< Luka 9 >

1 Bayan da Yesu ya tara Sha Biyun wuri ɗaya, sai ya ba su iko da izini na fitar da dukan aljanu, da na warkar da cututtuka.
And He called his twelve disciples together, and gave them power and authority over all demons, and to cure diseases:
2 Ya kuma aike su, su yi wa’azin mulkin Allah, su kuma warkar da marasa lafiya.
and He sent them forth to preach the kingdom of God, and to heal the sick.
3 Ya ce musu, “Kada ku ɗauki kome don tafiyar, wato, ba sanda, ba jaka, ba burodi, ba kuɗi, ba riga na biyu.
And He said unto them, Take nothing for your journey, neither staves, nor bag, nor bread, nor money; nor two coats a piece.
4 Duk gidan da kuka sauka, ku zauna nan sai kun bar garin.
And into whatever house ye enter, continue there, till ye leave that place.
5 In mutane ba su karɓe ku ba, sa’ad da kun bar garinsu, ku karkaɗe ƙurar ƙafafunku don shaida a kansu.”
And whosoever will not receive you, when ye depart from that city, shake off the very dust from your feet, for a testimony against them.
6 Sai suka tashi suka shiga ƙauye zuwa ƙauye suna wa’azin bishara, suna warkar da marasa lafiya a ko’ina.
And they went from town to town, preaching the gospel and healing every where.
7 Yanzu fa, Hiridus mai sarauta ya ji labarin dukan abubuwan da suke faruwa. Sai ya rikice, don waɗansu mutane suna cewa, Yohanna Mai Baftisma ne ya tashi daga matattu,
Now Herod the tetrarch heard of all the things that were done by Him; and was perplexed, because it was said by some that John was risen from the dead;
8 waɗansu kuma suna cewa, annabi Iliya ne ya sāke bayyana. Waɗansu kuma har wa yau, suna cewa, ɗaya daga cikin annabawa na dā ne, ya tashi.
and by some that Elias had appeared; and by others, that one of the ancient prophets was risen again.
9 Amma Hiridus ya ce, “Yohanna dai na yanke kansa, amma wanne mutum ne nake jin labarin abubuwan nan a kansa?” Sai ya yi ƙoƙari ya ga Yesu.
And Herod said, John have I beheaded: but who is this, of whom I hear such things? and he wanted to see Him.
10 Da manzannin suka dawo, sai suka faɗa wa Yesu abin da suka yi. Sai ya ɗauke su, suka keɓe kansu su kaɗai, zuwa wani gari da ake kira Betsaida.
And the apostles; when they were returned, told Him all that they had done: and He took them and retired privately into a desert place belonging to the city Bethsaida.
11 Amma taron mutane suka ji labari, sai suka bi shi. Ya marabce su, kuma ya yi musu magana a kan mulkin Allah, ya kuma warkar da masu bukatar warkarwa.
But when the people knew it they followed Him; and He received them, and spake to them concerning the kingdom of God, and healed those that had need of a cure.
12 Da rana ta kusa fāɗuwa, sai Sha Biyun suka zo wurinsa, suka ce, “Ka sallami taron domin su shiga ƙauyuka na kewaye, su nemi abin da za su ci, da wurin kwana, don inda muke, ba kowa.”
And when the day began to decline, the twelve came and said to Him, Dismiss the people, that they may go into the villages and country-places round about, and bait, and get food: for here we are in a desert place.
13 Yesu ya ce, “Ku, ku ba su wani abu su ci.” Sai suka ce masa, “Muna da burodi biyar da kifi biyu kaɗai. Sai dai, in mun je mu sayi abinci domin dukan wannan taron.”
But He said unto them, Do ye give them food. And they said, We have but five loaves and two fishes: unless we should go and buy provisions for all this people:
14 Maza kaɗai sun kai kusan dubu biyar. Amma ya ce wa almajiransa, “Ku sa su su zauna a ƙungiya hamsin-hamsin.”
for they were about five thousand men. And He said to his disciples, Make them sit down in companies by fifty.
15 Haka almajiran suka yi, kowa kuwa ya zauna.
And they did so, and caused them all to sit down.
