< Luka 9 >
1 Bayan da Yesu ya tara Sha Biyun wuri ɗaya, sai ya ba su iko da izini na fitar da dukan aljanu, da na warkar da cututtuka.
Jésus ayant assemblé les Douze, leur donna puissance et autorité pour chasser tous les démons et pour guérir toutes les maladies;
2 Ya kuma aike su, su yi wa’azin mulkin Allah, su kuma warkar da marasa lafiya.
puis il les envoya prêcher le royaume de Dieu et guérir les malades.
3 Ya ce musu, “Kada ku ɗauki kome don tafiyar, wato, ba sanda, ba jaka, ba burodi, ba kuɗi, ba riga na biyu.
Il leur dit: «Ne prenez rien pour la route, ni bâton, ni sac, ni pain, ni argent, ni deux tuniques.
4 Duk gidan da kuka sauka, ku zauna nan sai kun bar garin.
Dans quelque maison que vous entriez, restez-y, et que ce soit de là que vous partiez.
5 In mutane ba su karɓe ku ba, sa’ad da kun bar garinsu, ku karkaɗe ƙurar ƙafafunku don shaida a kansu.”
Quant à tous ceux qui ne vous recevront pas, sortez de leur ville, et secouez la poussière de vos pieds en témoignage contre eux.»
6 Sai suka tashi suka shiga ƙauye zuwa ƙauye suna wa’azin bishara, suna warkar da marasa lafiya a ko’ina.
Les disciples étant partis, allèrent de village en village, annonçant la bonne nouvelle et faisant partout des guérisons.
7 Yanzu fa, Hiridus mai sarauta ya ji labarin dukan abubuwan da suke faruwa. Sai ya rikice, don waɗansu mutane suna cewa, Yohanna Mai Baftisma ne ya tashi daga matattu,
Cependant Hérode, le tétrarque entendit parler de tout ce qui se passait, et il ne savait que penser, parce que les uns disaient que Jean était ressuscité des morts;
8 waɗansu kuma suna cewa, annabi Iliya ne ya sāke bayyana. Waɗansu kuma har wa yau, suna cewa, ɗaya daga cikin annabawa na dā ne, ya tashi.
les autres, qu'Elie était apparu; d'autres enfin, qu'un des anciens prophètes était ressuscité.
9 Amma Hiridus ya ce, “Yohanna dai na yanke kansa, amma wanne mutum ne nake jin labarin abubuwan nan a kansa?” Sai ya yi ƙoƙari ya ga Yesu.
Mais Hérode dit: «Quant à Jean, moi, je l'ai fait décapiter; qui est donc cet homme, dont j'entends dire des choses si extraordinaires?» Et il désirait le voir.
10 Da manzannin suka dawo, sai suka faɗa wa Yesu abin da suka yi. Sai ya ɗauke su, suka keɓe kansu su kaɗai, zuwa wani gari da ake kira Betsaida.
Les apôtres, étant de retour, racontèrent à Jésus tout ce qu'ils avaient fait; et Jésus les prenant avec lui, se retira à l'écart, vers une ville nommée Bethsaïde.
11 Amma taron mutane suka ji labari, sai suka bi shi. Ya marabce su, kuma ya yi musu magana a kan mulkin Allah, ya kuma warkar da masu bukatar warkarwa.
Mais les foules, en ayant eu connaissance, l'y suivirent: Jésus les accueillit, leur parla du royaume de Dieu, et guérit tous ceux qui avaient besoin d'être guéris.
12 Da rana ta kusa fāɗuwa, sai Sha Biyun suka zo wurinsa, suka ce, “Ka sallami taron domin su shiga ƙauyuka na kewaye, su nemi abin da za su ci, da wurin kwana, don inda muke, ba kowa.”
Comme le jour commençait à baisser, les Douze vinrent lui dire: «Renvoie cette foule de gens, afin qu'ils aillent loger dans les villages d'alentour et dans les campagnes, et qu'ils trouvent de quoi manger, car ici nous sommes dans un lieu désert.»
