< Luka 9 >
1 Bayan da Yesu ya tara Sha Biyun wuri ɗaya, sai ya ba su iko da izini na fitar da dukan aljanu, da na warkar da cututtuka.
Acunüng Jesuh naw axüisaw he xaleinghngih atänga jah khü lü, khawyai he avan jah mkhütnaka johit la natnak he jah m'yainak be theinak jah pe lü,
2 Ya kuma aike su, su yi wa’azin mulkin Allah, su kuma warkar da marasa lafiya.
Pamhnama khawa mawng sang hü khai he la, am phetki he jah m’yai be khai hea a jah tüih.
3 Ya ce musu, “Kada ku ɗauki kome don tafiyar, wato, ba sanda, ba jaka, ba burodi, ba kuɗi, ba riga na biyu.
Acunüng Jesuh naw, “Nami cehnaka ipi ä nami cehei vai, ksawngkhea pi kyase, kthäheinaka ngjaa pi kyase, eia pi kyase, nguia pi kyase, ä nami cehei vai, kcu nghngih ä nami cehei vai.
4 Duk gidan da kuka sauka, ku zauna nan sai kun bar garin.
“Acunüng nami phanaka ima nami awm laih laih vai, acun üngka naw nami ktawih be vai.
5 In mutane ba su karɓe ku ba, sa’ad da kun bar garinsu, ku karkaɗe ƙurar ƙafafunku don shaida a kansu.”
“Am ning jah dokhamki cun, acuna mlüh üngka naw nami ktawih be üng, ami ngsingnak vaia nami khawpha üngka mvut nami khawk hüt vai,” a ti.
6 Sai suka tashi suka shiga ƙauye zuwa ƙauye suna wa’azin bishara, suna warkar da marasa lafiya a ko’ina.
Acunüng axüisaw he cun ktawih u lü, ngnam naküta cit hü u lü, thangkdaw sang hü u lü, hmün naküt üng ami jah m’yai hü be.
7 Yanzu fa, Hiridus mai sarauta ya ji labarin dukan abubuwan da suke faruwa. Sai ya rikice, don waɗansu mutane suna cewa, Yohanna Mai Baftisma ne ya tashi daga matattu,
Acunüng, Kalile uki Herod naw ahmäi ngja law lü aktäa cäi lawki; avang he naw, “Baptican Johan xüng law beki ni,” ami ti.
8 waɗansu kuma suna cewa, annabi Iliya ne ya sāke bayyana. Waɗansu kuma har wa yau, suna cewa, ɗaya daga cikin annabawa na dā ne, ya tashi.
Avang naw, “Elijah ngdang lawki ni,” ti u se, avang he naw, “Ajana sahma mat mat xüng law beki he ni” ami ti.
9 Amma Hiridus ya ce, “Yohanna dai na yanke kansa, amma wanne mutum ne nake jin labarin abubuwan nan a kansa?” Sai ya yi ƙoƙari ya ga Yesu.
Acunüng, Herod naw, “Johan cun a lu ka xün päng ni, ahikba sena a mawng ka ngjak hin u ni?” a ti. Acunüng Herod naw Jesuh a hmuh vai aktäa ngjahlüki.
10 Da manzannin suka dawo, sai suka faɗa wa Yesu abin da suka yi. Sai ya ɗauke su, suka keɓe kansu su kaɗai, zuwa wani gari da ake kira Betsaida.
Acunüng, ngsä he law be u lü, ami bilawh he Jesuh üng ami jah mtheh law. Acunüng, Jesuh naw jah ngkhahpüi lü Bethsaida mlüh ami tia, a jah cehpüi.
11 Amma taron mutane suka ji labari, sai suka bi shi. Ya marabce su, kuma ya yi musu magana a kan mulkin Allah, ya kuma warkar da masu bukatar warkarwa.
Cunsepi, khyang he naw sim u lü, ami läk laih laih, acunüng Jesuh naw aktäa jah dokham lü, Pamhnama khawa mawng ngthu jah mtheki naw, m’yai be vai avan a jah m’yai be.
12 Da rana ta kusa fāɗuwa, sai Sha Biyun suka zo wurinsa, suka ce, “Ka sallami taron domin su shiga ƙauyuka na kewaye, su nemi abin da za su ci, da wurin kwana, don inda muke, ba kowa.”