16 Sai Yesu ya ɗauki burodin biyar da kifin biyun, ya ɗaga kansa sama, ya yi godiya, ya kuma kakkarya su. Ya ba wa almajiransa, domin su rarraba wa mutanen.
And He took the five loaves and the two fishes, and looking up to heaven He blessed them; and brake and gave them to the disciples to set before the multitude.
17 Duka kuwa suka ci suka ƙoshi. Almajiran suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna goma sha biyu.
And they did eat, and were all satisfied: and there was taken up what remained even of fragments twelve baskets.
18 Wata rana sa’ad da Yesu yana addu’a a ɓoye, almajiransa kuma suna tare da shi, sai ya tambaye, su ya ce, “Wa, taron mutane ke ce da ni?”
And it came to pass, as He was praying in private, his disciples were with Him: and He asked them saying, Whom say the people that I am?
19 Suka amsa, suka ce, “Waɗansu suna cewa, Yohanna Mai Baftisma, waɗansu kuma annabi Iliya, har wa yau waɗansu suna cewa, kai ɗaya daga cikin annabawan da ne, da ya tashi da rai.”
They answering said, John the baptist: but others say Elias: and others, that some ancient prophet is risen again.
20 “Amma ku fa, wa, kuke ce da ni?” Bitrus ya amsa ya ce, “Kiristi na Allah.”
And He said unto them, But whom say ye that I am? And Peter answered and said, The Christ the Son of God.
21 Yesu ya gargaɗe su da ƙarfi, kada su gaya wa kowa wannan magana.
But He strictly charged and commanded them to tell this to no one,
22 Ya sāke cewa, “Dole ne Ɗan mutum ya sha wahaloli da yawa, dattawa, da manyan firistoci, da malaman dokoki kuma su ƙi shi, kuma dole a kashe shi, a rana ta uku kuma a tā da shi da rai.”
saying, the Son of man must suffer many things, and be rejected by the elders, and chief priests, and scribes, and be put to death, and be raised again the third day.
23 Sai ya ce wa dukansu, “In wani zai bi ni, dole yă mūsanta kansa, ya ɗauki gicciyensa kowace rana, ya bi ni.
And He said unto them all, if any one is willing to come after me, let him deny himself, and take up his cross daily, and follow me:
24 Gama duk mai son ceton ransa zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa saboda ni zai same shi.
for he that would save his life shall lose it, but he that would lose his life for my sake shall save it.
25 Ina amfani, in mutum ya ribato duniya duka, amma ya rasa ransa, ko kuma ya yi hasarar ransa.
For what is a man profited, if he gain the whole world, and lose himself, or be destroyed?
26 Duk wanda yake jin kunyana da na kalmomina, Ɗan Mutum ma zai ji kunyarsa sa’ad da zai zo a cikin ɗaukakarsa, da ɗaukakar Uban, da kuma ta tsarkaka mala’ikun.
For whosoever shall be ashamed of me and of my words, of him shall the Son of man be ashamed, when He comes in his own glory, and in his Father's, and of the holy angels.
27 “Gaskiya nake gaya muku, waɗansu da suke tsattsaye a nan ba za su ga mutuwa ba, sai sun ga mulkin Allah.”
And I assure you, there be some of those who stand here, that shall not taste of death, till they have seen the kingdom of God.
28 Bayan kamar kwana takwas da yin wannan magana, sai Yesu ya ɗauki Bitrus, da Yohanna, da kuma Yaƙub, suka hau kan dutse tare don yin addu’a.
About eight days after these discourses, He took Peter, and John, and James, and went up to a mountain to pray.
29 Yana cikin addu’a, sai kamannin fuskarsa ta sāke, tufafinsa kuma suka zama da haske kamar hasken walƙiya.
And as He was praying the form of his countenance was altered, and his raiment white and glistering:
30 Sai ga mutum biyu, Musa da Iliya, suka bayyana cikin kyakkyawar daraja, suna magana da Yesu.
and behold two men talked with Him, which were Moses and Elias;
31 Suka yi zance a kan tashinsa, wanda shi ya kusan ya kawo ga cikarsa a Urushalima.
who appeared in glory, and spake of his exit, which He was to make at Jerusalem.
