< Malaki 2 >
1 “Yanzu fa wannan gargaɗi dominku ne, ku firistoci.
And now, O ye priests, this commandment is for you.
2 In ba ku saurara ba, in kuma ba ku sa zuciyarku ga girmama sunana ba, zan aukar muku da la’ana, zan kuma la’antar da albarkunku. I, na riga na la’anta su, domin ba ku sa zuciyarku ga girmama ni ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
If ye will not hear, and if ye will not lay it to heart, to give glory to my name, says Jehovah of hosts, then I will send the curse upon you, and I will curse your blessings. Yea, I have cursed them already, because ye do not lay it to heart.
3 “Saboda ku zan tsawata wa zuriyarku; zan watsa kashin dabbobin hadayunku a fuskokinku, a kuma kwashe ku tare da shi.
Behold, I will rebuke your seed, and will spread dung upon your faces, even the dung of your feasts, and ye shall be taken away with it.
4 Za ku kuwa san cewa ni ne na aika muku da wannan gargaɗi domin alkawarina da Lawi yă ci gaba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
And ye shall know that I have sent this commandment to you, that my covenant may be with Levi, says Jehovah of hosts.
5 “Alkawarina da shi, alkawari ne na rai da salama, wanda na ba shi; domin yă girmama ni, ya kuwa girmama ni, ya kuma ji tsoron sunana ƙwarai.
My covenant of life and peace was with him. And I gave them to him that he might fear, and he feared me, and stood in awe of my name.
6 Umarnin gaskiya yana a bakinsa, ba a kuma sami wani ƙarya a leɓunansa ba. Ya yi tafiya tare da ni cikin salama da adalci, ya kuwa juyo da mutane masu yawa daga zunubi.
The law of truth was in his mouth, and unrighteousness was not found in his lips. He walked with me in peace and uprightness, and turned many away from iniquity.
7 “Gama ya kamata leɓunan firist su kiyaye ilimi, ya kamata kuma mutane su nemi umarni daga bakinsa, domin shi ne manzon Ubangiji Maɗaukaki.
For the priest's lips should keep knowledge, and they should seek the law at his mouth. For he is the messenger of Jehovah of hosts.
8 Amma sai kuka kauce hanya, ta wurin koyarwarku kuma kuka sa mutane da yawa suka yi tuntuɓe; kun keta alkawarin da na yi da Lawi,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
But ye are turned aside out of the way. Ye have caused many to stumble in the law. Ye have corrupted the covenant of Levi, says Jehovah of hosts.
9 “Saboda haka na sa a rena ku, a kuma wulaƙanta ku a gaban dukan mutane, domin ba ku bi hanyoyina ba amma kuka nuna sonkai a al’amuran shari’a.”
Therefore I also have made you contemptible and base before all the people, according as ye have not kept my ways, but have had respect of persons in the law.
10 Ashe, ba Mahaifi guda dukanmu muke da shi ba? Ba Allah ɗaya ne ya halicce mu ba? Don me muka keta alkawarin kakanninmu ta wurin cin amanar juna?
Have we not all one father? Has not one God created us? Why do we deal treacherously every man against his brother, profaning the covenant of our fathers?
11 Yahuda ya ci amana. An yi abin kunya a Isra’ila da kuma a Urushalima. Yahuda ya ƙazantar da wuri mai tsarkin da Ubangiji yake ƙauna, ta wurin auren’yar wani baƙon allah.
Judah has dealt treacherously, and an abomination is committed in Israel and in Jerusalem. For Judah has profaned the holiness of Jehovah which he loves, and has married the daughter of a foreign god.
12 Game da mutumin da ya aikata wannan, ko wane ne shi, bari Ubangiji yă yanke shi daga tentunan Yaƙub, ko da ma ya kawo hadayu ga Ubangiji Maɗaukaki.
Jehovah will cut off out of the tents of Jacob, the man who does this: him who wakes, and him who answers, and him who offers an offering to Jehovah of hosts.
13 Ga kuma wani abin da kuke yi. Kukan cika bagaden Ubangiji da hawaye. Kukan yi kuka kuna ihu gama Ubangiji ba ya mai da hankali ga hadayunku ko yă karɓe su da farin ciki.
And this again ye do: Ye cover the altar of Jehovah with tears, with weeping, and with sighing, insomuch that he does not regard the offering any more, nor receives it with good will at your hand.
14 Kukan ce, “Don me ba ya karɓan hadayunmu?” Ai, domin Ubangiji ya zama shaida tsakaninka da matar ƙuruciyarka, gama ka keta amanar da ka yi mata, ko da yake ita abokiyar zamanka ce, matar aurenka ta alkawari.
Yet ye say, Why? Because Jehovah has been witness between thee and the wife of thy youth, against whom thou have dealt treacherously, though she is thy companion, and the wife of thy covenant.
15 Ashe, Ubangiji bai maishe su ɗaya ba? Cikin jiki da ruhu, su nasa ne. Me ya sa suke ɗaya? Domin yana neman’ya’ya masu tsoron Allah. Saboda haka sai ka lura da kanka, kada kuma ka ci amanar matar ƙuruciyarka.
And did he not make one, although he had the residue of the Spirit? And why one? He sought a godly seed. Therefore take heed to your spirit, and let none deal treacherously against the wife of his youth.
16 “Na ƙi kisan aure,” in ji Ubangiji, Allah na Isra’ila. “Na kuma ƙi mutumin da ya rufe kansa da tashin hankali kamar riga,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. Saboda haka sai ka lura da kanka, kada kuma ka ci amana.
For I hate putting away, says Jehovah, the God of Israel, and him who covers his garment with violence, says Jehovah of hosts. Therefore take heed to your spirit, that ye deal not treacherously.
17 Kun sa Ubangiji Maɗaukaki ya gaji da maganganunku. Sai kuka ce, “Yaya muka sa ya gaji?” Kun yi haka ta wurin cewa, “Duk waɗanda suke aikata mugunta, mutanen kirki ne a gaban Ubangiji, yana kuwa jin daɗinsu,” kuna kuma cewa, “Ina Allah mai adalci yake?”
Ye have wearied Jehovah with your words. Yet ye say, How have we wearied him? In that ye say, Everyone who does evil is good in the sight of Jehovah, and he delights in them, or Where is the God of justice?