Acunüng, nghngi kya law hlü se, xaleinghngih he Jesuha veia law u lü, “Khyang he mi peisu ngnam he la loea jah tüia, ngsutnak la ei vai hmuei khai hea, hina mäih khawkhyawng khawa mi awm ve,” ami ti.
13 Yesu ya ce, “Ku, ku ba su wani abu su ci.” Sai suka ce masa, “Muna da burodi biyar da kifi biyu kaɗai. Sai dai, in mun je mu sayi abinci domin dukan wannan taron.”
Acunüng Jesuh naw jah msang lü, “Nangmi naw ami ei vai jah pe ua,” a ti. Acunüng axüisaw he naw, “Muk mhma la nga nglung nghngih ni kami tak. Hin he avana hama, ei vai kami va kheih vai ti aih lü? ami ti.
14 Maza kaɗai sun kai kusan dubu biyar. Amma ya ce wa almajiransa, “Ku sa su su zauna a ƙungiya hamsin-hamsin.”
Kpami däng pi thawng mhma lawki hea kyaki. Acunüng Jesuh naw, axüisaw he üng, “Mhmakip cia, aphäh phäha jah ngawhsak u,” a ti.
15 Haka almajiran suka yi, kowa kuwa ya zauna.
Acunüng acunkba ami van ami jah ngawhsak.
16 Sai Yesu ya ɗauki burodin biyar da kifin biyun, ya ɗaga kansa sama, ya yi godiya, ya kuma kakkarya su. Ya ba wa almajiransa, domin su rarraba wa mutanen.
Jesuh naw muk mhma la nga nglung nghngih lo lü, khankhawa hang mang lü, josenak am kbe lü, boki naw, khyang hea maa, ami tak vaia axüisaw he üng a jah pet.
17 Duka kuwa suka ci suka ƙoshi. Almajiran suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna goma sha biyu.
Acunüng, ami van naw ei u lü phü u se, ami ei mnawi cä xaleinghngiha ami kaw.
18 Wata rana sa’ad da Yesu yana addu’a a ɓoye, almajiransa kuma suna tare da shi, sai ya tambaye, su ya ce, “Wa, taron mutane ke ce da ni?”
Acunüng hinkba kyaki, Jesuh amät ktaiyü se, axüisaw he a veia lawki he, Jesuh naw, “Khyang he naw ua ni ami na ngaih,” ti lü a jah kthäh.
19 Suka amsa, suka ce, “Waɗansu suna cewa, Yohanna Mai Baftisma, waɗansu kuma annabi Iliya, har wa yau waɗansu suna cewa, kai ɗaya daga cikin annabawan da ne, da ya tashi da rai.”
Acunüng, axüisaw he naw, “Baptican Johana ning ngai ve u; cunsepi, avang naw, ‘Elijaha’ ning ngai ve u, avang naw, ‘Akphyüma sahma mat mat xüng law beki ni’ ti ve u,” tia ami msang.
20 “Amma ku fa, wa, kuke ce da ni?” Bitrus ya amsa ya ce, “Kiristi na Allah.”
Acunüng Jesuh naw, “Acuna akyaküng, nangmi naw mä ua ni nami na ngaih,” a ti. Pita naw, “Nang cun Mhnama Mesijah ni” a ti.
21 Yesu ya gargaɗe su da ƙarfi, kada su gaya wa kowa wannan magana.
Acunüng, upi acuna mawng ä ami mtheh vaia a jah ksük.
22 Ya sāke cewa, “Dole ne Ɗan mutum ya sha wahaloli da yawa, dattawa, da manyan firistoci, da malaman dokoki kuma su ƙi shi, kuma dole a kashe shi, a rana ta uku kuma a tā da shi da rai.”
Acunüng Jesuh naw, “Khyanga capa naw aktäa khuikhanak khamei khai, angvai he, ktaiyü ngvai he la thum ksing he naw ma khai he, hnima kya khai, amhmüp kthum üng tho law be khai,” a ti.
23 Sai ya ce wa dukansu, “In wani zai bi ni, dole yă mūsanta kansa, ya ɗauki gicciyensa kowace rana, ya bi ni.
Acunüng, ami vana veia, “Upi na läk law khai ngaiki naw amät ä ngaikyu lü, a kutlamktung amhmüp tä se kawt lü na läk law se.
