< Luka 7 >

1 Bayan Yesu ya gama gaya wa mutanen dukan waɗannan abubuwa, sai ya shiga Kafarnahum.
耶稣向民众讲完这一切,就开始向迦百农走去。
2 A can, akwai wani bawan wani jarumin yana ciwo, yana kuma a bakin mutuwa. Maigidansa kuwa yana sonsa sosai.
那里的一位百夫长有一名十分器重的仆人,但这仆人快要死了。
3 Jarumin sojan ya ji labarin Yesu, sai ya aiki waɗansu dattawan Yahudawa wajensa, yana roƙonsa yă zo yă warkar da bawansa.
百夫长听见耶稣的事,就派来几位犹太人长老过来,求他去医治他的奴仆。
4 Da suka isa wurin Yesu, sai suka roƙe shi sosai, suka ce, “Wannan mutum, ai, ya dace a yi masa haka,
长老们就来见耶稣,恳求他说:“请过来为他做这件事吧,因为他值得你的帮助。
5 gama yana ƙaunar al’ummarmu ta Yahudawa, har ya gina majami’armu.”
因为他爱我们的人民,给我们建造会堂。”
6 Sai Yesu ya tafi tare da su. Da ya yi kusa da gidan, sai jarumin nan, ya aiki abokai su ce masa, “Ubangiji, kada ka dami kanka, gama ban isa ka shiga gidana ba.
耶稣就和他们一同前去。在距离百夫长住宅不远的地方,百夫长派几个朋友来说:“主啊,有劳你大驾光临,实在不敢当,
7 Shi ya sa ban ma ga na isa in zo wurinka ba. Amma ka yi magana kawai, bawana zai warke.
我觉得自己实在没有资格去见你,但只要你说一句话,我的仆人就能治愈了。
8 Gama ni kaina, mutum ne a ƙarƙashin iko, akwai kuma sojoji a ƙarƙashin ikona. Nakan ce wa wannan, ‘Je ka,’ sai yă tafi, ga wani kuma in ce, ‘Zo nan,’ sai yă zo. Nakan kuma ce wa bawana, ‘Yi abu kaza,’ sai yă yi.”
我既听命于自己的长官,手下也有士兵。如果我对士兵说‘去吧!’他就会去;对另一个人说‘来吧!’他就会来;我对仆人说‘做这个吧!’他就会做。”
9 Da Yesu ya ji haka, sai ya yi mamaki sosai. Ya juya ya wa taron da yake bin sa, “Ina faɗa muku, ban taɓa samun irin bangaskiya mai girma haka ko cikin Isra’ila ba.”
耶稣听见这些话,很是惊讶,转身对跟随的众人说:“告诉你们,我在以色列从未见过如此坚定的信心。”
10 Sai mutanen da aka aika, suka koma gida, suka tarar bawan ya warke.
百夫长的朋友回到家里,发现那奴仆已经痊愈了。
11 Ba a daɗe ba, sai Yesu ya tafi wani garin da ake kira Nayin. Almajiransa da taro mai yawa suka tafi tare da shi.
很快,耶稣开始向拿因城走去,身边跟着他的门徒和一大群民众。
12 Da ya yi kusa da ƙofar garin, sai ga wata gawa ana fitowa da ita. Shi ne ɗa kaɗai ga mahaifiyarsa, ita kuma gwauruwa ce. Taro mai yawa daga garin yana tare da ita.
他走近城门的时候,看到另一条路上有个送葬的队伍,那是一家的独子,母亲是个寡妇。城里有一大群人陪着她。
13 Da Ubangiji ya gan ta, sai ya ji tausayinta ya ce, “Kada ki yi kuka.”
主看见她便心生怜悯,对她说:“不要哭!”
14 Yesu ya je ya taɓa akwatin gawar, sai masu ɗaukarsa suka tsaya cik. Sai ya ce, “Saurayi, na ce maka, tashi!”
然后耶稣上前按着棺材,抬棺人站住。 耶稣说:“年轻人,我要对你说,起来吧!”
