< Luka 9 >

1 Bayan da Yesu ya tara Sha Biyun wuri ɗaya, sai ya ba su iko da izini na fitar da dukan aljanu, da na warkar da cututtuka.
Jisua'n ruoisi sômleinik ngei hah a koibûma, an kôma, ramkhori rujûlpai theina le natnangei mindam theinangei le rachamneina a pêk ngeia.
2 Ya kuma aike su, su yi wa’azin mulkin Allah, su kuma warkar da marasa lafiya.
Male chu, Pathien Rêngram thurchi misîr rang le damloingei mindam rangin a tîrsuok ngei zoia.
3 Ya ce musu, “Kada ku ɗauki kome don tafiyar, wato, ba sanda, ba jaka, ba burodi, ba kuɗi, ba riga na biyu.
Hanchu, an kôma, “Khuolchaina rangin ite chôi no roi, sunrol mo, cholite mo, sum mo, bu mo, kancholi insak mo,” a tipe ngeia.
4 Duk gidan da kuka sauka, ku zauna nan sai kun bar garin.
“Nangni an lei modômna ina han, om tit ungla, ma khopui nin mâk nôk mâka chu.
5 In mutane ba su karɓe ku ba, sa’ad da kun bar garinsu, ku karkaɗe ƙurar ƙafafunku don shaida a kansu.”
Mi'n nangni an lei modôm nônchu, anni rilnân nin kea pildi hah khôngpai roi.”
6 Sai suka tashi suka shiga ƙauye zuwa ƙauye suna wa’azin bishara, suna warkar da marasa lafiya a ko’ina.
Hanchu rouisingei an sea, muntina thurchisa misîrin khuotina an chaia, damloingei an mindam tir zoi.
7 Yanzu fa, Hiridus mai sarauta ya ji labarin dukan abubuwan da suke faruwa. Sai ya rikice, don waɗansu mutane suna cewa, Yohanna Mai Baftisma ne ya tashi daga matattu,
Hanchu Galilee rama roijêkpu, Herod'n neinun omtie ngei a rieta anîn chu a mulung a jînga, senkhatin Baptispu John kêng a ring nôk an tipe sikin,
8 waɗansu kuma suna cewa, annabi Iliya ne ya sāke bayyana. Waɗansu kuma har wa yau, suna cewa, ɗaya daga cikin annabawa na dā ne, ya tashi.
Senkhatin Elijah kêng a juong inlâr nôk zoi, an ti, senkhatin tienlâia dêipu tumakhat kêng a ring nôk zoi an tia.
9 Amma Hiridus ya ce, “Yohanna dai na yanke kansa, amma wanne mutum ne nake jin labarin abubuwan nan a kansa?” Sai ya yi ƙoƙari ya ga Yesu.
Herod'n John lu laka ka tan zoia, hi ang taka thurchi ki riet hih tumo ai ni? tiin Jisua mu rangin a nuoma.
10 Da manzannin suka dawo, sai suka faɗa wa Yesu abin da suka yi. Sai ya ɗauke su, suka keɓe kansu su kaɗai, zuwa wani gari da ake kira Betsaida.
Hanchu, tîrton sômleinik ngei an hongkîr nôkin chu an sin va tho Jisua an rila. Hanchu, a kôm a tuong ngeia, Bethsaida khopuia atheiin a sepui ngei zoi.
11 Amma taron mutane suka ji labari, sai suka bi shi. Ya marabce su, kuma ya yi musu magana a kan mulkin Allah, ya kuma warkar da masu bukatar warkarwa.
Mipuiin an rietin chu an jûia. A modôm ngeia, Pathien Rêngram thurchi a misîr pe ngeia, mindam anâng ngei kai chu a mindam ngeia.
12 Da rana ta kusa fāɗuwa, sai Sha Biyun suka zo wurinsa, suka ce, “Ka sallami taron domin su shiga ƙauyuka na kewaye, su nemi abin da za su ci, da wurin kwana, don inda muke, ba kowa.”
Hanchu, kholoi ahong nîn chu, ruoisi sômleinik ngei an honga, a kôma, “Mipui ngei hih min se ngei ta roh, khopui sûnga le akôlrevêla bu le riamun an man theina rangin, ei omna lak mun inthim kêng ani” an tia.