13 Yesu ya ce, “Ku, ku ba su wani abu su ci.” Sai suka ce masa, “Muna da burodi biyar da kifi biyu kaɗai. Sai dai, in mun je mu sayi abinci domin dukan wannan taron.”
Mais Jésus leur dit: «Donnez-leur, vous-mêmes, à manger.» Ils répondirent: «Nous n'avons que cinq pains et deux poissons... à moins que nous n'allions nous-mêmes acheter des vivres pour tout ce peuple.»
14 Maza kaɗai sun kai kusan dubu biyar. Amma ya ce wa almajiransa, “Ku sa su su zauna a ƙungiya hamsin-hamsin.”
En effet, il y avait environ cinq mille hommes. Jésus dit à ses disciples: «Faites-les asseoir par groupes de cinquante.»
15 Haka almajiran suka yi, kowa kuwa ya zauna.
Ils exécutèrent cet ordre; ils les firent tous asseoir.
16 Sai Yesu ya ɗauki burodin biyar da kifin biyun, ya ɗaga kansa sama, ya yi godiya, ya kuma kakkarya su. Ya ba wa almajiransa, domin su rarraba wa mutanen.
Alors Jésus prit les cinq pains et les deux poissons, et, levant les yeux au ciel, il les bénit, les rompit, et les donna aux disciples pour les distribuer à la foule.
17 Duka kuwa suka ci suka ƙoshi. Almajiran suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna goma sha biyu.
Tous mangèrent et furent rassasiés; et l'on emporta ce qu'ils avaient eu de trop, douze corbeilles de morceaux.
18 Wata rana sa’ad da Yesu yana addu’a a ɓoye, almajiransa kuma suna tare da shi, sai ya tambaye, su ya ce, “Wa, taron mutane ke ce da ni?”
Un jour que Jésus s'était retiré dans un lieu solitaire, pour prier, ses disciples vinrent le rejoindre, et il leur adressa cette question: «Qui dit-on, dans le peuple, que je suis?»
19 Suka amsa, suka ce, “Waɗansu suna cewa, Yohanna Mai Baftisma, waɗansu kuma annabi Iliya, har wa yau waɗansu suna cewa, kai ɗaya daga cikin annabawan da ne, da ya tashi da rai.”
Ils lui répondirent: «On dit que tu es Jean-Baptiste; d'autres disent que tu es Elie; d'autres, qu'un des anciens prophètes est ressuscité.»
20 “Amma ku fa, wa, kuke ce da ni?” Bitrus ya amsa ya ce, “Kiristi na Allah.”
— «Et vous, leur dit-il, qui dites-vous que je suis?» Pierre répondit: «Tu es l'Oint de Dieu.»
21 Yesu ya gargaɗe su da ƙarfi, kada su gaya wa kowa wannan magana.
Jésus leur recommanda sévèrement de ne le dire à personne,
22 Ya sāke cewa, “Dole ne Ɗan mutum ya sha wahaloli da yawa, dattawa, da manyan firistoci, da malaman dokoki kuma su ƙi shi, kuma dole a kashe shi, a rana ta uku kuma a tā da shi da rai.”
et il ajouta: «Il faut que le Fils de l'homme souffre beaucoup, qu'il soit rejeté par les anciens, les principaux sacrificateurs et les scribes, qu'il soit mis à mort, et qu'il ressuscite le troisième jour.»
23 Sai ya ce wa dukansu, “In wani zai bi ni, dole yă mūsanta kansa, ya ɗauki gicciyensa kowace rana, ya bi ni.
Puis s’adressant à tout le monde, il dit: «Si quelqu'un veut venir après moi, qu'il renonce à lui-même, qu'il se charge chaque jour de sa croix, et qu'il me suive.
24 Gama duk mai son ceton ransa zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa saboda ni zai same shi.
Car celui qui voudra sauver sa vie, la perdra; mais celui qui aura perdu sa vie à cause de moi, la sauvera.
