< Luka 7 >
1 Bayan Yesu ya gama gaya wa mutanen dukan waɗannan abubuwa, sai ya shiga Kafarnahum.
Men da han havde fuldendt alle sine Ord i Folkets Paahør, gik han ind i Kapernaum.
2 A can, akwai wani bawan wani jarumin yana ciwo, yana kuma a bakin mutuwa. Maigidansa kuwa yana sonsa sosai.
Men en Høvedsmands Tjener, som denne holdt meget af, var syg og nær ved at dø.
3 Jarumin sojan ya ji labarin Yesu, sai ya aiki waɗansu dattawan Yahudawa wajensa, yana roƙonsa yă zo yă warkar da bawansa.
Men da han hørte om Jesus, sendte han nogle af Jødernes Ældste til ham og bad ham om, at han vilde komme og helbrede hans Tjener.
4 Da suka isa wurin Yesu, sai suka roƙe shi sosai, suka ce, “Wannan mutum, ai, ya dace a yi masa haka,
Men da de kom til Jesus, bade de ham indtrængende og sagde: „Han er vel værd, at du gør dette for ham;
5 gama yana ƙaunar al’ummarmu ta Yahudawa, har ya gina majami’armu.”
thi han elsker vort Folk, og han har bygget Synagogen for os.”
6 Sai Yesu ya tafi tare da su. Da ya yi kusa da gidan, sai jarumin nan, ya aiki abokai su ce masa, “Ubangiji, kada ka dami kanka, gama ban isa ka shiga gidana ba.
Og Jesus gik med dem. Men da han allerede ikke var langt fra Huset, sendte Høvedsmanden nogle Venner og lod ham sige: „Herre! umag dig ikke; thi jeg er ikke værdig til, at du skal gaa ind under mit Tag.
7 Shi ya sa ban ma ga na isa in zo wurinka ba. Amma ka yi magana kawai, bawana zai warke.
Derfor agtede jeg heller ikke mig selv værdig til at komme til dig; men sig det med et Ord, saa bliver min Dreng helbredet.
8 Gama ni kaina, mutum ne a ƙarƙashin iko, akwai kuma sojoji a ƙarƙashin ikona. Nakan ce wa wannan, ‘Je ka,’ sai yă tafi, ga wani kuma in ce, ‘Zo nan,’ sai yă zo. Nakan kuma ce wa bawana, ‘Yi abu kaza,’ sai yă yi.”
Jeg er jo selv et Menneske, som staar under Øvrighed og har Stridsmænd under mig; og siger jeg til den ene: Gaa! saa gaar han; og til den anden: Kom! saa kommer han; og til min Tjener: Gør dette! saa gør han det.”
9 Da Yesu ya ji haka, sai ya yi mamaki sosai. Ya juya ya wa taron da yake bin sa, “Ina faɗa muku, ban taɓa samun irin bangaskiya mai girma haka ko cikin Isra’ila ba.”
Men da Jesus hørte dette, forundrede han sig over ham; og han vendte sig om og sagde til Skaren, som fulgte ham: „Jeg siger eder, end ikke i Israel har jeg fundet saa stor en Tro.”
10 Sai mutanen da aka aika, suka koma gida, suka tarar bawan ya warke.
Og da de, som vare udsendte, kom tilbage til Huset, fandt de den syge Tjener sund.
11 Ba a daɗe ba, sai Yesu ya tafi wani garin da ake kira Nayin. Almajiransa da taro mai yawa suka tafi tare da shi.
Og det skete Dagen derefter, at han gik til en By, som hed Nain, og der gik mange af hans Disciple og en stor Skare med ham.
12 Da ya yi kusa da ƙofar garin, sai ga wata gawa ana fitowa da ita. Shi ne ɗa kaɗai ga mahaifiyarsa, ita kuma gwauruwa ce. Taro mai yawa daga garin yana tare da ita.
Men da han nærmede sig Byens Port, se, da blev en død baaren ud, som var sin Moders enbaarne Søn, og hun var Enke; og en stor Skare fra Byen gik med hende.
