< Luka 8 >
1 Bayan wannan sai Yesu ya zazzaga gari da ƙauye, yana wa’azin bisharar mulkin Allah. Sha Biyun nan kuwa suna tare da shi,
In zgodí se po tem, in on je hodil po mestih in vaséh, učeč in oznanjujoč evangelj o kraljestvu Božjem; in dvanajsteri ž njim,
2 da kuma waɗansu mata waɗanda aka warkar da su daga cututtukansu, da kuma mugayen ruhohi. Cikinsu akwai Maryamu (wadda ake kira Magdalin) wadda aljanu bakwai suka fito daga cikinta.
In nektere žene, ktere so uzdravljene bile od duhov hudobnih in od bolezni, Marija, ki se imenuje Magdalena, iz ktere je bilo sedem hudičev izšlo,
3 Da Yowanna matar Kuza, manajan iyalin Hiridus; da Suzana; da waɗansu mata da yawa. Waɗannan mata suna taimaka musu cikin hidima, daga cikin abin da suke da shi na zaman gari.
Joana žena Huza pristavnika Herodovega, in Suzana, in drugih veliko, ktere so mu služile z imenjem svojim.
4 Yayinda taron mai girma na taruwa, mutane kuma daga garuruwa dabam-dabam suna zuwa wurin Yesu, sai ya ba da wannan misali ya ce,
Ko se je pa veliko ljudstva sešlo, in tistih, kteri so iz mest prihajali k njemu, pové jim v priliki:
5 “Wani manomi ya fita domin ya shuka irinsa. Da yana watsa irin, sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, aka tattaka su, tsuntsayen sararin sama kuma suka cinye su.
Izšel je sejalec sejat seme svoje; in ko je sejal, eno je padlo poleg ceste, in pogazilo se je, in tice nebeške so ga pozobale.
6 Waɗansu suka fāɗi a kan dutse, da suka tsira sai suka yanƙwane don babu ruwa a wurin.
In drugo je padlo na skalo, in ko je pognalo, usahnilo je, ker ni imelo vlage.
7 Waɗansu kuma suka fāɗi a cikin ƙaya. Da suka yi girma tare, sai ƙayan suka shaƙe su.
In drugo je padlo sredi trnja, in trnje je zrastlo, in udušilo ga je.
8 Waɗansu kuma har yanzu, suka fāɗi a ƙasa mai kyau, suka yi girma, suka ba da amfani riɓi ɗari-ɗari, fiye da abin da aka shuka.” Da faɗin haka sai ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
In drugo je padlo na dobro zemljo, in ko je pognalo, doneslo je stoteri sad. Ko je to pravil, klical je: Kdor ima ušesa, da sliši, naj sliši!
9 Almajiransa suka tambaye shi ma’anar wannan misali.
Vpraševali pa so ga učenci njegovi, govoreč: Kakošna bi bila ta prilika?
10 Sai ya ce, “Ku ne aka ba sanin asirin mulkin Allah, amma ga sauran mutane kam, ina magana da misalai, saboda, “‘ko da yake suna kallo, ba za su gani ba, ko da yake suna ji, ba za su gane ba.’
On pa reče: Vam je dano, da spoznate skrivnosti kraljestva Božjega; drugim pa v prilikah, da gledajo in ne vidijo, ter slišijo in ne umejo.
11 “Ga ma’anar misalin, irin, shi ne maganar Allah.
Ta prilika pa je: Seme je beseda Božja:
12 Waɗanda suka fāɗi a kan hanya su ne mutanen da suka ji, amma Iblis, yakan zo ya ɗauke maganar daga zuciyarsu, don kada su gaskata, su sami ceto.
A kteri so poleg ceste posejani, ti so, kteri slišijo: ali potem pride hudič in vzeme besedo iz srca njih, da ne bi verovali in zveličali se.
13 Na kan dutse kuwa, su ne da jin maganar, sukan karɓa da murna, amma ba su da saiwa. Sukan gaskata na ɗan lokaci, amma lokacin gwaji, sai su ja da baya.
A kteri so na skalo posejani, ti, kteri besedo, ko so jo sklišali, z veseljem sprejemajo; in ti korenine nimajo, kteri nekaj časa verujejo, a v čas izkušnjave odpadejo.
14 Irin da suka fāɗi a cikin ƙaya kuwa, su ne mutanen da suka ji, amma a kwana a tashi, tunanin kayan duniya, da neman arziki, da son jin daɗi, sukan hana su ba da’ya’ya.
Kar je pa v trnje padlo, to so ti, kteri slišijo: ali ker za skrbmí in bogastvom in slastmi življenja hodijo, udušé se, in ne donašajo sadú.