25 Ina amfani, in mutum ya ribato duniya duka, amma ya rasa ransa, ko kuma ya yi hasarar ransa.
A quoi sert-il à un homme de gagner le monde entier, s'il se perd ou se ruine lui-même?
26 Duk wanda yake jin kunyana da na kalmomina, Ɗan Mutum ma zai ji kunyarsa sa’ad da zai zo a cikin ɗaukakarsa, da ɗaukakar Uban, da kuma ta tsarkaka mala’ikun.
En effet, si quelqu'un a honte de moi et de mes paroles, le Fils de l'homme aura honte de lui, quand il viendra dans sa gloire, dans celle de son Père et dans celle des saints anges.
27 “Gaskiya nake gaya muku, waɗansu da suke tsattsaye a nan ba za su ga mutuwa ba, sai sun ga mulkin Allah.”
Je vous le dis, certainement quelques-uns de ceux qui sont ici présents, ne goûteront point la mort, qu'ils n'aient vu le royaume de Dieu.»
28 Bayan kamar kwana takwas da yin wannan magana, sai Yesu ya ɗauki Bitrus, da Yohanna, da kuma Yaƙub, suka hau kan dutse tare don yin addu’a.
Environ huit jours après ce discours, Jésus prit avec lui Pierre, Jean et Jacques, et monta sur la montagne pour prier.
29 Yana cikin addu’a, sai kamannin fuskarsa ta sāke, tufafinsa kuma suka zama da haske kamar hasken walƙiya.
Pendant qu'il priait, son visage parut tout autre et ses vêtements devinrent éblouissants de blancheur.
30 Sai ga mutum biyu, Musa da Iliya, suka bayyana cikin kyakkyawar daraja, suna magana da Yesu.
Tout à coup parurent, entourés de gloire, deux hommes qui s'entretenaient avec lui: c'était Moïse et Élie;
31 Suka yi zance a kan tashinsa, wanda shi ya kusan ya kawo ga cikarsa a Urushalima.
ils parlaient de son départ qui devait s'accomplir à Jérusalem.
32 Barci kuwa ya kama Bitrus da abokan tafiyarsa sosai. Da idanunsu suka warware, sai suka ga ɗaukakarsa da kuma mutum biyun tsaye tare da shi.
Pierre et ses compagnons étaient accablés de sommeil; mais s’étant tenus éveillés, ils virent sa gloire et les deux hommes qui étaient avec lui;
33 Da mutanen na barin Yesu, sai Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, ya yi kyau da muke nan. Bari mu kafa bukkoki guda uku, wato, ɗaya dominka, ɗaya domin Musa, ɗaya kuma domin Iliya.” (Bai ma san abin da yake faɗi ba.)
et au moment où Moïse et Élie se séparaient de lui, Pierre dit à Jésus: «Maître, il est bon que nous soyons ici; dressons trois tentes, une pour toi, une pour Moïse, et une pour Elie»: il ne savait pas ce qu'il disait.
34 Yayinda yake cikin magana, sai wani girgije ya bayyana ya rufe su, sai suka ji tsoro, yayinda suke shiga cikin girgijen.
Comme il parlait ainsi, une nuée vint, qui les enveloppa, et en les voyant entrer dans la nuée, les disciples furent saisis de frayeur.
35 Wata murya ta fito daga cikin girgijen, tana cewa, “Wannan Ɗana ne, zaɓaɓɓena, ku saurare shi.”
Il sortit de la nuée une voix qui dit: «Celui-ci est mon Fils élu; écoutez-le; »
36 Da muryar ta gama magana, sai suka tarar Yesu shi kaɗai ne. Almajiran kuwa suka riƙe wannan al’amari a zukatansu. A lokacin nan, ba su gaya wa kowa abin da suka gani ba.
et après que la voix se fut fait entendre, Jésus se trouva seul. Les disciples gardèrent le silence sur ce qui s’était passé, et ne rapportèrent pour lors à personne rien de ce qu'ils avaient vu.