13 Da Ubangiji ya gan ta, sai ya ji tausayinta ya ce, “Kada ki yi kuka.”
Og da Herren saa hende, ynkedes han inderligt over hende og sagde til hende: „Græd ikke!”
14 Yesu ya je ya taɓa akwatin gawar, sai masu ɗaukarsa suka tsaya cik. Sai ya ce, “Saurayi, na ce maka, tashi!”
Og han traadte til og rørte ved Baaren; men de, som bare, stode stille, og han sagde: „Du unge Mand, jeg siger dig, staa op!”
15 Sai mamacin ya tashi zaune, ya fara magana. Yesu kuma ya ba da shi ga mahaifiyarsa.
Og den døde rejste sig op og begyndte at tale; og han gav ham til hans Moder.
16 Sai tsoro ya kama su duka, suka yabi Allah, suna cewa, “Babban annabi ya bayyana a cikinmu. Allah ya zo domin yă taimaki mutanensa.”
Men Frygt betog alle, og de priste Gud og sagde: „Der er en stor Profet oprejst iblandt os, og Gud har besøgt sit Folk.”
17 Wannan labarin game da Yesu, ya bazu ko’ina a Yahudiya da kewayenta.
Og denne Tale om ham kom ud i hele Judæa og i hele det omliggende Land.
18 Almajiran Yohanna suka gaya masa dukan waɗannan abubuwa. Sai ya kira biyu daga cikinsu,
Og Johannes's Disciple fortalte ham om alt dette. Og Johannes kaldte to af sine Disciple til sig
19 ya aike su wurin Ubangiji, su tambaya su ce, “Kai ne wanda zai zo, ko kuma mu saurari wani dabam?”
og sendte dem til Herren og lod sige: „Er du den, som kommer, eller skulle vi vente en anden?”
20 Da mutanen suka iso wurin Yesu, sai suka ce, “Yohanna Mai Baftisma ne ya aike mu wurinka, mu yi tambaya, ‘Ko kai ne wanda zai zo, ko kuma mu saurari wani dabam?’”
Og da Mændene kom til ham, sagde de: „Johannes Døberen har sendt os til dig og lader sige: Er du den, som kommer, eller skulle vi vente en anden?”
21 A daidai lokacin nan, Yesu ya warkar da mutane da yawa masu ciwo, masu cututtuka, da kuma masu mugayen ruhohi. Ya kuma ba makafi da yawa ganin gari.
I den samme Time helbredte han mange for Sygdomme og Plager og onde Aander og skænkede mange blinde Synet.
22 Sai ya amsa wa almajiran Yohanna ya ce, “Ku koma ku faɗa wa Yohanna abin da kuka ji, da abin da kuka gani. Makafi suna ganin gari, guragu suna tafiya, ana warkar da waɗanda suke da kuturta, kurame suna ji, ana tā da matattu, ana kuma yi wa matalauta wa’azin bishara.
Og han svarede og sagde til dem: „Gaar hen, og forkynder Johannes de Ting, som I have set og hørt: Blinde se, lamme gaa, spedalske renses, døve høre, døde staa op, Evangeliet forkyndes for fattige;
23 Mai albarka ne mutumin da bai yi shakkar bangaskiyar da yake da ita a kaina ba.”
og salig er den, som ikke forarges paa mig.”
24 Bayan almajiran Yohanna suka tafi, sai Yesu ya fara yi wa taron magana game da Yohanna ya ce, “Me kuka je kallo a hamada? Ciyawar da iska take kaɗawa ne?
Men da Johannes's Sendebud vare gaaede bort, begyndte han at sige til Skarerne om Johannes: „Hvad gik I ud i Ørkenen at skue? Et Rør, som bevæges hid og did af Vinden?
25 In ba haka ba, to, me kuka je kallo? Mutum mai sanye da tufafi masu kyau ne? A’a, masu sa kayan tsada da suke cikin annashuwa, ai, a fada suke.