13 Yesu ya ce, “Ku, ku ba su wani abu su ci.” Sai suka ce masa, “Muna da burodi biyar da kifi biyu kaɗai. Sai dai, in mun je mu sayi abinci domin dukan wannan taron.”
Ania Jisua'n an kôma, “Nangnin sâkruo pêk ngei roi” a tipe ngeia. “Annin, vâipôl tâp rangnga le nga inik mang kêng kin nei.
14 Maza kaɗai sun kai kusan dubu biyar. Amma ya ce wa almajiransa, “Ku sa su su zauna a ƙungiya hamsin-hamsin.”
Hi dôra pasal isâng rangnga sâk rang hih a rochôk rangin kin se rang mini?” tiin an thuona. Hanchu, Jisua'n a ruoisingei kôma, “Mipui hi sômranga ngân abukin min sung ngei roi,” a tia.
15 Haka almajiran suka yi, kowa kuwa ya zauna.
Hanchu, a ruoisingeiin a he bê angin mipui ngei hah an minsung ngeia.
16 Sai Yesu ya ɗauki burodin biyar da kifin biyun, ya ɗaga kansa sama, ya yi godiya, ya kuma kakkarya su. Ya ba wa almajiransa, domin su rarraba wa mutanen.
Hanchu, Jisua'n vâipôl rangnga le nga inik hah a lâka, invân tieng a tanga, Pathien kôm râisânchong a rila, a khoia, hanchu mipui ngei sem rangin a ruoisingei a pêka.
17 Duka kuwa suka ci suka ƙoshi. Almajiran suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna goma sha biyu.
Hanchu, anrêngin an khop dodôrin an sâk suonûkin, an sâk minieng, tâidôn sômleinik ruoisingeiin an rût minsip ani.
18 Wata rana sa’ad da Yesu yana addu’a a ɓoye, almajiransa kuma suna tare da shi, sai ya tambaye, su ya ce, “Wa, taron mutane ke ce da ni?”
Sûnkhat chu, Jisua'n atheiin chubai a thoa, a ruoisingei an honga, an kôma, “Mipuingeiin tumo min ti ngâi?” tiin a rekela.
19 Suka amsa, suka ce, “Waɗansu suna cewa, Yohanna Mai Baftisma, waɗansu kuma annabi Iliya, har wa yau waɗansu suna cewa, kai ɗaya daga cikin annabawan da ne, da ya tashi da rai.”
“Senkhatin, ‘Baptispu John’ senkhatin ‘Elijah,’ senkhatin tienlâia dêipu tumakhat, a juong nôk nang an ti ngâi,” tiin an thuona.
20 “Amma ku fa, wa, kuke ce da ni?” Bitrus ya amsa ya ce, “Kiristi na Allah.”
Hanchu, “nangnin te tumo minin ti?” tiin a rekel ngeia. Peter'n, “Messiah Pathien na ni” tiin a thuona.
21 Yesu ya gargaɗe su da ƙarfi, kada su gaya wa kowa wannan magana.
Hanchu, Jisua'n hi chong hih tute kôma misîr tet loi rangin chong a be ngeia.
22 Ya sāke cewa, “Dole ne Ɗan mutum ya sha wahaloli da yawa, dattawa, da manyan firistoci, da malaman dokoki kuma su ƙi shi, kuma dole a kashe shi, a rana ta uku kuma a tā da shi da rai.”
An kôma, “Miriem Nâipasal hi upangei, Ochaisingei, Balam minchupungeiin hengpai an ta, dengmanthei ok an tih. That an ta, ania, sûnthum suole chu a ringin inthoi nôk a tih,” a tia.
23 Sai ya ce wa dukansu, “In wani zai bi ni, dole yă mūsanta kansa, ya ɗauki gicciyensa kowace rana, ya bi ni.
Hanchu an rênga kôma, “Tutu, ni jûi a nuoma anîn chu ama in mingilin, anîngtin a khros ruputin ni jûi rese.
