< Malaki 2 >
1 “Yanzu fa wannan gargaɗi dominku ne, ku firistoci.
Khathesi-ke, bapristi, umlayo lo ngowenu.
2 In ba ku saurara ba, in kuma ba ku sa zuciyarku ga girmama sunana ba, zan aukar muku da la’ana, zan kuma la’antar da albarkunku. I, na riga na la’anta su, domin ba ku sa zuciyarku ga girmama ni ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Uba lingalaleli, njalo uba lingakubeki enhliziyweni ukunika ibizo lami udumo, itsho iNkosi yamabandla, ngizathumela isiqalekiso phakathi kwenu, ngiqalekise izibusiso zenu. Yebo, sengiziqalekisile, ngoba kalikubeki enhliziyweni.
3 “Saboda ku zan tsawata wa zuriyarku; zan watsa kashin dabbobin hadayunku a fuskokinku, a kuma kwashe ku tare da shi.
Khangelani, ngizakona inzalo yenu, ngithele umswane ebusweni benu, umswane wamadili enu, lisuswe kanye lawo.
4 Za ku kuwa san cewa ni ne na aika muku da wannan gargaɗi domin alkawarina da Lawi yă ci gaba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Njalo lizakwazi ukuthi ngithumele lumlayo kini, ukuze isivumelwano sami sibe loLevi, itsho iNkosi yamabandla.
5 “Alkawarina da shi, alkawari ne na rai da salama, wanda na ba shi; domin yă girmama ni, ya kuwa girmama ni, ya kuma ji tsoron sunana ƙwarai.
Isivumelwano sami besilaye siyikuphila lokuthula; ngamnika khona kube yikwesaba angesaba ngakho; wathuthumela phambi kwebizo lami.
6 Umarnin gaskiya yana a bakinsa, ba a kuma sami wani ƙarya a leɓunansa ba. Ya yi tafiya tare da ni cikin salama da adalci, ya kuwa juyo da mutane masu yawa daga zunubi.
Umlayo weqiniso wawusemlonyeni wakhe, lesiphambeko kasitholakalanga endebeni zakhe. Wahamba lami ngokuthula langobuqotho, waphendula abanengi ebubini.
7 “Gama ya kamata leɓunan firist su kiyaye ilimi, ya kamata kuma mutane su nemi umarni daga bakinsa, domin shi ne manzon Ubangiji Maɗaukaki.
Ngoba indebe zompristi ziyagcina ulwazi, njalo bayadinga umlayo emlonyeni wakhe, ngoba uyisithunywa seNkosi yamabandla.
8 Amma sai kuka kauce hanya, ta wurin koyarwarku kuma kuka sa mutane da yawa suka yi tuntuɓe; kun keta alkawarin da na yi da Lawi,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Kodwa lina liphambukile endleleni, lakhubekisa abanengi emlayweni; lona isivumelwano sikaLevi, itsho iNkosi yamabandla.
9 “Saboda haka na sa a rena ku, a kuma wulaƙanta ku a gaban dukan mutane, domin ba ku bi hanyoyina ba amma kuka nuna sonkai a al’amuran shari’a.”
Ngakho lami ngilenzile laba ngabadelelekayo labehliselwe phansi phambi kwabantu bonke, njengokuba lingagcinanga izindlela zami, kodwa lamukele ubuso emlayweni.
10 Ashe, ba Mahaifi guda dukanmu muke da shi ba? Ba Allah ɗaya ne ya halicce mu ba? Don me muka keta alkawarin kakanninmu ta wurin cin amanar juna?
Kasilababa munye yini thina sonke? UNkulunkulu munye kasidalanga yini? Kungani sisenza ngenkohliso, omunye emelene lomfowabo, ngokungcolisa isivumelwano sabobaba?
11 Yahuda ya ci amana. An yi abin kunya a Isra’ila da kuma a Urushalima. Yahuda ya ƙazantar da wuri mai tsarkin da Ubangiji yake ƙauna, ta wurin auren’yar wani baƙon allah.
UJuda wenze ngenkohliso, njalo kwenziwe amanyala koIsrayeli leJerusalema; ngoba uJuda ungcolisile ubungcwele bukaJehova abuthandayo, uthethe indodakazi kankulunkulu wezizweni.
12 Game da mutumin da ya aikata wannan, ko wane ne shi, bari Ubangiji yă yanke shi daga tentunan Yaƙub, ko da ma ya kawo hadayu ga Ubangiji Maɗaukaki.
INkosi izaquma umuntu owenza lokhu, ovusayo lophendulayo, asuke emathenteni kaJakobe, lalowo oletha umnikelo eNkosini yamabandla.
13 Ga kuma wani abin da kuke yi. Kukan cika bagaden Ubangiji da hawaye. Kukan yi kuka kuna ihu gama Ubangiji ba ya mai da hankali ga hadayunku ko yă karɓe su da farin ciki.
Lalokhu likwenzile kabili; lisibekela ilathi leNkosi ngezinyembezi, ngokukhala, langokububula, okungangokuthi kayisawunanzi umnikelo, kumbe ukuwemukela ngokuthokoza esandleni senu.
14 Kukan ce, “Don me ba ya karɓan hadayunmu?” Ai, domin Ubangiji ya zama shaida tsakaninka da matar ƙuruciyarka, gama ka keta amanar da ka yi mata, ko da yake ita abokiyar zamanka ce, matar aurenka ta alkawari.
Kanti lithi: Kungani? Kungoba iNkosi yayingumfakazi phakathi kwakho lomfazi wobutsha bakho, wena omphethe ngenkohliso, kanti engumngane wakho, lomfazi wesivumelwano sakho.
15 Ashe, Ubangiji bai maishe su ɗaya ba? Cikin jiki da ruhu, su nasa ne. Me ya sa suke ɗaya? Domin yana neman’ya’ya masu tsoron Allah. Saboda haka sai ka lura da kanka, kada kuma ka ci amanar matar ƙuruciyarka.
Kenzanga yini oyedwa? Njalo elomoya oseleyo. Njalo kungani oyedwa? Wadinga inzalo kaNkulunkulu. Ngakho qaphelisani ngomoya wenu, njalo kakungabi lophatha umfazi wobutsha bakhe ngenkohliso.
16 “Na ƙi kisan aure,” in ji Ubangiji, Allah na Isra’ila. “Na kuma ƙi mutumin da ya rufe kansa da tashin hankali kamar riga,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. Saboda haka sai ka lura da kanka, kada kuma ka ci amana.
Ngoba iNkosi uNkulunkulu kaIsrayeli ithi iyazonda ukwalana. Ngoba omunye usibekela udlakela ngesembatho sakhe, itsho iNkosi yamabandla. Ngakho qaphelisani ngomoya wenu, ukuze lingenzi ngenkohliso.
17 Kun sa Ubangiji Maɗaukaki ya gaji da maganganunku. Sai kuka ce, “Yaya muka sa ya gaji?” Kun yi haka ta wurin cewa, “Duk waɗanda suke aikata mugunta, mutanen kirki ne a gaban Ubangiji, yana kuwa jin daɗinsu,” kuna kuma cewa, “Ina Allah mai adalci yake?”
Liyidinisile iNkosi ngamazwi enu. Kanti lithi: Siyidinise ngani? Ngokuthi kwenu: Wonke owenza okubi ulungile emehlweni eNkosi, njalo iyathokoza ngabo; kumbe: Ungaphi uNkulunkulu wesahlulelo?