Eller hvad gik I ud at se? Et Menneske, iført bløde Klæder? Se, de, som leve i prægtige Klæder og i Vellevned, ere i Kongsgaardene.
26 Amma me kuka je kallo? Annabi? I, ina kuma faɗa muku, ya ma fi annabi.
Eller hvad gik I ud at se? En Profet? Ja, siger jeg eder, endog mere end en Profet!
27 Wannan shi ne wanda aka rubuta game da shi cewa, “‘Zan aiko da ɗan saƙona yă sha gabanka, wanda zai shirya hanya, a gabanka.’
Han er den, om hvem der er skrevet: Se, jeg sender min Engel for dit Ansigt, han skal berede din Vej foran dig.
28 Ina faɗa muku, a cikin duk waɗanda mata suka haifa, ba wanda ya fi Yohanna girma. Duk da haka wanda ya fi ƙasƙanta a Mulkin Allah ya fi shi.”
Jeg siger eder: Iblandt dem, som ere fødte af Kvinder, er ingen større Profet end Johannes; men den mindste i Guds Rige er større end han.
29 (Dukan mutane, har da masu karɓar haraji, da suka ji kalmomin Yesu, sai suka yarda cewa hanyar Allah gaskiya ce, domin Yohanna ne ya yi musu baftisma.
Og hele Folket, som hørte ham, endog Tolderne, gav Gud Ret, idet de bleve døbte med Johannes's Daab.
30 Amma Farisiyawa da masanan dokoki, suka ƙi nufin Allah game da su, domin Yohanna bai yi musu baftisma ba.)
Men Farisæerne og de lovkyndige have foragtet Guds Raad med dem selv, idet de ikke bleve døbte af ham.
31 Yesu ya ci gaba da cewa, “To, da me zan kwatanta mutanen zamanin nan? Kamar me suke?
Ved hvem skal jeg da ligne denne Slægts Mennesker? og hvem ligne de?
32 Suna kama da yaran da suke zama a bakin kasuwa, suna kiran juna, suna cewa, “‘Mun busa muku sarewa, amma ba ku yi rawa ba, Mun kuma yi muku waƙar makoki, ba ku kuma yi kuka ba.’
De ligne Børn, som sidde paa Torvet og raabe til hverandre og sige: Vi blæste paa Fløjte for eder, og I dansede ikke, vi sang Klagesange for eder, og I græd ikke.
33 Gama Yohanna Mai Baftisma ya zo, ba ya cin burodi, ba ya shan ruwan inabi, sai kuka ce, ‘Ai, yana da aljani.’
Thi Johannes Døberen kom, som hverken spiste Brød eller drak Vin, og I sige: Han er besat.
34 Ɗan Mutum ya zo yana ci, yana sha, sai kuka ce, ‘Ga mai yawan ci, mashayi, da kuma abokin masu karɓar haraji da masu zunubi.’
Menneskesønnen kom, som spiser og drikker, og I sige: Se, en Fraadser og en Vindranker, Tolderes og Synderes Ven!
35 Amma akan tabbatar da hikima ta gaskiya bisa ga dukan’ya’yanta.”
Dog Visdommen er retfærdiggjort ved alle sine Børn.”
36 To, ana nan, sai ɗaya daga cikin Farisiyawa ya gayyaci Yesu cin abincin yamma a gidansa, ya kuwa tafi gidan Bafarisiyen, ya zauna a tebur.
Men en af Farisæerne bad ham om, at han vilde spise med ham; og han gik ind i Farisæerens Hus og satte sig til Bords.
37 Da wata mace wadda ta yi rayuwar zunubi a wannan gari ta ji Yesu yana cin abinci a gidan Bafarisiyen, sai ta kawo ɗan tulun turaren alabasta,
Og se, der var en Kvinde, som var en Synderinde i Byen; da hun fik at vide, at han sad til Bords i Farisæerens Hus, kom hun med en Alabastkrukke med Salve;
38 ta kuma tsaya daga bayansa, wajen ƙafafunsa tana kuka, sai hawayenta sun fara zuba a ƙafafunsa. Sai ta goge su da gashin kanta, ta sumbace su, sa’an nan ta shafa musu turare.
og hun stillede sig bag ved ham, ved hans Fødder og græd og begyndte at væde hans Fødder med sine Taarer og aftørrede dem med sit Hovedhaar og kyssede hans Fødder og salvede dem med Salven.
39 Da Bafarisiyen da ya gayyace shi, ya ga wannan, sai ya ce a ransa, “Da mutumin nan annabi ne, da ya san ko wace ce take taɓansa, da kuma irin macen da take, cewa mai zunubi ce.”
Men da Farisæeren, som havde indbudt ham, saa det, sagde han ved sig selv: „Dersom denne var en Profet, vidste han, hvem og hvordan en Kvinde denne er, som rører ved ham, at hun er en Synderinde.”
40 Sai Yesu ya ce masa, “Siman, ina da abin da zan faɗa maka.” Shi kuwa ya ce, “Malam sai ka faɗa.”
Og Jesus tog til Orde og sagde til ham: „Simon! jeg har noget at sige dig.” Men han siger: „Mester, sig frem!”
41 Yesu ya ce, “An yi waɗansu mutum biyu da suke riƙe bashin mai ba da rance. Ana bin guda dinari ɗari biyar, ɗayan kuma hamsin.
„En Mand, som udlaante Penge, havde to Skyldnere; den ene var fem Hundrede Denarer skyldig, men den anden halvtredsindstyve.
42 Dukan biyun suka gagara biyansa, sai ya yafe musu. To, a ganinka, wa zai fi ƙaunar mutumin nan?”
Da de ikke havde noget at betale med, eftergav han dem det begge. Hvem af dem vil nu elske ham mest?”
43 Siman ya amsa ya ce, “A ganina, wanda aka yafe wa mai yawa ne.” Sai Yesu ya ce, “Ka faɗa daidai.”
Simon svarede og sagde: „Jeg holder for, den, hvem han eftergav mest?” Men han sagde til ham: „Du dømte ret.”
44 Sai ya juya wajen macen, ya ce wa Siman, “Ka ga macen nan? Na shigo gidanka, ba ka ba ni ruwa don ƙafafuna ba, amma ta wanke ƙafafuna da hawayenta, ta kuma goge su da gashin kanta.
Og han vendte sig imod Kvinden og sagde til Simon: „Ser du denne Kvinde? Jeg kom ind i dit Hus; du gav mig ikke Vand til mine Fødder; men hun vædede mine Fødder med sine Taarer og aftørrede dem med sit Haar.
45 Ba ka yi mini sumba ba, amma tun shigowata a nan, macen nan ba tă daina sumbar ƙafafuna ba.
Du gav mig intet Kys; men hun ophørte ikke med at kysse mine Fødder, fra jeg kom herind.
46 Ba ka shafa mai a kaina ba, amma ta zubo turare a ƙafafuna.
Du salvede ikke mit Hoved med Olie; men hun salvede mine Fødder med Salve.
47 “Saboda haka ina gaya maka, zunubanta masu yawa, an gafarta mata, gama ƙaunarta mai yawa ce. Amma wanda aka gafarta wa kaɗan kuwa, yakan nuna ƙauna kaɗan.”
Derfor siger jeg dig: Hendes mange Synder ere hende forladte, eftersom hun elskede meget; men den, hvem lidet forlades, elsker lidet.”
48 Sai Yesu ya ce mata, “An gafarta miki zunubanki.”
Men han sagde til hende: „Dine Synder ere forladte!”
49 Sauran baƙin suka fara ce wa juna, “Wane ne wannan, wanda har yake gafarta zunubai?”
Og de, som sade til Bords med ham, begyndte at sige ved sig selv: „Hvem er denne, som endog forlader Synder?”
50 Yesu ya ce wa macen, “Bangaskiyarki ta cece ki, ki sauka lafiya.”
Men han sagde til Kvinden: „Din Tro har frelst dig, gaa bort med Fred!”