15 Sai mamacin ya tashi zaune, ya fara magana. Yesu kuma ya ba da shi ga mahaifiyarsa.
那死去之人就坐起来,开口说话,耶稣把他交给他母亲。
16 Sai tsoro ya kama su duka, suka yabi Allah, suna cewa, “Babban annabi ya bayyana a cikinmu. Allah ya zo domin yă taimaki mutanensa.”
众人都感到敬畏万分,纷纷颂赞上帝:“我们中间出现了伟大的先知!”又说:“上帝眷顾他的子民了!”
17 Wannan labarin game da Yesu, ya bazu ko’ina a Yahudiya da kewayenta.
关于耶稣的消息传遍了犹太和周围各地。
18 Almajiran Yohanna suka gaya masa dukan waɗannan abubuwa. Sai ya kira biyu daga cikinsu,
约翰的门徒把这一切都告诉约翰,约翰叫来他的两名门徒,
19 ya aike su wurin Ubangiji, su tambaya su ce, “Kai ne wanda zai zo, ko kuma mu saurari wani dabam?”
派他们去主那里,说:“你就是我们一直期待的人?还是我们需要继续等待其他人?”
20 Da mutanen suka iso wurin Yesu, sai suka ce, “Yohanna Mai Baftisma ne ya aike mu wurinka, mu yi tambaya, ‘Ko kai ne wanda zai zo, ko kuma mu saurari wani dabam?’”
两人来到耶稣跟前,说:“施洗约翰派我们来问你,‘你就是我们一直期待的人?还是我们需要继续等待其他人?’”
21 A daidai lokacin nan, Yesu ya warkar da mutane da yawa masu ciwo, masu cututtuka, da kuma masu mugayen ruhohi. Ya kuma ba makafi da yawa ganin gari.
耶稣这时正在治愈众多患病、遭难、恶鬼附体之人,让盲人可以看到。
22 Sai ya amsa wa almajiran Yohanna ya ce, “Ku koma ku faɗa wa Yohanna abin da kuka ji, da abin da kuka gani. Makafi suna ganin gari, guragu suna tafiya, ana warkar da waɗanda suke da kuturta, kurame suna ji, ana tā da matattu, ana kuma yi wa matalauta wa’azin bishara.
耶稣回答约翰的门徒:“你们回去把所见所闻都告诉约翰。盲人可以看见,跛人可以走路,麻风患者被治愈,聋人可以听见,死人复活,穷人听到了福音。
23 Mai albarka ne mutumin da bai yi shakkar bangaskiyar da yake da ita a kaina ba.”
那些不会因我而感到冒犯的人,有福了。”
24 Bayan almajiran Yohanna suka tafi, sai Yesu ya fara yi wa taron magana game da Yohanna ya ce, “Me kuka je kallo a hamada? Ciyawar da iska take kaɗawa ne?
约翰派来的人走了以后,耶稣开始对众人说:“关于约翰,你们到荒野去寻找他时,希望看到什么?风吹动的芦苇吗?
25 In ba haka ba, to, me kuka je kallo? Mutum mai sanye da tufafi masu kyau ne? A’a, masu sa kayan tsada da suke cikin annashuwa, ai, a fada suke.
身穿华服之人吗?不,那些衣着华丽、生活奢侈的人都生活在宫殿中。
26 Amma me kuka je kallo? Annabi? I, ina kuma faɗa muku, ya ma fi annabi.
你们是在寻找先知吗?是的,约翰是先知。但我要说的是,他比先知重要得多了。
27 Wannan shi ne wanda aka rubuta game da shi cewa, “‘Zan aiko da ɗan saƙona yă sha gabanka, wanda zai shirya hanya, a gabanka.’
