< Malaki 1 >

1 Annabci, wannan ita ce maganar Ubangiji ga Isra’ila ta wurin Malaki.
[the] oracle of [the] word of Yahweh to Israel by [the] hand of Malachi.
2 “Na ƙaunace ku, in ji Ubangiji. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya ka ƙaunace mu?’ “Isuwa ba ɗan’uwan Yaƙub ba ne?” In ji Ubangiji. “Duk da haka na ƙaunaci Yaƙub,
I have loved you he says Yahweh and you say how? have you loved us ¿ not [did] a brother Esau [belong] to Jacob [the] utterance of Yahweh and I loved Jacob.
3 amma na ƙi Isuwa, na kuma mai da ƙasarsa da take kan duwatsu kango, na ba da gādonsa ga dilolin hamada.”
And Esau I hated and I have made mountains his a waste and inheritance his for jackals of [the] wilderness.
4 Edom zai iya cewa, “Ko da yake an ragargaza mu, ai, za mu sāke gina kufanmu.” Amma ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Za su iya gini, amma zan rushe. Za a ce da su Muguwar Ƙasa, mutane da kullum suke a ƙarƙashi fushin Ubangiji.
For it will say Edom we have been shattered and we may return so we may rebuild [the] ruins thus he says Yahweh of hosts they they will build and I I will tear down and people will call them a territory of wickedness and the people which he was indignant Yahweh until perpetuity.
5 Za ku ga wannan da idanunku ku kuma ce, ‘Ubangiji da girma yake, har gaba da iyakokin Isra’ila ma!’
And eyes your they will see and you you will say he is great Yahweh over [the] border of Israel.
6 “Ɗa yakan girmama mahaifinsa, bawa kuma yakan girmama maigidansa. In ni mahaifi ne, ina girman da ya dace da ni? In ni maigida ne, ina girman da ya dace da ni?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Ku firistoci, ku ne kuka rena sunana. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya muka rena sunanka?’
A son he honors a father and a servant master his and if [am] a father I where? [is] honor my and if [am] a master I where? [is] fear my he says - Yahweh of hosts to you O priests [who] despise name my and you say how? have we despised name your.
7 “Kun ajiye abinci mai ƙazanta a kan bagadena. “Sai kuka ce, ‘Yaya muka ƙazantar da kai?’ “Ta wurin cewa teburin Ubangiji abin reni ne.
[you are] bringing near On altar my food defiled and you say how? have we defiled you by saying you [the] table of Yahweh [is] despicable it.
8 Sa’ad da kuka kawo makauniyar dabba don ku miƙa mini hadaya, wannan daidai ne? Sa’ad da kuka miƙa gurguwar dabba ko marar lafiya, wannan daidai ne? Ku gwada ba wa gwamnanku irin wannan ku gani! Kuna gani zai ji daɗinku? Zai karɓe ku ne?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
And if you bring near! a blind [animal] to sacrifice not? [is it] evil and if you bring near a lame [animal] and a sick [animal] [is it] not? evil bring near it please to governor your ¿ will he be pleased with you or ¿ will he lift up face your he says Yahweh of hosts.
9 “To, firistoci yanzu ku gwada ku roƙi Allah yă yi mana alheri. Da irin hadayun nan a hannuwanku ne zai ji ku?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
And now entreat please [the] face of God so he may show favor to us from hand your it was this ¿ will he lift up any of you face he says Yahweh of hosts.
10 “Kash, da ma wani daga cikinku ya rufe ƙofofin haikali don kada ku shiga, ku hura wuta marar amfani a bisa bagadena! Ba na jin daɗinku, ba zan kuwa karɓi hadaya daga hannuwanku ba” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Who? also [is] among you so he may shut [the] doors and not you will set light to altar my in vain not [belongs] to me pleasure in you he says Yahweh of hosts and an offering not I will accept from hand your.
11 Sunana zai zama mai girma a cikin al’ummai, daga fitowar rana har zuwa fāɗuwarta. A kowane wuri za a miƙa wa sunana turare da tsabtacciyar hadaya domin sunana zai zama mai girma a cikin al’ummai, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
For from [the] rising of [the] sun and to setting its [is] great name my among the nations and in every place incense [is being] brought near to name my and an offering a pure for [is] great name my among the nations he says Yahweh of hosts.
12 “Amma kun ƙazantar da sunana ta wurin cewa ‘Teburin Ubangiji ya ƙazantu,’ kuka kuma yi magana a kan abincinsa kuna cewa, ‘Abin reni ne.’
And you [are] profaning it by saying you [the] table of [the] Lord [is] defiled it and fruit its [is] despicable food its.
13 Kun kuma ce, ‘Mun gaji da irin wannan wahala!’ Kuna hura mini hancin reni,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Sa’ad da kuka kawo raunannu, gurguntattun dabbobi, ko kuma dabbobi masu fama da cuta, kuka kuma miƙa su hadaya, kuna gani zan karɓi wannan daga gare ku?” In ji Ubangiji.
And you say there! what weariness! and you sniff at it he says Yahweh of hosts and you bring a stolen [animal] and the lame [animal] and the sick [animal] and you bring the offering ¿ will I accept it from hand your he says Yahweh.
14 “La’ananne ne macucin da yake da lafiyayyiyar dabba namiji a garkensa wadda ya yi alkawari zai bayar, amma sai ya miƙa hadayar dabba mai aibi ga Ubangiji. Gama ni babban sarki ne, za a kuma ji tsoron sunana a cikin al’ummai,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
And [be] cursed [one who] deals deceptively and there among flock his [is] a male and [one who] makes a vow and [one who] sacrifices a blemished [animal] to [the] Lord for [am] a king great I he says Yahweh of hosts and name my [is] feared among the nations.

< Malaki 1 >