37 Kashegari, sa’ad da Yesu tare da almajiran nan uku suka sauka daga kan dutsen, sai taro mai yawa ya haɗu da shi.
Le lendemain, lorsqu'ils furent descendus de la montagne, une foule considérable se porta à la rencontre de Jésus,
38 Sai wani mutum daga cikin taron ya yi kira da ƙarfi ya ce, “Malam, ina roƙonka, ka dubi ɗan nan nawa, gama shi ne kaɗai nake da shi.
et un homme s'écria du milieu de la foule: «Maître, je t'en prie, jette un regard sur mon fils, car je n'ai que cet enfant:
39 Wani ruhu yakan kama shi, sai ya yi ihu farar ɗaya. Yakan sa shi farfaɗiya, har bakinsa ya yi kumfa. Da ƙyar yake barinsa, yana kuwa kan hallakar da shi.
un esprit le saisit, et soudain lui arrache des cris; puis il le jette dans des convulsions où il écume, et il le quitte à grand'peine en le brisant encore.
40 Na roƙi almajiranka su fitar da shi, amma ba su iya ba.”
J'ai prié tes disciples de le chasser, et ils ne l'ont pu.»
41 Yesu ya amsa ya ce, “Ya karkataccen zamani marar bangaskiya, har yaushe ne zan kasance tare da ku, ina kuma haƙuri da ku? Kawo yaronka nan.”
Jésus répondit: «Race incrédule et perverse, jusqu'à quand serai-je avec vous, et vous supporterai-je?... Amène ici ton fils.»
42 Yaron yana kan zuwa ke nan, sai aljanin ya buga shi ƙasa, cikin farfaɗiya. Amma Yesu ya kwaɓe mugun ruhun, ya warkar da yaron, sai ya miƙa shi ga mahaifinsa.
Au moment où l'enfant s'approchait, le démon le jeta par terre, dans des convulsions; mais Jésus tança l'esprit impur, guérit l'enfant, et le rendit à son père.
43 Duk suka yi mamakin girman Allah. Yayinda kowa yana cikin mamakin dukan abubuwan da Yesu ya yi, sai ya ce wa almajiransa,
Tous les assistants étaient frappés de la grandeur de Dieu. Tandis que tout le monde était dans l'admiration de tout ce que Jésus faisait, il dit à ses disciples:
44 “Ku kasa kunne da kyau ga abin da zan faɗa muku. Za a bashe Ɗan Mutum ga hannun mutane.”
«Pour vous, mettez-vous bien dans l'esprit ce que je vais vous dire: c'est que le Fils de l'homme doit être livré entre les mains des hommes.»
45 Amma ba su fahimci abin da yake nufi da wannan magana ba. Ba su gane ba, don an ɓoye musu shi. Su kuwa sun ji tsoro su tambaye shi.
Mais les disciples ne comprenaient pas cette parole; elle était voilée pour eux, afin qu'ils n'en sentissent point la portée; et ils craignaient de l'interroger là -dessus.
46 Wata gardama ta tashi a tsakanin almajiran, a kan ko wane ne a cikinsu zai zama mafi girma
Une pensée s'éleva dans leur esprit: ils se demandaient lequel d'entre eux serait le plus grand.
47 Da yake Yesu ya san tunaninsu, sai ya ɗauki wani ƙaramin yaro, ya sa ya tsaya kusa da shi.
Jésus voyant la pensée de leur coeur, prit un petit enfant, le plaça auprès de lui,
48 Sai ya ce musu, “Duk wanda ya karɓi wannan ƙaramin yaron a cikin sunana, ni ya karɓa, kuma duk wanda ya karɓe ni, ya karɓi wanda ya aiko ni ne. Gama mafi ƙanƙanta duka a cikinku, shi ne kuma mafi girma.”
et leur dit: «Celui qui reçoit ce petit enfant en mon nom, me reçoit; et celui qui me reçoit, reçoit celui qui m'a envoyé; car celui d'entre vous tous qui est le plus petit, c'est celui-là qui est grand.»
