< Luka 9 >

1 Bayan da Yesu ya tara Sha Biyun wuri ɗaya, sai ya ba su iko da izini na fitar da dukan aljanu, da na warkar da cututtuka.
Then he called the Twelve together, and gave them power and authority over all demons, and to heal;
2 Ya kuma aike su, su yi wa’azin mulkin Allah, su kuma warkar da marasa lafiya.
and sent them out to preach the kingdom of God, and heal the sick.
3 Ya ce musu, “Kada ku ɗauki kome don tafiyar, wato, ba sanda, ba jaka, ba burodi, ba kuɗi, ba riga na biyu.
And he said to them. "Take nothing for your journey, neither staff, nor bag, nor bread, nor money, and do not have two tunics.
4 Duk gidan da kuka sauka, ku zauna nan sai kun bar garin.
"Into whatever house you enter, there stay, and thence depart.
5 In mutane ba su karɓe ku ba, sa’ad da kun bar garinsu, ku karkaɗe ƙurar ƙafafunku don shaida a kansu.”
"If any one will not receive you, shake off the dust from your feet as you leave this town, as a testimony against them."
6 Sai suka tashi suka shiga ƙauye zuwa ƙauye suna wa’azin bishara, suna warkar da marasa lafiya a ko’ina.
So they went forth, and walked from village to village, preaching the gospel and healing everywhere.
7 Yanzu fa, Hiridus mai sarauta ya ji labarin dukan abubuwan da suke faruwa. Sai ya rikice, don waɗansu mutane suna cewa, Yohanna Mai Baftisma ne ya tashi daga matattu,
Now Herod, the Tetrarch, heard of all that was happening; and he was perplexed because of its being said by someone that Johnwas risen from the dead;
8 waɗansu kuma suna cewa, annabi Iliya ne ya sāke bayyana. Waɗansu kuma har wa yau, suna cewa, ɗaya daga cikin annabawa na dā ne, ya tashi.
and by some that Elijah had appeared; and by others that one of the ancient prophets was risen again.
9 Amma Hiridus ya ce, “Yohanna dai na yanke kansa, amma wanne mutum ne nake jin labarin abubuwan nan a kansa?” Sai ya yi ƙoƙari ya ga Yesu.
So Herod said, "I beheaded John, but who is this of whom I am hearing such reports," And he kept seeking to see him.
10 Da manzannin suka dawo, sai suka faɗa wa Yesu abin da suka yi. Sai ya ɗauke su, suka keɓe kansu su kaɗai, zuwa wani gari da ake kira Betsaida.
On their return the apostles told him what they had done. and he took them and withdrew in private to a town called Bethsaida.
11 Amma taron mutane suka ji labari, sai suka bi shi. Ya marabce su, kuma ya yi musu magana a kan mulkin Allah, ya kuma warkar da masu bukatar warkarwa.
But when the crowd learned this they followed him. He received them kindly and spoke to them concerning the kingdom of God, and healed those who needed restored to good health.
12 Da rana ta kusa fāɗuwa, sai Sha Biyun suka zo wurinsa, suka ce, “Ka sallami taron domin su shiga ƙauyuka na kewaye, su nemi abin da za su ci, da wurin kwana, don inda muke, ba kowa.”
But now the day began to decline, and the twelve came to him and said. "Send away the crowd so that they may go into the villages and surrounding the country to lodge and buy provisions; for here we are on a solitary place."
13 Yesu ya ce, “Ku, ku ba su wani abu su ci.” Sai suka ce masa, “Muna da burodi biyar da kifi biyu kaɗai. Sai dai, in mun je mu sayi abinci domin dukan wannan taron.”
"Do you yourselves give them food," he answered. "We have nothing," they replied "Except five loaves, and a couple fish, unless you mean for us to go and buy provisions for all the crowd."
14 Maza kaɗai sun kai kusan dubu biyar. Amma ya ce wa almajiransa, “Ku sa su su zauna a ƙungiya hamsin-hamsin.”
(For there were about five thousand men.) "Make them sit down in table-companies, of about fifty each," he said to his disciples.
15 Haka almajiran suka yi, kowa kuwa ya zauna.
This they did, and made them all sit down.