24 Gama duk mai son ceton ransa zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa saboda ni zai same shi.
Tutu, a ringna minjôk a nuom kaiin chu machân a ta, ania, keima sika a ringna machân kaiin ring an tih.
25 Ina amfani, in mutum ya ribato duniya duka, amma ya rasa ransa, ko kuma ya yi hasarar ransa.
Mîn rammuol hih apumin nei senla, a theiin inmangin mo, machânin mo om ta senla ata rangin imo ânlap!
26 Duk wanda yake jin kunyana da na kalmomina, Ɗan Mutum ma zai ji kunyarsa sa’ad da zai zo a cikin ɗaukakarsa, da ɗaukakar Uban, da kuma ta tsarkaka mala’ikun.
Mîn keima le ka thurchi inzakpui chu, Miriem Nâipasal khomin, a roiipuina leh Pa roiinpuina leh vântîrton inthieng ngei leh a juong tikin inzakpui a tih.
27 “Gaskiya nake gaya muku, waɗansu da suke tsattsaye a nan ba za su ga mutuwa ba, sai sun ga mulkin Allah.”
Hitaka senkhat ngei hin Pathien rêngram an mu mâka chu thi noni ngei iti riettit roi” a tia.
28 Bayan kamar kwana takwas da yin wannan magana, sai Yesu ya ɗauki Bitrus, da Yohanna, da kuma Yaƙub, suka hau kan dutse tare don yin addu’a.
Hi chong a misîr zoia, hapta khat suole chu, Jisua'n Peter, John le Jacob ngei hah muol chunga chubai tho rangin a tuong ngeia.
29 Yana cikin addu’a, sai kamannin fuskarsa ta sāke, tufafinsa kuma suka zama da haske kamar hasken walƙiya.
Hanchu, chubai a tho lâitakin a mâi ânthûla, a mêl le a puonsilngei khom avâr intêrrakin a oma.
30 Sai ga mutum biyu, Musa da Iliya, suka bayyana cikin kyakkyawar daraja, suna magana da Yesu.
Harenghan mi inik an juong oma, an chongpuia, Moses le Elijah an ni.
31 Suka yi zance a kan tashinsa, wanda shi ya kusan ya kawo ga cikarsa a Urushalima.
Invân roiinpuinân an juong inlâra, Pathien bôkna len ranga, Jerusalema Jisua thi rang tie an misîra.
32 Barci kuwa ya kama Bitrus da abokan tafiyarsa sosai. Da idanunsu suka warware, sai suka ga ɗaukakarsa da kuma mutum biyun tsaye tare da shi.
Peter le a champui ngei chu an inphara, an inthoiin chu Jisua roiinpuina le a kôma mi inik inding ngei an mua.
33 Da mutanen na barin Yesu, sai Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, ya yi kyau da muke nan. Bari mu kafa bukkoki guda uku, wato, ɗaya dominka, ɗaya domin Musa, ɗaya kuma domin Iliya.” (Bai ma san abin da yake faɗi ba.)
Mingei han Jisua an mak rangtôn chu, Peter'n a kôma, “Hitaka om hi eita rangin asa, puon in inthum nata rang inkhat, Moses rang inkhat le Elijah rang inkhat sin kin tih” a tia. (ha a chong ti hah asadimin riet minthâr mak)
34 Yayinda yake cikin magana, sai wani girgije ya bayyana ya rufe su, sai suka ji tsoro, yayinda suke shiga cikin girgijen.
A la chong lâitakin sûmin a juong minlia, an chunga sûmin a juong mukhûn chu ruoisingeiin an chia.
35 Wata murya ta fito daga cikin girgijen, tana cewa, “Wannan Ɗana ne, zaɓaɓɓena, ku saurare shi.”
Sûm renga rôlin, “Ama hih ka Nâipasal ka thangsuok chu ani, a chong rangâi roi” a tia.
36 Da muryar ta gama magana, sai suka tarar Yesu shi kaɗai ne. Almajiran kuwa suka riƙe wannan al’amari a zukatansu. A lokacin nan, ba su gaya wa kowa abin da suka gani ba.
Rôl amongin chu, Jisua vai a om zoia. ruoisingei han an neinun mu tute ril loiin an ip tita.