经文中记着:‘看啊,我派遣使者先你一步,预备你的道路’,说的就是他。
28 Ina faɗa muku, a cikin duk waɗanda mata suka haifa, ba wanda ya fi Yohanna girma. Duk da haka wanda ya fi ƙasƙanta a Mulkin Allah ya fi shi.”
我告诉你们,女人所诞下的人类中,没有谁比约翰更伟大,但他在上帝之国中却是最不重要的那一个!”
29 (Dukan mutane, har da masu karɓar haraji, da suka ji kalmomin Yesu, sai suka yarda cewa hanyar Allah gaskiya ce, domin Yohanna ne ya yi musu baftisma.
经过约翰施洗的众人,甚至包括税吏,听到此言便纷纷决定追随上帝的善意正道。
30 Amma Farisiyawa da masanan dokoki, suka ƙi nufin Allah game da su, domin Yohanna bai yi musu baftisma ba.)
但法利赛人和研究法律的专家未受过约翰的洗礼,便拒绝上帝对他们的美意。
31 Yesu ya ci gaba da cewa, “To, da me zan kwatanta mutanen zamanin nan? Kamar me suke?
耶稣又说:“这个世界的人可以比作什么呢?他们像什么呢?
32 Suna kama da yaran da suke zama a bakin kasuwa, suna kiran juna, suna cewa, “‘Mun busa muku sarewa, amma ba ku yi rawa ba, Mun kuma yi muku waƙar makoki, ba ku kuma yi kuka ba.’
他们就像小孩子坐在巿中心,对彼此说:‘我们给你们吹笛子,你们却不跳舞,我们唱哀歌,你们也不痛哭。’
33 Gama Yohanna Mai Baftisma ya zo, ba ya cin burodi, ba ya shan ruwan inabi, sai kuka ce, ‘Ai, yana da aljani.’
施洗约翰来了,不吃饭,不喝酒,你们就说他是恶魔附体。
34 Ɗan Mutum ya zo yana ci, yana sha, sai kuka ce, ‘Ga mai yawan ci, mashayi, da kuma abokin masu karɓar haraji da masu zunubi.’
现在人子来了,看他吃喝你们又说:‘你看,这人又贪吃,又贪杯,还与税吏和罪人为伍。’
35 Amma akan tabbatar da hikima ta gaskiya bisa ga dukan’ya’yanta.”
但上帝的智慧之道,已被他的所有追随者所证实!”
36 To, ana nan, sai ɗaya daga cikin Farisiyawa ya gayyaci Yesu cin abincin yamma a gidansa, ya kuwa tafi gidan Bafarisiyen, ya zauna a tebur.
有一个法利赛人请耶稣同他一起用餐,于是他就到那位法利赛人家中赴宴。
37 Da wata mace wadda ta yi rayuwar zunubi a wannan gari ta ji Yesu yana cin abinci a gidan Bafarisiyen, sai ta kawo ɗan tulun turaren alabasta,
城里有一个女人,是个罪人。得知他在法利赛人家里吃饭,就拿着一瓶香膏来到这里。
38 ta kuma tsaya daga bayansa, wajen ƙafafunsa tana kuka, sai hawayenta sun fara zuba a ƙafafunsa. Sai ta goge su da gashin kanta, ta sumbace su, sa’an nan ta shafa musu turare.
她跪在耶稣身边,眼泪沾湿了他的脚。于是她用自己的头发把泪水擦干,然后亲吻他的脚,抹上香膏。
39 Da Bafarisiyen da ya gayyace shi, ya ga wannan, sai ya ce a ransa, “Da mutumin nan annabi ne, da ya san ko wace ce take taɓansa, da kuma irin macen da take, cewa mai zunubi ce.”
请耶稣吃饭的法利赛人看见她,心想:“这人若真的是先知,必定知道是谁在触摸他。这是怎样的女人,她是个罪人!”
40 Sai Yesu ya ce masa, “Siman, ina da abin da zan faɗa maka.” