< Malaki 2 >

1 “Yanzu fa wannan gargaɗi dominku ne, ku firistoci.
Og nu kommer dette bud til eder, I prester!
2 In ba ku saurara ba, in kuma ba ku sa zuciyarku ga girmama sunana ba, zan aukar muku da la’ana, zan kuma la’antar da albarkunku. I, na riga na la’anta su, domin ba ku sa zuciyarku ga girmama ni ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Dersom I ikke vil høre og ikke legge eder det på hjerte, så I gir mitt navn ære, sier Herren, hærskarenes Gud, så vil jeg sende forbannelsen mot eder og forbanne eders velsignelser; ja, jeg har alt forbannet dem, fordi I ikke legger eder det på hjerte.
3 “Saboda ku zan tsawata wa zuriyarku; zan watsa kashin dabbobin hadayunku a fuskokinku, a kuma kwashe ku tare da shi.
Se, jeg forbanner eders ætt og kaster møkk i ansiktet på eder, møkk av eders høitidsoffere; og I skal selv bli kastet op i den.
4 Za ku kuwa san cewa ni ne na aika muku da wannan gargaɗi domin alkawarina da Lawi yă ci gaba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Da skal I kjenne at jeg har sendt eder dette bud, forat det skal være min pakt med Levi, sier Herren, hærskarenes Gud.
5 “Alkawarina da shi, alkawari ne na rai da salama, wanda na ba shi; domin yă girmama ni, ya kuwa girmama ni, ya kuma ji tsoron sunana ƙwarai.
Den pakt jeg hadde med ham, lovte ham liv og lykke; det gav jeg ham forat han skulde frykte mig, og han fryktet mig og var forferdet for mitt navn.
6 Umarnin gaskiya yana a bakinsa, ba a kuma sami wani ƙarya a leɓunansa ba. Ya yi tafiya tare da ni cikin salama da adalci, ya kuwa juyo da mutane masu yawa daga zunubi.
Sannhets lov var i hans munn, og urett blev ikke funnet på hans leber; i fred og ærlighet vandret han med mig, og mange omvendte han fra misgjerning.
7 “Gama ya kamata leɓunan firist su kiyaye ilimi, ya kamata kuma mutane su nemi umarni daga bakinsa, domin shi ne manzon Ubangiji Maɗaukaki.
For en prests leber skal holde fast ved kunnskap, og lov skal hentes fra hans munn; for han er Herrens, hærskarenes Guds sendebud.
8 Amma sai kuka kauce hanya, ta wurin koyarwarku kuma kuka sa mutane da yawa suka yi tuntuɓe; kun keta alkawarin da na yi da Lawi,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Men I har veket av fra veien og har fått mange til å støte an mot loven; I har fordervet Levi-pakten, sier Herren, hærskarenes Gud.
9 “Saboda haka na sa a rena ku, a kuma wulaƙanta ku a gaban dukan mutane, domin ba ku bi hanyoyina ba amma kuka nuna sonkai a al’amuran shari’a.”
Derfor har også jeg gjort eder foraktet og ringe i alt folkets øine, fordi I ikke akter på mine veier, men gjør forskjell på folk for loven.
10 Ashe, ba Mahaifi guda dukanmu muke da shi ba? Ba Allah ɗaya ne ya halicce mu ba? Don me muka keta alkawarin kakanninmu ta wurin cin amanar juna?
Har vi ikke alle sammen én far? Har ikke en Gud skapt oss? Hvorfor er vi da troløse mot hverandre, så vi vanhelliger våre fedres pakt?
11 Yahuda ya ci amana. An yi abin kunya a Isra’ila da kuma a Urushalima. Yahuda ya ƙazantar da wuri mai tsarkin da Ubangiji yake ƙauna, ta wurin auren’yar wani baƙon allah.
Juda har vært troløs, og vederstyggelige ting er gjort i Israel og i Jerusalem; for Juda har vanhelliget Herrens helligdom, som han elsker, og har tatt en fremmed guds døtre til ekte.
12 Game da mutumin da ya aikata wannan, ko wane ne shi, bari Ubangiji yă yanke shi daga tentunan Yaƙub, ko da ma ya kawo hadayu ga Ubangiji Maɗaukaki.
Hos den mann som det gjør, skal Herren utrydde av Jakobs telter hver levende sjel, og den som bærer offergaver frem for Herren, hærskarenes Gud!
13 Ga kuma wani abin da kuke yi. Kukan cika bagaden Ubangiji da hawaye. Kukan yi kuka kuna ihu gama Ubangiji ba ya mai da hankali ga hadayunku ko yă karɓe su da farin ciki.
For det annet gjør I også dette: I dekker Herrens alter med tårer, med gråt og sukk, så han ikke mere ser på offergaven eller med velbehag tar imot noget av eders hånd.
14 Kukan ce, “Don me ba ya karɓan hadayunmu?” Ai, domin Ubangiji ya zama shaida tsakaninka da matar ƙuruciyarka, gama ka keta amanar da ka yi mata, ko da yake ita abokiyar zamanka ce, matar aurenka ta alkawari.
Og I sier: Hvorfor? Fordi Herren har vært vidne mellem dig og din ungdoms hustru, som du har vært troløs mot, enda hun er din ektemake og din hustru som du har inngått pakt med.
15 Ashe, Ubangiji bai maishe su ɗaya ba? Cikin jiki da ruhu, su nasa ne. Me ya sa suke ɗaya? Domin yana neman’ya’ya masu tsoron Allah. Saboda haka sai ka lura da kanka, kada kuma ka ci amanar matar ƙuruciyarka.
Men har ikke en gjort det og er enda blitt i live? Men hvad gjorde denne ene? Han vilde opnå den ætt Gud hadde lovt ham; men I skal ta vare på eders liv, og mot din ungdoms hustru må du ikke være troløs!
16 “Na ƙi kisan aure,” in ji Ubangiji, Allah na Isra’ila. “Na kuma ƙi mutumin da ya rufe kansa da tashin hankali kamar riga,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. Saboda haka sai ka lura da kanka, kada kuma ka ci amana.
For jeg hater skilsmisse, sier Herren, Israels Gud; en dekker derved sitt klædebon med vold, sier Herren, hærskarenes Gud. Så ta da vare på eders liv og vær ikke troløse!
17 Kun sa Ubangiji Maɗaukaki ya gaji da maganganunku. Sai kuka ce, “Yaya muka sa ya gaji?” Kun yi haka ta wurin cewa, “Duk waɗanda suke aikata mugunta, mutanen kirki ne a gaban Ubangiji, yana kuwa jin daɗinsu,” kuna kuma cewa, “Ina Allah mai adalci yake?”
I har trettet Herren med eders ord, og I sier: Hvorledes har vi trettet ham? Ved å si: Hver den som gjør ondt, er god i Herrens øine, og i sådanne har han velbehag, eller: Hvor er Gud, han som dømmer?

< Malaki 2 >