16 Sai Yesu ya ɗauki burodin biyar da kifin biyun, ya ɗaga kansa sama, ya yi godiya, ya kuma kakkarya su. Ya ba wa almajiransa, domin su rarraba wa mutanen.
Then he took the five loaves and the two fish, and looking up in heaven, he blessed them, broke them in pieces, and began to giving to his disciples to apportion among the crowd.
17 Duka kuwa suka ci suka ƙoshi. Almajiran suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna goma sha biyu.
So they ate and were filled, all of them. And there was picked up that which remained over to them, of broken pieces, twelve basketfuls.
18 Wata rana sa’ad da Yesu yana addu’a a ɓoye, almajiransa kuma suna tare da shi, sai ya tambaye, su ya ce, “Wa, taron mutane ke ce da ni?”
Now it happened that while he was praying by himself, the disciples were with him, and he asked them a question. "Who do the crowd think I am?"
19 Suka amsa, suka ce, “Waɗansu suna cewa, Yohanna Mai Baftisma, waɗansu kuma annabi Iliya, har wa yau waɗansu suna cewa, kai ɗaya daga cikin annabawan da ne, da ya tashi da rai.”
"Johnthe Baptist," they answered, "But others say Elijah, and others that one of the ancient prophets is risen again."
20 “Amma ku fa, wa, kuke ce da ni?” Bitrus ya amsa ya ce, “Kiristi na Allah.”
Then he said to them, "But who do you say I am? Then Peter answered saying, "The Christ of God.’
21 Yesu ya gargaɗe su da ƙarfi, kada su gaya wa kowa wannan magana.
Then he strictly forbade them to tell this to any one;
22 Ya sāke cewa, “Dole ne Ɗan mutum ya sha wahaloli da yawa, dattawa, da manyan firistoci, da malaman dokoki kuma su ƙi shi, kuma dole a kashe shi, a rana ta uku kuma a tā da shi da rai.”
and he said, "The Son of man must suffer much, and be restricted by the elders and high priests and scribes and be put to death, and on the third day be raised again."
23 Sai ya ce wa dukansu, “In wani zai bi ni, dole yă mūsanta kansa, ya ɗauki gicciyensa kowace rana, ya bi ni.
And he said to all. "If any man wills to follow me, Let him renounce self and take up his cross daily and follow me.
24 Gama duk mai son ceton ransa zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa saboda ni zai same shi.
"For whoever wills to save his life shall lose it; and whoever loses his life for my sake shall save it.
25 Ina amfani, in mutum ya ribato duniya duka, amma ya rasa ransa, ko kuma ya yi hasarar ransa.
"For what shall it profit a man if he shall gain the whole world and lose or forfeit himself?
26 Duk wanda yake jin kunyana da na kalmomina, Ɗan Mutum ma zai ji kunyarsa sa’ad da zai zo a cikin ɗaukakarsa, da ɗaukakar Uban, da kuma ta tsarkaka mala’ikun.
"For whoever is ashamed of me and of my teachings, of him shall the Son of man be ashamed when he comes in his own and in his Father’s glory, and in that of the holy angels.
27 “Gaskiya nake gaya muku, waɗansu da suke tsattsaye a nan ba za su ga mutuwa ba, sai sun ga mulkin Allah.”
"But I tell you truly there are some of those standing here who will not taste death till they see the kingdom of God."
28 Bayan kamar kwana takwas da yin wannan magana, sai Yesu ya ɗauki Bitrus, da Yohanna, da kuma Yaƙub, suka hau kan dutse tare don yin addu’a.
About eight days after this it happened that Jesus took Peter, James, and John, and went up on the mountain to pray.
29 Yana cikin addu’a, sai kamannin fuskarsa ta sāke, tufafinsa kuma suka zama da haske kamar hasken walƙiya.
And as he was praying the appearances of his countenance became different, and his clothing became white and dazzling.
30 Sai ga mutum biyu, Musa da Iliya, suka bayyana cikin kyakkyawar daraja, suna magana da Yesu.
And suddenly there were two men talking with him, who were Moses and Elijah.
31 Suka yi zance a kan tashinsa, wanda shi ya kusan ya kawo ga cikarsa a Urushalima.
These appeared in glory and talked about his departure which he was about to accomplish at Jerusalem.