37 Kashegari, sa’ad da Yesu tare da almajiran nan uku suka sauka daga kan dutsen, sai taro mai yawa ya haɗu da shi.
Anangtûka Jisua le ruoisi inthum ngei hah muol chung renga an juong chumin chu mipui tamtak ngeiin an lei dona.
38 Sai wani mutum daga cikin taron ya yi kira da ƙarfi ya ce, “Malam, ina roƙonka, ka dubi ɗan nan nawa, gama shi ne kaɗai nake da shi.
Hanchu, mipuingei lâia mi inkhatin, “Minchupu, ka nâipasal, ke neisun hi en ta,” tia ngênin ân-ieka.
39 Wani ruhu yakan kama shi, sai ya yi ihu farar ɗaya. Yakan sa shi farfaɗiya, har bakinsa ya yi kumfa. Da ƙyar yake barinsa, yana kuwa kan hallakar da shi.
“Ramkhorin a sûra, a minleta, a cherhuon asuoka, a minna, inningloiin a min ieka, a vôr raka darnân a min se ngâia.
40 Na roƙi almajiranka su fitar da shi, amma ba su iya ba.”
A rujûlpai rangin nu ruoisingei ke ngên ngei lakin thei mak ngeia” a tia.
41 Yesu ya amsa ya ce, “Ya karkataccen zamani marar bangaskiya, har yaushe ne zan kasance tare da ku, ina kuma haƙuri da ku? Kawo yaronka nan.”
Jisua'n, “Iemna neiloi le mi puoloingei o! Iten sôt mo nin kôma omin nangni ko donsûi ranga? Na nâipasal hah hin hong tuong roh” a tia.
42 Yaron yana kan zuwa ke nan, sai aljanin ya buga shi ƙasa, cikin farfaɗiya. Amma Yesu ya kwaɓe mugun ruhun, ya warkar da yaron, sai ya miƙa shi ga mahaifinsa.
Hanchu nâipang hah a hongin chu, ramkhori han a nîka pila inngil rakin a vôra. Jisua'n ramkhori hah chong a pêka, nâipang hah a mindama, a pa kôma a pêk zoi.
43 Duk suka yi mamakin girman Allah. Yayinda kowa yana cikin mamakin dukan abubuwan da Yesu ya yi, sai ya ce wa almajiransa,
Pathien sinthotheina roiinpui hah mipui ngei murdi'n an kamâm ok ani. Mipui ngeiin Jisua sinthongei an kamâm lâiin, a ruoisingei kôma,
44 “Ku kasa kunne da kyau ga abin da zan faɗa muku. Za a bashe Ɗan Mutum ga hannun mutane.”
“Nangni ki ril rang hih mingil no roi, Miriem Nâipasal hih miriemngei kôma ipêk nîng a tih” a tia.
45 Amma ba su fahimci abin da yake nufi da wannan magana ba. Ba su gane ba, don an ɓoye musu shi. Su kuwa sun ji tsoro su tambaye shi.
Ania, ruoisingei lakin ai ti omtie hah rietthei mak ngeia. An riet thei loina ranga chong inthup ania, ama laka an chi sikin rekel ngam mak ngeia.
46 Wata gardama ta tashi a tsakanin almajiran, a kan ko wane ne a cikinsu zai zama mafi girma
Hanchu, ruoisingei han ei lâia tumo a lien rang tak tiin inkhalna an neia.
47 Da yake Yesu ya san tunaninsu, sai ya ɗauki wani ƙaramin yaro, ya sa ya tsaya kusa da shi.
Jisua'n an mindonna a rieta, nâipangte a kaia, a kôla a mindinga.
48 Sai ya ce musu, “Duk wanda ya karɓi wannan ƙaramin yaron a cikin sunana, ni ya karɓa, kuma duk wanda ya karɓe ni, ya karɓi wanda ya aiko ni ne. Gama mafi ƙanƙanta duka a cikinku, shi ne kuma mafi girma.”
An kôma, “Tutu, hi nâipangte ki riminga modôm chu, keima ni modôm ani; tutu keima ni modôm chu ni tîrpu modôm ani. Nin lâia a chintak hi a lientak ani,” a tipe ngeia.