49 Sai Yohanna ya ce, “Ubangiji, mun ga wani mutum yana fitar da aljanu a cikin sunanka, muka yi ƙoƙarin hana shi, don shi ba ɗaya ba ne daga cikinmu.”
Jean, prenant la parole, lui dit: «Maître, nous avons vu un homme qui chassait des démons en ton nom, et nous l'en avons empêché, parce qu'il ne va pas avec nous.»
50 Yesu ya ce, “Kada ku hana shi, gama duk wanda ba ya gāba da ku, naku ne.”
Jésus lui dit: «Ne l'en empêchez point: celui qui n'est pas contre vous est pour vous.»
51 Da lokaci ya yi kusa da za a ɗauki Yesu zuwa sama, sai ya ɗaura niyyar tafiya Urushalima.
Quand le temps où Jésus devait être enlevé du monde fut venu, il prit la résolution de s'acheminer à Jérusalem.
52 Sai ya aiki’yan saƙo, su yi gaba. Su kuwa, suka shiga cikin wani ƙauyen Samariyawa, don su shirya masa abubuwa.
Il se fit précéder par des messagers. Ceux-ci, s'en étant allés, entrèrent dans une ville des Samaritains pour lui préparer un logement;
53 Amma mutanen ƙauyen ba su karɓe shi ba, don yana kan hanyar zuwa Urushalima ne.
mais on ne le reçut point, parce qu'il se rendait à Jérusalem.
54 Da almajiransa, Yaƙub da Yohanna suka ga haka, sai suka yi tambaya suka ce, “Ubangiji, kana so mu kira wuta ta sauka daga sama ta hallaka su?”
Ses disciples, Jacques et Jean, témoins de ce refus, dirent: «Seigneur, veux-tu qu'à l'exemple d'Élie, nous commandions que le feu descende du ciel et consume ces gens-là?»
55 Amma Yesu ya juya, ya kwaɓe su.
Mais Jésus s’étant retourné, les réprimanda, et leur dit: «Vous ne savez de quel esprit vous êtes animés.»
56 Sai shi da almajiransa suka tafi wani ƙauye.
Et ils gagnèrent un autre village.
57 Suna kan tafiya a hanya, sai wani mutum ya ce masa, “Zan bi ka, duk inda za ka.”
Comme ils s'y rendaient, un homme lui dit en chemin: «Seigneur, je te suivrai partout où tu iras.»
58 Yesu ya ce, “Yanyawa suna da ramummuka, tsuntsayen sararin sama suna da sheƙuna, amma Ɗan Mutum ba shi da wurin da zai sa kansa.”
Et Jésus lui dit: «Les renards ont des tanières, et les oiseaux du ciel, des abris; mais le Fils de l'homme n'a pas un lieu pour reposer sa tête.»
59 Ya kuma ce wa wani mutum, “Ka bi ni.” Amma mutumin ya amsa ya ce, “Ubangiji, bari in je in binne mahaifina tukuna.”
Il dit à un autre: «Suis-moi.» Celui-ci lui dit: «Seigneur, permets-moi d'aller auparavant ensevelir mon père.»
60 Yesu ya ce masa, “Ka bar matattu su binne matattunsu, amma kai, ka je ka yi shelar mulkin Allah.”
Mais il lui repartit: «Laisse les morts ensevelir leurs morts; pour toi, va annoncer le royaume de Dieu.»
61 Har wa yau, wani ya ce, “Zan bi ka, Ubangiji, amma ka bar ni in je in yi bankwana da iyalina tukuna.”
Un autre lui dit aussi: «Je te suivrai, Seigneur, mais permets-moi d'aller auparavant faire mes adieux à ma famille.»
62 Yesu ya amsa ya ce, “Babu wani da yakan sa hannunsa a garman shanu, sa’an nan ya waiwaya baya, da ya isa ya shiga hidima a cikin mulkin Allah ba.”
Jésus lui dit: «Quiconque met la main à la charrue et regarde en arrière, n'est pas propre au royaume de Dieu.»