed.
7 Tun zamanin kakanninku, kun juye wa ƙa’idodina baya, ba ku kuma kiyaye su ba. Ku komo gare ni, ni kuma zan koma gare ku,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya za mu koma gare ka?’
For, from the days of your fathers, you have withdrawn from my ordinances and have not kept them. Return to me, and I will return to you, says the Lord of hosts. And you have said, “In what way, shall we return?”
8 “Mutum zai iya yi wa Allah fashi ne? Duk da haka kun yi mini fashi. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya muka yi maka fashi?’ “A wajen zakka da hadayu.
If a man will afflict God, then you greatly afflict me. And you have said, “In what way, do we afflict you?” In tithes and in first-fruits.
9 Kuna ƙarƙashin la’ana, dukan al’ummarku, domin kuna yin mini fashi.
And you have been cursed with privation, and you greatly afflict me, even your entire people.
10 Ku kawo dukan zakka cikin gidan ajiya, don a kasance da abinci a gidana. Ku gwada ni a wannan ku ga, ko ba zan buɗe taskokin sama in zubo muku albarka mai yawa, wadda har ba za ku rasa wurin sa ta ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Bring all the tithes into the storehouse, and let there be food in my house. And test me about this, says the Lord, as to whether I will not open to you the floodgates of heaven, and pour out to you a blessing, all the way to abundance.
11 Zan hana ƙwari su cinye hatsinku. Kuringar inabi a gonakinku kuma ba za su zubar da’ya’yansu kafin su nuna ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
And I will rebuke for your sakes the devourer, and he will not corrupt the fruit of your land. Neither will the vine in the field be barren, says the Lord of hosts.
12 “Sa’an nan dukan al’ummai za su ce da ku masu albarka, gama ƙasarku za tă yi daɗin zama,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
And all nations will call you blessed. For you will be a desirable land, says the Lord of hosts.
13 “Kun faɗi mugayen abubuwa a kaina,” in ji Ubangiji. “Duk da haka kuka ce, ‘Me muka faɗa a kanka?’
Your words have gathered strength over me, says the Lord.
14 “Kun ce, ‘Ba amfani a bauta wa Allah. Wanda amfani muka samu ta wurin kiyaye umarnansa muna yawo kamar masu makoki a gaban Ubangiji Maɗaukaki?
And you have said, “What have we spoken against you?” You have said, “He labors in vain who serves God,” and, “What advantage is it that we have kept his precepts, and that we have walked sorrowfully in the sight of the Lord of hosts?”
15 A ganinmu, masu girman kai suna jin daɗi. Masu aikata mugunta kuwa ba arziki kaɗai suka yi ba, amma sukan gwada Allah da mugayen ayyukansu, su kuwa zauna lafiya.’”
Now, therefore, we call the arrogant blessed, as if those who work impiety have been built up, and as if they have tempted God and been saved.
16 Sa’an nan waɗanda suke tsoron Ubangiji suka yi magana da juna, Ubangiji kuwa ya kasa kunne ya kuma ji. A gabansa aka rubuta a littafin tarihi waɗanda suke tsoron Ubangiji, suna kuma girmama sunansa.
Then those who fear the Lord spoke, each one with his neighbor. And the Lord paid attention and heeded. And a book of remembrance was written in his sight, for those who fear the Lord and for those who consider his name.
17 “A ranar da na shirya ajiyayyen mallakata, za su zama nawa,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan ji kansu kamar yadda mahaifi cikin tausayi yakan ji kan ɗansa wanda yake masa hidima.
And they will be my special possession, says the Lord of hosts, on the day that I act. And I will spare them, just as a man spares his son who serves him.
18 Za ku kuma ga bambanci tsakanin masu adalci da mugaye, tsakanin waɗanda suke wa Allah hidima da kuma waɗanda ba sa yi.
And you shall be converted, and you will see the difference between the just and the impious, and between those who serve God and those who do not serve him.

< Malaki 3 >