24 Gama duk mai son ceton ransa zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa saboda ni zai same shi.
“Upi a xünnak küikyanei khai büki naw mkhyüh lü, upi keia phäha, a xünnak mkhyühki naw küikyanei khai.
25 Ina amfani, in mutum ya ribato duniya duka, amma ya rasa ransa, ko kuma ya yi hasarar ransa.
“Khyang naw khawmdek avan ka na lü, amät la amät pyeh se, am acunüng xükse, ia ni a ngmangnak kawm?
26 Duk wanda yake jin kunyana da na kalmomina, Ɗan Mutum ma zai ji kunyarsa sa’ad da zai zo a cikin ɗaukakarsa, da ɗaukakar Uban, da kuma ta tsarkaka mala’ikun.
“Upi, kei la ka ngthu ngkekhyakei naki cun, khyanga Capa naw, a pa hlüngtainak, amäta hlüngtainak la khankhawngsä ngcim he am a law be üng, ngkekhyakei na be khai.
27 “Gaskiya nake gaya muku, waɗansu da suke tsattsaye a nan ba za su ga mutuwa ba, sai sun ga mulkin Allah.”
“Akcanga ka ning jah mthehki, hin üng ngdüiki he avang, Pamhnama khaw am ami hmuh hlana küt üng am thi khai he awmki he” a ti.
28 Bayan kamar kwana takwas da yin wannan magana, sai Yesu ya ɗauki Bitrus, da Yohanna, da kuma Yaƙub, suka hau kan dutse tare don yin addu’a.
Acuna ngthu a pyen kän amhmüp khyet üng, Pita, Johan la Jakuk jah ngkhahpüi lü, ktaiyü khaia mcunga kaiki.
29 Yana cikin addu’a, sai kamannin fuskarsa ta sāke, tufafinsa kuma suka zama da haske kamar hasken walƙiya.
A ktaiyü k’um üng, a hmai hnga law lü, a suisak he a ktäa bawk law lü ngkah lawki.
30 Sai ga mutum biyu, Musa da Iliya, suka bayyana cikin kyakkyawar daraja, suna magana da Yesu.
Acunüng, khyang nghngih Jesuh am ngthuheiki xawi, acun kxawi cun Mosi la Elijaha kyaki xawi,
31 Suka yi zance a kan tashinsa, wanda shi ya kusan ya kawo ga cikarsa a Urushalima.
khankhaw hlüngtai kyäpsawknak suiawi ni lü, Jerusalema a khuikhanak vaia mawng pyenki xawi.
32 Barci kuwa ya kama Bitrus da abokan tafiyarsa sosai. Da idanunsu suka warware, sai suka ga ɗaukakarsa da kuma mutum biyun tsaye tare da shi.
Acunüng, Pita la a püi he ipeiki he let law u lü, a hlüngtainak la a peia khyang nghngih ngdüiki xawi ami jah hmuh.
33 Da mutanen na barin Yesu, sai Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, ya yi kyau da muke nan. Bari mu kafa bukkoki guda uku, wato, ɗaya dominka, ɗaya domin Musa, ɗaya kuma domin Iliya.” (Bai ma san abin da yake faɗi ba.)
Acun xawi naw Jesuh ani ktawih law hlü tak üng, Pita naw i a pyen ä ksingei lü Jesuh üng, “Saja aw, hia awm hin daw ve, na hama mat, Mosia hama mat, Elijaha hama mat samca kthum kami sa khai,” a ti.
34 Yayinda yake cikin magana, sai wani girgije ya bayyana ya rufe su, sai suka ji tsoro, yayinda suke shiga cikin girgijen.
Acukba a pyen k’um üng khawngmei naw jah msungin law se, axüisaw he kyü lawki he.
35 Wata murya ta fito daga cikin girgijen, tana cewa, “Wannan Ɗana ne, zaɓaɓɓena, ku saurare shi.”
Ngmei üng “Hin hin ka xüa ka Capa ni, a ngthu ngai u,” tia ngthu ngthang lawki.
36 Da muryar ta gama magana, sai suka tarar Yesu shi kaɗai ne. Almajiran kuwa suka riƙe wannan al’amari a zukatansu. A lokacin nan, ba su gaya wa kowa abin da suka gani ba.
Acunüng, ngthu a ngdüm la, Jesuh amät däng ami hmuh. Axüisaw he cun am khikheh u lü, ami hmuha mawng cun, acuna pät üng u üng pi am mtheh u.