15 Amma irin da suka fāɗi a ƙasa mai kyau kuwa, su ne mutane masu kyakkyawar zuciya, mai kyau, da suka ji, suka riƙe, suka kuma jimre har suka ba da’ya’ya.”
Kar je pa na dobro zemljo padlo, to so ti, kteri v dobrem in blagem srcu varujejo besedo, ktero so slišali, in donašajo sad v trpljenji.
16 “Ba mai ƙuna fitila sa’an nan ya ɓoye ta a cikin tulu, ko kuma ya sa ta a ƙarƙashin gado ba. A maimakon haka, yakan sa ta a kan wurin ajiye fitila, saboda mutane masu shigowa su ga haske.
Nikdor pa sveče, ko jo prižgè, ne skrije pod mernik, ali dene pod posteljo; nego postavi jo na svečnik, da ti, kteri vhajajo, vidijo luč.
17 Ba abin da yake ɓoye da ba za a fallasa ba. Kuma ba abin da yake rufe, da ba za a sani ba, ko a fitar da shi a fili ba.
Kajti nič ni prikritega, kar se ne bo razodelo; tudi skrivnega ne, kar se ne bo zvedelo in na svetlo prišlo.
18 Saboda haka, ku yi tunani da kyau yadda kuke saurara. Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, duk wanda ba shi da shi kuma, abin da yake tsammani yana da shi ma, za a karɓe daga gare shi.”
Glejte torej, kako boste poslušali: kajti kdor imá, dalo mu se bo; a kdor nima, odvzelo mu se bo tudi to, kar misli, da ima.
19 Sai uwar Yesu da’yan’uwansa suka zo, domin su gan shi, amma ba su iya zuwa kusa da shi ba, saboda taron.
Pridejo pa k njemu mati njegova in bratje njegovi; ali za voljo ljudstva niso mogli priti do njega.
20 Sai wani ya faɗa masa cewa, “Ga uwarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje suna so su gan ka.”
In sporočé mu, govoreč: Mati tvoja in bratje tvoji stojé zunej, in radi bi te videli.
21 Ya amsa ya ce, “Mahaifiyata da’yan’uwana, su ne waɗanda suke jin maganar Allah, suna kuma aikata ta.”
On pa odgovarjajoč, reče jim: Mati moja in bratje moji so ti, kteri besedo Božjo poslušajo in delajo po njej.
22 Wata rana Yesu ya ce wa almajiransa, “Mu haye zuwa wancan gefen tafkin.” Sai suka shiga jirgin ruwa suka fara tafiya.
In zgodí se en dan, in on stopi v ladjo in učenci njegovi; in reče jim: Prepeljimo se na oni kraj jezera! In odpeljejo se.
23 Da suna cikin tafiya, sai barci ya kwashe shi. Sai wata babban iska ta taso kan tafkin, har ruwa ya fara shiga cikin jirgin. Suka shiga babban hatsari.
A ko so se peljali, zaspí. Kar snide vihar na jezero, in potapljali so se, in bili so v nevarnosti.
24 Almajiran suka je suka tashe shi daga barci, suka ce, “Ubangiji, Ubangiji, za mu nutse!” Ya tashi ya kwaɓe iskar da kuma haukar ruwan. Sai ruwan da iskar suka natsu. Kome ya yi tsit.
In pristopivši, zbudé ga, govoreč: Učenik! učenik! pogibamo! A on vstavši, zapretí vetru in valovju; in umirita se, in nastala je tihota.
25 Sai ya tambayi almajiransa, “Ina bangaskiyarku?” A cikin tsoro da mamaki, suka ce wa junansu, “Wane ne wannan? Yana ba da umarni ga iska da ruwa ma, kuma suna biyayya da shi?”
In reče jim: Kje je vera vaša? A oni so se uplašili, in začudijo se, govoreč eden drugemu: Kdo neki je ta, da tudi vetrovom zapoveduje in vodi, in poslušajo ga?
26 Suka shiga jirgin ruwa zuwa yankin Gerasenawa da yake a hayin tafkin, daga wajen Galili.
In preplavijo se v zemljo Gadarensko, ktera je Galileji nasproti.
27 Da Yesu ya sauka daga jirgin, sai ga wani mutum mai aljanu daga garin. Mutumin ya daɗe bai sa tufafi ba, kuma ba ya zama a gida. Yana zama a cikin kaburbura.
Ko pa izide na zemljo, sreča ga en človek iz mesta, kteri je imel hudiča uže dolgo časa, in v obleko se ni oblačil, in v hiši ni prebival, nego v grobih.