32 Barci kuwa ya kama Bitrus da abokan tafiyarsa sosai. Da idanunsu suka warware, sai suka ga ɗaukakarsa da kuma mutum biyun tsaye tare da shi.
Now Peter and they that were with Him were heavy with sleep; but being awakened they saw his glory, and the two men that stood with Him.
33 Da mutanen na barin Yesu, sai Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, ya yi kyau da muke nan. Bari mu kafa bukkoki guda uku, wato, ɗaya dominka, ɗaya domin Musa, ɗaya kuma domin Iliya.” (Bai ma san abin da yake faɗi ba.)
And as they were departing from Him, Peter said unto Jesus, Master, it is good for us to be here, let us make three tabernacles, one for Thee, and one for Moses, and one for Elias: not knowing what he said.
34 Yayinda yake cikin magana, sai wani girgije ya bayyana ya rufe su, sai suka ji tsoro, yayinda suke shiga cikin girgijen.
And as he was saying this, there came a cloud and overshadowed them; and they were afraid, when they went up into the cloud and disappeared.
35 Wata murya ta fito daga cikin girgijen, tana cewa, “Wannan Ɗana ne, zaɓaɓɓena, ku saurare shi.”
And there came a voice out of the cloud saying, This is my beloved Son, hear ye Him.
36 Da muryar ta gama magana, sai suka tarar Yesu shi kaɗai ne. Almajiran kuwa suka riƙe wannan al’amari a zukatansu. A lokacin nan, ba su gaya wa kowa abin da suka gani ba.
And when the voice was uttered, Jesus was found alone. And they kept it to themselves, and told no one at that time any of the things which they had seen.
37 Kashegari, sa’ad da Yesu tare da almajiran nan uku suka sauka daga kan dutsen, sai taro mai yawa ya haɗu da shi.
And the next day, when they came down from the mountain, a great multitude met Him:
38 Sai wani mutum daga cikin taron ya yi kira da ƙarfi ya ce, “Malam, ina roƙonka, ka dubi ɗan nan nawa, gama shi ne kaɗai nake da shi.
and one of the people cried out, saying, Master, I beseech thee look upon my son, for he is my only child;
39 Wani ruhu yakan kama shi, sai ya yi ihu farar ɗaya. Yakan sa shi farfaɗiya, har bakinsa ya yi kumfa. Da ƙyar yake barinsa, yana kuwa kan hallakar da shi.
and lo, a spirit seizeth him, and all on a sudden he screameth, and it convulses him with foaming; and bruising him, with much ado departs from him.
40 Na roƙi almajiranka su fitar da shi, amma ba su iya ba.”
And I prayed thy disciples to cast him out, and they could not.
41 Yesu ya amsa ya ce, “Ya karkataccen zamani marar bangaskiya, har yaushe ne zan kasance tare da ku, ina kuma haƙuri da ku? Kawo yaronka nan.”
Then Jesus answered and said, O unbelieving and perverse generation, how long shall I be with you, and bear with you? Bring thy son hither.
42 Yaron yana kan zuwa ke nan, sai aljanin ya buga shi ƙasa, cikin farfaɗiya. Amma Yesu ya kwaɓe mugun ruhun, ya warkar da yaron, sai ya miƙa shi ga mahaifinsa.
And as he was coming along, the devil bruised and convulsed him: but Jesus rebuked the impure spirit, and healed the child, and delivered him to his father.
43 Duk suka yi mamakin girman Allah. Yayinda kowa yana cikin mamakin dukan abubuwan da Yesu ya yi, sai ya ce wa almajiransa,
And they were all amazed at the mighty power of God: but while they were all wondering at the things which Jesus did, He said to his disciples,
44 “Ku kasa kunne da kyau ga abin da zan faɗa muku. Za a bashe Ɗan Mutum ga hannun mutane.”
Receive these words into your ears; for the Son of man is going to be delivered into the hands of men.
45 Amma ba su fahimci abin da yake nufi da wannan magana ba. Ba su gane ba, don an ɓoye musu shi. Su kuwa sun ji tsoro su tambaye shi.
But they understood not this saying, and it was hid from them, so that they perceived it not, and they were afraid to ask Him concerning it.
46 Wata gardama ta tashi a tsakanin almajiran, a kan ko wane ne a cikinsu zai zama mafi girma
Then a dispute rose among them, which of them should be greatest.
