< Malaki 1 >

1 Annabci, wannan ita ce maganar Ubangiji ga Isra’ila ta wurin Malaki.
Pa inge kas su LEUM GOD El sang nu sel Malachi in fahkak nu sin mwet Israel.
2 “Na ƙaunace ku, in ji Ubangiji. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya ka ƙaunace mu?’ “Isuwa ba ɗan’uwan Yaƙub ba ne?” In ji Ubangiji. “Duk da haka na ƙaunaci Yaƙub,
LEUM GOD El fahk nu sin mwet lal, “Nga nuna lungse kowos pacl nukewa.” Tusruktu elos topuk fahk, “Kom akkalemye lungse lom nu sesr fuka?” LEUM GOD El topuk, “Esau ac Jacob eltal tamulel, tuh nga lungse Jacob ac fwil natul,
3 amma na ƙi Isuwa, na kuma mai da ƙasarsa da take kan duwatsu kango, na ba da gādonsa ga dilolin hamada.”
ac nga srungal Esau ac fwil natul. Nga sukela acn sel Esau ac sang fulan eol we tuh in nien muta lun kosro lemnak.”
4 Edom zai iya cewa, “Ko da yake an ragargaza mu, ai, za mu sāke gina kufanmu.” Amma ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Za su iya gini, amma zan rushe. Za a ce da su Muguwar Ƙasa, mutane da kullum suke a ƙarƙashi fushin Ubangiji.
Mwet Edom, su fwil natul Esau, fin fahk, “Siti sesr kunausyukla, tusruktu kut ac fah sifilpa musaeak,” na LEUM GOD El fah topuk, “Lela elos in sifil musai — nga fah sifil kunausla. Ac fah pangpang elos, ‘Sie facl koluk,’ ac ‘Mutunfacl se su LEUM GOD El kasrkusrak se nwe tok!’”
5 Za ku ga wannan da idanunku ku kuma ce, ‘Ubangiji da girma yake, har gaba da iyakokin Isra’ila ma!’
Mwet Israel elos fah sifacna liye ma inge ke mutalos, ac elos ac fahk, “LEUM GOD El arulana ku, ac ku lal liyeyuk sayen facl Israel pac!”
6 “Ɗa yakan girmama mahaifinsa, bawa kuma yakan girmama maigidansa. In ni mahaifi ne, ina girman da ya dace da ni? In ni maigida ne, ina girman da ya dace da ni?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Ku firistoci, ku ne kuka rena sunana. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya muka rena sunanka?’
LEUM GOD Kulana El fahk nu sin mwet tol uh, “Sie wen el sunakin papa tumal, ac sie mwet kulansap el sunakin mwet kacto lal. Nga papa tomowos — efu kowos ku tia sunakinyu? Nga Mwet Kacto lowos — efu kowos ku tia akfulatyeyu? Kowos aksruksrukeyu, a kowos siyuk, ‘Kut aksruksruke kom fuka?’
7 “Kun ajiye abinci mai ƙazanta a kan bagadena. “Sai kuka ce, ‘Yaya muka ƙazantar da kai?’ “Ta wurin cewa teburin Ubangiji abin reni ne.
Ke kowos kisakin mwe mongo kolukla fin loang luk uh. Na kowos sifil siyuk, ‘Kut tia akfulatye kom fuka?’ Nga ac fahk nu suwos: ke kowos aklusrongtenye loang luk.
8 Sa’ad da kuka kawo makauniyar dabba don ku miƙa mini hadaya, wannan daidai ne? Sa’ad da kuka miƙa gurguwar dabba ko marar lafiya, wannan daidai ne? Ku gwada ba wa gwamnanku irin wannan ku gani! Kuna gani zai ji daɗinku? Zai karɓe ku ne?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
Ke kowos use soko kosro kun ku mas ku osaksak in kisakin nu sik, ya kowos nunku mu wangin ma koluk kac? Srike sangwin soko kain kosro se ingan nu sel governor — ya el ac insewowo suwos, ku oru kutena ma in kasrekowos?”
9 “To, firistoci yanzu ku gwada ku roƙi Allah yă yi mana alheri. Da irin hadayun nan a hannuwanku ne zai ji ku?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
Inge, kowos mwet tol, srike siyuk sin God Elan oru wo nu sesr. El ac tia topuk pre lowos uh, na ac fah ma lowos pa koluk uh.
10 “Kash, da ma wani daga cikinku ya rufe ƙofofin haikali don kada ku shiga, ku hura wuta marar amfani a bisa bagadena! Ba na jin daɗinku, ba zan kuwa karɓi hadaya daga hannuwanku ba” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
LEUM GOD Kulana El fahk, “Nga ke sie suwos in kaliya srungul ke Tempul, in kosrala kowos in tia akosak e fin loang luk uh ke wangin sripa. Nga tiana insewowo suwos. Nga fah tia eis mwe sang ma kowos us nu yuruk.
11 Sunana zai zama mai girma a cikin al’ummai, daga fitowar rana har zuwa fāɗuwarta. A kowane wuri za a miƙa wa sunana turare da tsabtacciyar hadaya domin sunana zai zama mai girma a cikin al’ummai, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Ke pacl faht uh takak nwe ke pacl faht uh tili, mwet in mutunfacl nukema faclu elos sunakinyu. Yen nukewa elos esukak mwe keng ac ase mwe kisa wowo nu sik. Elos nukewa akfulatyeyu!
12 “Amma kun ƙazantar da sunana ta wurin cewa ‘Teburin Ubangiji ya ƙazantu,’ kuka kuma yi magana a kan abincinsa kuna cewa, ‘Abin reni ne.’
Tusruktu kowos akkolukye loang luk ke kowos fahk mu wangin sripa, ac ke kowos kisakin mwe mongo koluk fac.
13 Kun kuma ce, ‘Mun gaji da irin wannan wahala!’ Kuna hura mini hancin reni,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Sa’ad da kuka kawo raunannu, gurguntattun dabbobi, ko kuma dabbobi masu fama da cuta, kuka kuma miƙa su hadaya, kuna gani zan karɓi wannan daga gare ku?” In ji Ubangiji.
Kowos fahk mu, ‘Kut totola ke oreyen ma inge uh!’ ac sungalik infwewos nu sik. Kowos use kosro pusrla, ku ma osaksak, ku mas, in kisakin nu sik. Ya kowos nunku mu nga ac eis ma ingan suwos?
14 “La’ananne ne macucin da yake da lafiyayyiyar dabba namiji a garkensa wadda ya yi alkawari zai bayar, amma sai ya miƙa hadayar dabba mai aibi ga Ubangiji. Gama ni babban sarki ne, za a kuma ji tsoron sunana a cikin al’ummai,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
In selngawiyuk mwet kutasrik se su kisakin soko kosro koluk lumah nu sik, ke oasr ma na wo ac fas soko inmasrlon un kosro natul, su el tuh wulema in kisakin nu sik! Tuh nga sie tokosra fulat, ac mwet in mutunfacl nukewa sangeng sik.”

< Malaki 1 >