28 Da ya ga Yesu, sai mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi, ya fāɗi a gabansa, yana ihu cewa, “Ina ruwanka da ni, Yesu, Ɗan Allah Mafi Ɗaukaka? Ina roƙonka, kada ka ba ni wahala!”
A ko ugleda Jezusa, zakričí in pade pred-nj, in z močnim glasom reče: Kaj imaš z menoj, Jezus, sin Boga najvišega: Prosim te, nikar mene muči!
29 Gama Yesu ya riga ya umarci mugun ruhun ya fita daga mutumin. Sau da yawa mugun ruhun ya sha kamunsa. Ko da yake akan daure shi hannu da ƙafa, da sarƙa, a kuma yi gadinsa, amma yakan tsinke sarƙoƙinsa, aljanun kuma su kore shi zuwa wuraren kaɗaici, inda ba kowa.
Ukazal je bil namreč duhu nečistemu, naj izide iz človeka: kajti uže dolgo časa ga je bil metal, in vezali so ga z verigami in vezmí, ter so ga varovali; ali potrgal je vezí, in gonil ga je hudič po puščavah.
30 Yesu ya tambaye shi, “Mene ne sunanka?” Sai ya amsa, “Tuli,” gama aljanu masu ɗumbun yawa ne suna cikinsa.
Vpraša pa ga Jezus, govoreč: Kako ti je ime? On pa reče: Množica; kajti obsedlo ga je bilo mnogo hudičev.
31 Suka yi ta roƙonsa kada yă umarce su su shiga ramin Abis. (Abyssos )
In prosili so ga, naj jim ne zapové iti v brezno. (Abyssos )
32 A wurin kuwa, akwai babban garken aladu da suke kiwo a gefen tudu. Aljanun suka roƙi Yesu ya bar su, su shiga cikin aladun, ya kuwa yardar musu.
Bila je pa tam velika čreda svinj, ktere so se pasle na gori; in prosili so ga, naj jim dovoli, da vnidejo va-nje. In dovoli jim.
33 Da aljanun suka fita daga cikin mutumin, sai suka shiga cikin aladun. Garken kuma ya gangara daga kan tudun zuwa cikin tafkin, kuma suka nutse.
In hudiči izidejo iz človeka in vnidejo v svinje; in zakadí se čreda z brega v jezero, in potonejo.
34 Da masu kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka ruga da gudu zuwa garin da kewaye suka kai labari.
Videvši pa pastirji, kar se je zgodilo, pobegnejo, ter odidejo in sporočé po mestu in po vaséh.
35 Mutanen kuma suka fito don su ga abin da ya faru. Da suka iso wurin Yesu, sai suka tarar da mutumin da aljanun suka fita daga cikinsa, yana zaune kusa da Yesu sanye da tufafi, kuma cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
Ter izidejo gledat, kaj se je zgodilo; in pridejo k Jezusu, in najdejo človeka, iz kterega so bili hudiči izšli, da je oblečen in pameten, in sedí pri nogah Jezusovih; in uplašijo se.
36 Waɗanda suka ga abin da faru, suka gaya wa mutanen yadda aka warkar da mai aljanun.
Sporočé pa jim tudi ti, kteri so bili videli, kako je obsedenec ozdravel.
37 Sai dukan mutanen yankin Gerasenawa suka roƙi Yesu ya bar su, don sun tsorata sosai. Sai Yesu ya shiga jirgin ruwa ya tafi.
In zaprosi ga vsa množica iz okolice Gadarenske, naj odide od njih; kajti strah velik jih je preletal. A on stopi v ladjo in se vrne.
38 Mutumin da aka fitar da aljanun daga cikinsa, ya roƙi Yesu don yă tafi tare da shi, amma Yesu ya sallame shi ya ce,
Prosil pa ga je mož, iz kterega so bili izšli hudiči, da bi bil ž njim; ali Jezus ga odpravi, govoreč:
39 “Koma gida, ka shaida babban alherin da Allah ya yi maka.” Sai mutumin ya tafi yana faɗin abin da Yesu ya yi masa a duk garin.
Vrni se na dom svoj, in pripoveduj, kaj ti je storil Bog. Pa odide, po vsem mestu oznanjujoč, kaj mu je storil Jezus.
40 Da Yesu ya koma, taron suka marabce shi, don dā ma duk suna jiransa.
Zgodí se pa, ko se vrne Jezus, sprejme ga ljudstvo; kajti vsi so ga pričakovali.