49 Sai Yohanna ya ce, “Ubangiji, mun ga wani mutum yana fitar da aljanu a cikin sunanka, muka yi ƙoƙarin hana shi, don shi ba ɗaya ba ne daga cikinmu.”
John'n, “Minchupu, mi inkhatin ni rimingin, ramkhori a rujûlpaia, ei pâla mi ani loi sikin, kan khap” a tia.
50 Yesu ya ce, “Kada ku hana shi, gama duk wanda ba ya gāba da ku, naku ne.”
Jisua'n a kôma le adangngei kôma, “Khap no roi nangni chakal loi chu nin tienga kop ani” a tipe ngeia.
51 Da lokaci ya yi kusa da za a ɗauki Yesu zuwa sama, sai ya ɗaura niyyar tafiya Urushalima.
Jisua invâna a kal rang ni a hong nâia anîn chu, Jerusalema se rangin a mulungin a bôka, a se kelen zoi.
52 Sai ya aiki’yan saƙo, su yi gaba. Su kuwa, suka shiga cikin wani ƙauyen Samariyawa, don su shirya masa abubuwa.
A motona thangthei a tîra, ata ranga neinuntin lei cherêl rangin Samari khuo inkhata an lûta.
53 Amma mutanen ƙauyen ba su karɓe shi ba, don yana kan hanyar zuwa Urushalima ne.
Ania, Jerusalema se anni iti an rietminthâr sikin lei modôm mak ngeia.
54 Da almajiransa, Yaƙub da Yohanna suka ga haka, sai suka yi tambaya suka ce, “Ubangiji, kana so mu kira wuta ta sauka daga sama ta hallaka su?”
Hanchu, ruoisi Jacob le John'n an rietin chu a kôma, “Pumapa, anni ngei minmangna rangin Elijah angin invân renga mei koisumna rangin mini nuom mo?” an tia.
55 Amma Yesu ya juya, ya kwaɓe su.
Jisua an tieng ânheia, a ngo ngeia.
56 Sai shi da almajiransa suka tafi wani ƙauye.
Male Jisua le a ruoisingei chu khuo danga an se zoi.
57 Suna kan tafiya a hanya, sai wani mutum ya ce masa, “Zan bi ka, duk inda za ka.”
Hanchu, lampuia an lôn lâiin, mi inkhatin Jisua kôma, “Na sêna muntina nang jûi ki tih” a tia.
58 Yesu ya ce, “Yanyawa suna da ramummuka, tsuntsayen sararin sama suna da sheƙuna, amma Ɗan Mutum ba shi da wurin da zai sa kansa.”
Jisua'n a kôma, “Sialngei'n kuo an dôna, vangeiin rubu an dôna, ania, Miriem Nâipasal chu a lu minngamna rang luo mun dôn mak” a tipea.
59 Ya kuma ce wa wani mutum, “Ka bi ni.” Amma mutumin ya amsa ya ce, “Ubangiji, bari in je in binne mahaifina tukuna.”
Hanchu midang kôma, “Ni jûi roh” a tipea. Ania ha mi han, “Pumapa, sêng ka ta, ka pa la phûm bak ki tih,” a tia.
60 Yesu ya ce masa, “Ka bar matattu su binne matattunsu, amma kai, ka je ka yi shelar mulkin Allah.”
Jisua'n a kôma, “A thi ngeiin an mithi champui ngei phûm rese ngei, nang chu sênla, Pathien Rêngram thurchi va misîr roh” a tia.
61 Har wa yau, wani ya ce, “Zan bi ka, Ubangiji, amma ka bar ni in je in yi bankwana da iyalina tukuna.”
Mi dangin a kôma, “Pumapa, nang jûi ki tih, ania, ki inmingei chong hoiin ni manthân bak roh” a tia.
62 Yesu ya amsa ya ce, “Babu wani da yakan sa hannunsa a garman shanu, sa’an nan ya waiwaya baya, da ya isa ya shiga hidima a cikin mulkin Allah ba.”
Hanchu Jisua'n a kôma, “Tutu, âl kaina taka kut bânga, nûk tienga en chu, Pathien Rêngrama ranga mi nithei mak” a tipea.

< Luka 9 >