37 Kashegari, sa’ad da Yesu tare da almajiran nan uku suka sauka daga kan dutsen, sai taro mai yawa ya haɗu da shi.
A ngawi üng mcung üngka naw axüisaw kthum am kyum be u se, khyang khawjah naw ami na khyum.
38 Sai wani mutum daga cikin taron ya yi kira da ƙarfi ya ce, “Malam, ina roƙonka, ka dubi ɗan nan nawa, gama shi ne kaɗai nake da shi.
Acunüng, khyang hea ksunga khyang mat ngpyang lü, “Saja aw, amät däng ka canak ka capa teng law, ning hui na veng.
39 Wani ruhu yakan kama shi, sai ya yi ihu farar ɗaya. Yakan sa shi farfaɗiya, har bakinsa ya yi kumfa. Da ƙyar yake barinsa, yana kuwa kan hallakar da shi.
“Khawyai naw man khawi se, ngpyangin sawxat xatki, a mci mvawn pi kya law khaia pawh lü mdek üng a kyuk sak khawi, acunkba mkhuimkha lü am ceh hlü ta.
40 Na roƙi almajiranka su fitar da shi, amma ba su iya ba.”
“Acunüng, na xüisaw he üng ami ktäm vaia jah nghui na ni se, amimi naw pi ani cun am ami ktäm thei,” a ti.
41 Yesu ya amsa ya ce, “Ya karkataccen zamani marar bangaskiya, har yaushe ne zan kasance tare da ku, ina kuma haƙuri da ku? Kawo yaronka nan.”
Jesuh naw, “Jumnak am ta lü, üpnak am awmkia khyang he, nami veia ivei ka awm khai aw? Ivei ka ning jah msawk vai aw?” ti lü, acuna khyang üng, “Na ca hia lawpüia,” ti lü a msang.
42 Yaron yana kan zuwa ke nan, sai aljanin ya buga shi ƙasa, cikin farfaɗiya. Amma Yesu ya kwaɓe mugun ruhun, ya warkar da yaron, sai ya miƙa shi ga mahaifinsa.
Acunüng, hnasen a law k'um üng, khawyai naw khawmdek khana kyuk sak lü, aknaa a pawh. Cunsepi, Jesuh naw, khawyai kse jüi lü, anghmaw mdaw beki naw a pa üng a pet.
43 Duk suka yi mamakin girman Allah. Yayinda kowa yana cikin mamakin dukan abubuwan da Yesu ya yi, sai ya ce wa almajiransa,
Acunüng, khyang avan naw Pamhnama hlüngtainak cun aktäa kyühkhyai lawki he. Ami van naw acunkba, a bilawh he ami kyühkhyai law üng, Jesuh naw axüisaw he üng,
44 “Ku kasa kunne da kyau ga abin da zan faɗa muku. Za a bashe Ɗan Mutum ga hannun mutane.”
“Ka ning jah mtheh hlü ä mhnih u; Khyanga Capa, khyang hea kut üng mansak vai ng'et law ve,” a ti.
45 Amma ba su fahimci abin da yake nufi da wannan magana ba. Ba su gane ba, don an ɓoye musu shi. Su kuwa sun ji tsoro su tambaye shi.
Cunsepi, a ngthu pyena suilam cun am ami ksing, ami ksing vaia mjiha kyaki, ami kthäh vaia pi ami kyüh.
46 Wata gardama ta tashi a tsakanin almajiran, a kan ko wane ne a cikinsu zai zama mafi girma
Acunüng, u kyäp säih khai tia amimät he ana ngcuh hü u se,
47 Da yake Yesu ya san tunaninsu, sai ya ɗauki wani ƙaramin yaro, ya sa ya tsaya kusa da shi.
Jesuh naw ami ngaikyunak jah ksing lü, hnasenca mat kai lü, a peia taki naw,
48 Sai ya ce musu, “Duk wanda ya karɓi wannan ƙaramin yaron a cikin sunana, ni ya karɓa, kuma duk wanda ya karɓe ni, ya karɓi wanda ya aiko ni ne. Gama mafi ƙanƙanta duka a cikinku, shi ne kuma mafi girma.”
“Upi hina hnasenca, ka ngming üng dokhamki cun, kei na dokhamki ni, acunüng u pi, kei na dokhamki cun, kei na tüi lawki pi dokhamki ni. Nangmi üng jaw säihki, acun cen kyäp säih khai,” a ti.