41 Sai wani mutum mai suna Yayirus, wani mai mulkin majami’a, ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, yana roƙonsa ya zo gidansa,
In glej, pa pride mož, kteremu je bilo ime Jair, (in ta je bil starešina v shajališči, ) in pade Jezusu pred noge, in prosil ga je, naj vnide v hišo njegovo;
42 domin diyarsa ɗaya tak, wadda ta kai shekara goma sha biyu, tana bakin mutuwa. Da Yesu yake kan hanyarsa, taron mutane masu yawa suka yi ta matsa shi a kowane gefe.
Kajti imel je hčer edinico pri dvanajstih letih, in ta je umirala. A ko je šel, stiskalo ga je ljudstvo.
43 A wurin kuwa, akwai wata mace wadda tana da ciwon zubar da jini, har na shekara goma sha biyu, amma babu wanda ya iya warkar da ita.
In žena, ktera je imela krvotok uže dvanajst let, in je bila vse imenje svoje potrošila na zdravnike, ktere ni mogel nobeden uzdraviti.
44 Sai ta zo ta bayansa, ta taɓa bakin rigarsa. Nan da nan, zubar da jininta ya tsaya.
Pristopi od zadi in se dotakne robú obleke njegove; in precej se je ustavil vir krví njene.
45 Yesu ya yi tambaya, “Wa ya taɓa ni?” Bayan kowa ya yi musu, sai Bitrus ya ce, “Ubangiji, ai, mutane da yawa suna matsinka ta kowane gefe.”
Pa reče Jezus: Kdo se me je dotaknil? Ko so se pa vsi odgovarjali, reče Peter in kteri so bili ž njim; Učenik, ljudstvo te gnjete in stiska, pa praviš: Kdo se me je dotaknil?
46 Amma Yesu ya ce, “Wani ya taɓa ni, na san cewa iko ya fita daga wurina.”
Jezus pa reče: Nekdo se me je dotaknil; kajti jaz sem očutil, da je odšla moč od mene.
47 Sai macen, da ta ga ba halin ɓoyewa, sai ta fita, jikinta na rawa, ta fāɗi a gabansa. A gaban dukan mutanen, ta faɗi dalilin da ya sa ta taɓa shi, da yadda ta warke nan take.
Videč pa žena, da se ni prikrila, pristopi drhtajoč, in pade pred-nj, in pové mu pred vsem ljudstvom, za kaj se ga je dotaknila, in kako je ozdravela precej.
48 Sai Yesu ya ce mata, “Diyata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya.”
On jej pa reče: Zaupaj, hčer! vera tvoja ti je pomogla; pojdi v miru.
49 Yayinda Yesu na cikin magana har yanzu, sai ga wani daga gidan Yayirus, mai mulkin majami’ar ya ce, “Kada ka ƙara damun malam, diyarka ta rasu.”
Ko je še govoril, pride nekdo od starešine shajališčnega, govoreč mu: Umrla je hčer tvoja; ne trudi učenika.
50 Da Yesu ya ji wannan, sai ya ce wa Yayirus, “Kada ka ji tsoro, ka gaskata, za a kuma warkar da ita.”
Slišavši pa to Jezus, odgovorí mu, govoreč: Ne boj se! le veruj, in ozdravela bo.
51 Da ya iso gidan Yayirus, sai ya hana kowa yă bi shi cikin ɗakin, sai dai Bitrus, da Yohanna, da Yaƙub, da kuma mahaifin da mahaifiyar.
Ko je pa prišel v hišo, ni dal nikomur vniti, razen Petru in Jakobu in Janezu, in očetu in materi deklice.
52 Ana cikin haka, dukan mutanen kuma sai kuka da makoki suke ta yi, domin yarinyar. Sai Yesu ya ce, “Ka daina yin kuka, ba tă mutu ba, tana barci ne.”
Vsi pa so jokali, in tarnali po njej. On pa reče: Ne jokajte! ni umrla, nego spí.
53 Sai suka yi masa dariya, da yake sun san cewa, ta mutu.
In posmehovali so mu se, vedoč, da je umrla.
54 Amma Yesu ya kama ta a hannu ya ce, “Diyata, tashi.”
On pa izgnavši vse, in prijemši jo za roko, zakliče, govoreč: Deklica, vstani!
55 Ruhunta ya dawo, kuma ta tashi, nan take. Yesu ya ce musu, su ba ta wani abu tă ci.
In vrne se duh nje, in vstala je precej; in ukaže jim, naj jej dadó jesti.
56 Iyayenta suka yi mamaki, amma ya ba su umarni kada su faɗa wa kowa abin da ya faru.
In zavzemeta se roditelja njena; a on jima naročí, naj nikomur ne povesta, kar se je zgodilo.