32 Barci kuwa ya kama Bitrus da abokan tafiyarsa sosai. Da idanunsu suka warware, sai suka ga ɗaukakarsa da kuma mutum biyun tsaye tare da shi.
Now Peter and those who were with him were heavy with sleep; but when they were fully awake they saw his glory, and the two men were standing beside him.
33 Da mutanen na barin Yesu, sai Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, ya yi kyau da muke nan. Bari mu kafa bukkoki guda uku, wato, ɗaya dominka, ɗaya domin Musa, ɗaya kuma domin Iliya.” (Bai ma san abin da yake faɗi ba.)
And when they were preparing to depart from him Peter said to Jesus. "Master, it is good for us to be here; and let us make three tents, one for you, one for Moses, and one for Elijah" - not knowing what he was saying.
34 Yayinda yake cikin magana, sai wani girgije ya bayyana ya rufe su, sai suka ji tsoro, yayinda suke shiga cikin girgijen.
And while he was saying this, there came a cloud and began to overshadow them; and they were awestruck as they entered into the cloud.
35 Wata murya ta fito daga cikin girgijen, tana cewa, “Wannan Ɗana ne, zaɓaɓɓena, ku saurare shi.”
And a voice came out of the cloud, saying. "This is my Son, my chosen one; listen to him."
36 Da muryar ta gama magana, sai suka tarar Yesu shi kaɗai ne. Almajiran kuwa suka riƙe wannan al’amari a zukatansu. A lokacin nan, ba su gaya wa kowa abin da suka gani ba.
When the voice ceased Jesus was found alone. And they held their peace, and told no one at that time about what they had seen.
37 Kashegari, sa’ad da Yesu tare da almajiran nan uku suka sauka daga kan dutsen, sai taro mai yawa ya haɗu da shi.
It happened the next day, when they were come down from the mountain, that a large crowd came to meet him;
38 Sai wani mutum daga cikin taron ya yi kira da ƙarfi ya ce, “Malam, ina roƙonka, ka dubi ɗan nan nawa, gama shi ne kaɗai nake da shi.
and a man called out of the crowd saying. "Teacher, I beg you to look upon my son; for he is my only boy,
39 Wani ruhu yakan kama shi, sai ya yi ihu farar ɗaya. Yakan sa shi farfaɗiya, har bakinsa ya yi kumfa. Da ƙyar yake barinsa, yana kuwa kan hallakar da shi.
"and behold a spirit seizes hold of him, and rudely he shouts out, It convulses him till he foams; indeed it will hardly leave off bruising him sorely.
40 Na roƙi almajiranka su fitar da shi, amma ba su iya ba.”
"I begged your disciples to cast it out, but they could not."
41 Yesu ya amsa ya ce, “Ya karkataccen zamani marar bangaskiya, har yaushe ne zan kasance tare da ku, ina kuma haƙuri da ku? Kawo yaronka nan.”
"O faithless and perverse generation," said Jesus, "how long shall I be with you and bear with you? Bring your son to me."
42 Yaron yana kan zuwa ke nan, sai aljanin ya buga shi ƙasa, cikin farfaɗiya. Amma Yesu ya kwaɓe mugun ruhun, ya warkar da yaron, sai ya miƙa shi ga mahaifinsa.
But while he was yet coming the demon dashed him down, and cruelly convulsed him. Then Jesus rebuked the unclean spirit, and cured the boy, and gave him back to his father.
43 Duk suka yi mamakin girman Allah. Yayinda kowa yana cikin mamakin dukan abubuwan da Yesu ya yi, sai ya ce wa almajiransa,
And they were all awestruck at the mighty power of God. But while everyone was marveling at what he was doing, he said to his disciples.
44 “Ku kasa kunne da kyau ga abin da zan faɗa muku. Za a bashe Ɗan Mutum ga hannun mutane.”
"Let these words sink into your ears; for the son of man is about to be betrayed into the hands of men."
45 Amma ba su fahimci abin da yake nufi da wannan magana ba. Ba su gane ba, don an ɓoye musu shi. Su kuwa sun ji tsoro su tambaye shi.
But they did not understand this saying; it was hidden from them so that they perceived it not, and they were sore afraid to ask him about his saying.