49 Sai Yohanna ya ce, “Ubangiji, mun ga wani mutum yana fitar da aljanu a cikin sunanka, muka yi ƙoƙarin hana shi, don shi ba ɗaya ba ne daga cikinmu.”
Acunüng Johan naw, “Saja aw, khyang mat naw na ngming am khawyai he jah ktäm se kami hmuh, keimi üngka am nikia kyase am a pawh ti vaia kami kpyai,” a ti.
50 Yesu ya ce, “Kada ku hana shi, gama duk wanda ba ya gāba da ku, naku ne.”
Acunüng, Jesuh naw, “Ä kpyai ti ua, u pi nangmi am ning jah hnengki cun nami püia kyaki ni,” a ti.
51 Da lokaci ya yi kusa da za a ɗauki Yesu zuwa sama, sai ya ɗaura niyyar tafiya Urushalima.
Acunüng, khankhawa a cehnak vai ng'et law se, Jerusalema a ceh vai lingki.
52 Sai ya aiki’yan saƙo, su yi gaba. Su kuwa, suka shiga cikin wani ƙauyen Samariyawa, don su shirya masa abubuwa.
Ngsä he a ma a jah na tüih. Acunüng, ana dawng u lü, ana ngtün pe khai hea Samarih khaw mata lutki he.
53 Amma mutanen ƙauyen ba su karɓe shi ba, don yana kan hanyar zuwa Urushalima ne.
Jerusalema cit khaia a büa phäha Samarih khyang he naw am a na dokham u.
54 Da almajiransa, Yaƙub da Yohanna suka ga haka, sai suka yi tambaya suka ce, “Ubangiji, kana so mu kira wuta ta sauka daga sama ta hallaka su?”
Acunüng, axüisaw xawi Johan la Jakuk naw acun ani ksing la, “Bawipa aw, hin he ami ngkhihnak bäih vaia, khankhawa mei han khü vaia na ngjahlüki aw?” tia ani kthäh.
55 Amma Yesu ya juya, ya kwaɓe su.
Acunüng, Jesuh naw ani veia nghlat law lü, a jah jüih.
56 Sai shi da almajiransa suka tafi wani ƙauye.
Acunüng ngnam kcea citki he.
57 Suna kan tafiya a hanya, sai wani mutum ya ce masa, “Zan bi ka, duk inda za ka.”
Lam ami ceh k'um üng khyang mat naw, “Na cehnak avana ka ning läk khai,” ti lü Jesuh a mtheh,
58 Yesu ya ce, “Yanyawa suna da ramummuka, tsuntsayen sararin sama suna da sheƙuna, amma Ɗan Mutum ba shi da wurin da zai sa kansa.”
Jesuh naw, “Sauie naw khui ta u lü, kha he naw pi ngbu taki he, khyanga Capa naw ta a lu a khännak vai la a xüieinak vai pi am ta ve,” a ti.
59 Ya kuma ce wa wani mutum, “Ka bi ni.” Amma mutumin ya amsa ya ce, “Ubangiji, bari in je in binne mahaifina tukuna.”
Acunüng, Jesuh naw khyang kcea veia, “Na läk lawa,” a ti. Cunsepi ani naw, “Bawipa aw, cit be lü ka pa va k'ut hüt ma vang,” a ti.
60 Yesu ya ce masa, “Ka bar matattu su binne matattunsu, amma kai, ka je ka yi shelar mulkin Allah.”
Acunüng Jesuh naw, “Khyangkthi he naw amimät akthi k'utei u se; nang ta Pamhnama khawa mawng ngthu va sanga,” a ti.
61 Har wa yau, wani ya ce, “Zan bi ka, Ubangiji, amma ka bar ni in je in yi bankwana da iyalina tukuna.”
Akce naw pi, “Saja aw, ka ning läk law khai; cunsepi, ka im üngka he, ngthukdaw am jah va ngkhyahpüi ma vang,” a ti.
62 Yesu ya amsa ya ce, “Babu wani da yakan sa hannunsa a garman shanu, sa’an nan ya waiwaya baya, da ya isa ya shiga hidima a cikin mulkin Allah ba.”
Acunüng, Jesuh naw mtheh lü, “Upi, lai thawn khaia ngtün lü, a hnu lam tengki cun Pamhnama khaw am ä nghlawiki ni,” a ti.