< Malaki 1 >

1 Annabci, wannan ita ce maganar Ubangiji ga Isra’ila ta wurin Malaki.
The prophecy of the word of Jehovah, concerning Israel, by Malachi.
2 “Na ƙaunace ku, in ji Ubangiji. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya ka ƙaunace mu?’ “Isuwa ba ɗan’uwan Yaƙub ba ne?” In ji Ubangiji. “Duk da haka na ƙaunaci Yaƙub,
I have loved you, saith Jehovah. But ye say, “Wherein hast thou loved us?” Was not Esau Jacob's brother, saith Jehovah? Yet I loved Jacob,
3 amma na ƙi Isuwa, na kuma mai da ƙasarsa da take kan duwatsu kango, na ba da gādonsa ga dilolin hamada.”
And Esau I hated; And I made his mountains a desolation, And his inheritance to be habitations of the desert.
4 Edom zai iya cewa, “Ko da yake an ragargaza mu, ai, za mu sāke gina kufanmu.” Amma ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Za su iya gini, amma zan rushe. Za a ce da su Muguwar Ƙasa, mutane da kullum suke a ƙarƙashi fushin Ubangiji.
Although Edom say, “We are ruined, Yet will we build again the desolate places.” Thus saith Jehovah of hosts: They may build, but I will throw down; And men shall call them “The impious land, The people against whom Jehovah hath indignation forever.”
5 Za ku ga wannan da idanunku ku kuma ce, ‘Ubangiji da girma yake, har gaba da iyakokin Isra’ila ma!’
And your eyes shall see it, and ye shall say, “Great is Jehovah beyond the borders of Israel!”
6 “Ɗa yakan girmama mahaifinsa, bawa kuma yakan girmama maigidansa. In ni mahaifi ne, ina girman da ya dace da ni? In ni maigida ne, ina girman da ya dace da ni?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Ku firistoci, ku ne kuka rena sunana. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya muka rena sunanka?’
A son honoreth his father, And a servant his master; If I, then, be a father, where is mine honor? And if I be a master, where is my fear? Saith Jehovah of hosts to you, ye priests that despise my name. Ye say, “Wherein do we despise thy name?”
7 “Kun ajiye abinci mai ƙazanta a kan bagadena. “Sai kuka ce, ‘Yaya muka ƙazantar da kai?’ “Ta wurin cewa teburin Ubangiji abin reni ne.
Ye bring polluted food to mine altar. And ye say, “Wherein do we pollute thee?” In that ye say, “The table of Jehovah is contemptible.”
8 Sa’ad da kuka kawo makauniyar dabba don ku miƙa mini hadaya, wannan daidai ne? Sa’ad da kuka miƙa gurguwar dabba ko marar lafiya, wannan daidai ne? Ku gwada ba wa gwamnanku irin wannan ku gani! Kuna gani zai ji daɗinku? Zai karɓe ku ne?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
For when ye bring the blind for sacrifice, [[ye say, ]] “It is not evil.” And when ye offer the lame and the sick, [[Ye say, ]] “It is not evil.” Offer it, then, to thy governor; Will he be pleased with thee, Or have regard to thee? Saith Jehovah of hosts.
9 “To, firistoci yanzu ku gwada ku roƙi Allah yă yi mana alheri. Da irin hadayun nan a hannuwanku ne zai ji ku?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
And now, I pray you, beseech God to be gracious unto us! Since such things are done by you, Will he have regard to you, Saith Jehovah of hosts?
10 “Kash, da ma wani daga cikinku ya rufe ƙofofin haikali don kada ku shiga, ku hura wuta marar amfani a bisa bagadena! Ba na jin daɗinku, ba zan kuwa karɓi hadaya daga hannuwanku ba” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
O that some one of you would close the doors, That ye might not kindle the fire upon mine altar in vain! I have no pleasure in you, saith Jehovah of hosts, Neither will I accept an offering at your hand.
11 Sunana zai zama mai girma a cikin al’ummai, daga fitowar rana har zuwa fāɗuwarta. A kowane wuri za a miƙa wa sunana turare da tsabtacciyar hadaya domin sunana zai zama mai girma a cikin al’ummai, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
For from the rising of the sun even to the going down of the same My name shall be great among the nations. And in every place shall incense be offered to my name, And a pure offering; For my name shall be great among the nations, Saith Jehovah of hosts.
12 “Amma kun ƙazantar da sunana ta wurin cewa ‘Teburin Ubangiji ya ƙazantu,’ kuka kuma yi magana a kan abincinsa kuna cewa, ‘Abin reni ne.’
But ye profane it, In that ye say, “The table of Jehovah is polluted, And what is offered thereon, even its food, is contemptible.”
13 Kun kuma ce, ‘Mun gaji da irin wannan wahala!’ Kuna hura mini hancin reni,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Sa’ad da kuka kawo raunannu, gurguntattun dabbobi, ko kuma dabbobi masu fama da cuta, kuka kuma miƙa su hadaya, kuna gani zan karɓi wannan daga gare ku?” In ji Ubangiji.
Ye say also, “Behold, what weariness!” And ye snuff at it, Saith Jehovah of hosts; And ye bring that which is plundered, and lame, and sick, And present it for an offering; Shall I accept it at your hand? Saith Jehovah.
14 “La’ananne ne macucin da yake da lafiyayyiyar dabba namiji a garkensa wadda ya yi alkawari zai bayar, amma sai ya miƙa hadayar dabba mai aibi ga Ubangiji. Gama ni babban sarki ne, za a kuma ji tsoron sunana a cikin al’ummai,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Cursed be the deceiver, Who hath in his flock a male, And yet voweth and sacrificeth to Jehovah that which is marred; For I am a great king, saith Jehovah of hosts; And my name is terrible among the nations.

< Malaki 1 >