46 Wata gardama ta tashi a tsakanin almajiran, a kan ko wane ne a cikinsu zai zama mafi girma
Now there arose a dispute among them as to which one of them was the greatest.
47 Da yake Yesu ya san tunaninsu, sai ya ɗauki wani ƙaramin yaro, ya sa ya tsaya kusa da shi.
And Jesus who knew the dispute that was in their hearts, took a young child, and placed him by his side;
48 Sai ya ce musu, “Duk wanda ya karɓi wannan ƙaramin yaron a cikin sunana, ni ya karɓa, kuma duk wanda ya karɓe ni, ya karɓi wanda ya aiko ni ne. Gama mafi ƙanƙanta duka a cikinku, shi ne kuma mafi girma.”
then he said to them. "Whoever shall receive this little child in my name receives me; and whoever shall receive me receives him that sent me. For it is the lowliest among you all who is great."
49 Sai Yohanna ya ce, “Ubangiji, mun ga wani mutum yana fitar da aljanu a cikin sunanka, muka yi ƙoƙarin hana shi, don shi ba ɗaya ba ne daga cikinmu.”
"Master," said John, "we saw a man who was casting out demons in your name, and we forbade him, because he was not following us."
50 Yesu ya ce, “Kada ku hana shi, gama duk wanda ba ya gāba da ku, naku ne.”
But Jesus said, "Forbid him not, for he who is not against you is for you."
51 Da lokaci ya yi kusa da za a ɗauki Yesu zuwa sama, sai ya ɗaura niyyar tafiya Urushalima.
When now when the time drew near for him to be received up, he stedfastly set his face to go to Jerusalem,
52 Sai ya aiki’yan saƙo, su yi gaba. Su kuwa, suka shiga cikin wani ƙauyen Samariyawa, don su shirya masa abubuwa.
and sent messengers before him. These went and entered into a Samaritan village to make ready for him.
53 Amma mutanen ƙauyen ba su karɓe shi ba, don yana kan hanyar zuwa Urushalima ne.
But they did not receive him because his face was set to go to Jerusalem.
54 Da almajiransa, Yaƙub da Yohanna suka ga haka, sai suka yi tambaya suka ce, “Ubangiji, kana so mu kira wuta ta sauka daga sama ta hallaka su?”
And when his disciples, Jamesand John, saw this they said, "Lord, are you willing for us to bid fire come down from heaven and destroy them?" As Elijah did.
55 Amma Yesu ya juya, ya kwaɓe su.
But he turned and rebuked them and said,
56 Sai shi da almajiransa suka tafi wani ƙauye.
"You know not what kind of spirit you share, for the Son of man came not to destroy men’s lives, but to save them." And they went to another village.
57 Suna kan tafiya a hanya, sai wani mutum ya ce masa, “Zan bi ka, duk inda za ka.”
As they were going on their way, a man came to him and said, "I will follow wherever you go."
58 Yesu ya ce, “Yanyawa suna da ramummuka, tsuntsayen sararin sama suna da sheƙuna, amma Ɗan Mutum ba shi da wurin da zai sa kansa.”
"The foxes have their holes," Jesus answered, "and the wild birds have their nest, but the Son of man has not where to lay his head."
59 Ya kuma ce wa wani mutum, “Ka bi ni.” Amma mutumin ya amsa ya ce, “Ubangiji, bari in je in binne mahaifina tukuna.”
To another he said, "Follow me!" But he replied, "Permit me first to go and bury my father."
60 Yesu ya ce masa, “Ka bar matattu su binne matattunsu, amma kai, ka je ka yi shelar mulkin Allah.”
"Leave the dead to bury their own dead," said Jesus to him, "go you and announce, far and wide the kingdom of God."
61 Har wa yau, wani ya ce, “Zan bi ka, Ubangiji, amma ka bar ni in je in yi bankwana da iyalina tukuna.”
And another man also said to him. "I will follow you, Lord; but first permit me to bid farewell to those who are in my house."
62 Yesu ya amsa ya ce, “Babu wani da yakan sa hannunsa a garman shanu, sa’an nan ya waiwaya baya, da ya isa ya shiga hidima a cikin mulkin Allah ba.”
But Jesus answered him, "No man who puts his hand to the plow and then looks back, is fit for the kingdom of God."

< Luka 9 >