47 Da yake Yesu ya san tunaninsu, sai ya ɗauki wani ƙaramin yaro, ya sa ya tsaya kusa da shi.
And Jesus knowing the thought of their heart, took a child and set him by Him, and said unto them,
48 Sai ya ce musu, “Duk wanda ya karɓi wannan ƙaramin yaron a cikin sunana, ni ya karɓa, kuma duk wanda ya karɓe ni, ya karɓi wanda ya aiko ni ne. Gama mafi ƙanƙanta duka a cikinku, shi ne kuma mafi girma.”
Whosoever shall receive this little child for my sake, receiveth me: and he that receiveth me, receiveth Him that sent me. For he that is lest among you all, shall be great.
49 Sai Yohanna ya ce, “Ubangiji, mun ga wani mutum yana fitar da aljanu a cikin sunanka, muka yi ƙoƙarin hana shi, don shi ba ɗaya ba ne daga cikinmu.”
And John answered and said, Master, we saw one casting out demons in thy name, and we forbad him, because he followeth not thee with us.
50 Yesu ya ce, “Kada ku hana shi, gama duk wanda ba ya gāba da ku, naku ne.”
And Jesus said unto him, Forbid him not; for he, that is not against us, is for us.
51 Da lokaci ya yi kusa da za a ɗauki Yesu zuwa sama, sai ya ɗaura niyyar tafiya Urushalima.
And it came to pass, as the days were almost fulfilled of his being received up again into heaven, that He set his face to go to Jerusalem,
52 Sai ya aiki’yan saƙo, su yi gaba. Su kuwa, suka shiga cikin wani ƙauyen Samariyawa, don su shirya masa abubuwa.
and sent messengers before Him: who went into a village of the Samaritans to get a place ready for Him.
53 Amma mutanen ƙauyen ba su karɓe shi ba, don yana kan hanyar zuwa Urushalima ne.
But they would not entertain Him, because his face was towards Jerusalem.
54 Da almajiransa, Yaƙub da Yohanna suka ga haka, sai suka yi tambaya suka ce, “Ubangiji, kana so mu kira wuta ta sauka daga sama ta hallaka su?”
And when his disciples James and John saw it, they said, Lord, wilt thou that we command fire to come down from heaven and consume them, as Elias did?
55 Amma Yesu ya juya, ya kwaɓe su.
But He turned and rebuked them, and said, Ye know not what spirit ye are of:
56 Sai shi da almajiransa suka tafi wani ƙauye.
for the Son of man came not to destroy mens lives, but to save them. And they went to another village.
57 Suna kan tafiya a hanya, sai wani mutum ya ce masa, “Zan bi ka, duk inda za ka.”
And as they were going by the way, there was one said to Him, Lord, I will follow thee whithersoever thou goest:
58 Yesu ya ce, “Yanyawa suna da ramummuka, tsuntsayen sararin sama suna da sheƙuna, amma Ɗan Mutum ba shi da wurin da zai sa kansa.”
and Jesus answered him, The foxes have holes, and the fowls of heaven their nests, but the Son of man hath not where to lay his head.
59 Ya kuma ce wa wani mutum, “Ka bi ni.” Amma mutumin ya amsa ya ce, “Ubangiji, bari in je in binne mahaifina tukuna.”
And He said to another, Follow me: but he said, Lord, permit me to go first and bury my father:
60 Yesu ya ce masa, “Ka bar matattu su binne matattunsu, amma kai, ka je ka yi shelar mulkin Allah.”
but Jesus said unto him, Leave the dead to bury their dead; but go thou and preach the kingdom of God.
61 Har wa yau, wani ya ce, “Zan bi ka, Ubangiji, amma ka bar ni in je in yi bankwana da iyalina tukuna.”
And another also said, Lord, I will follow thee, but allow me first to go and take my leave of my family.
62 Yesu ya amsa ya ce, “Babu wani da yakan sa hannunsa a garman shanu, sa’an nan ya waiwaya baya, da ya isa ya shiga hidima a cikin mulkin Allah ba.”
But Jesus said unto him, No one, that hath put his hand to the plough and looketh back, is fit for the kingdom of God.

< Luka 9 >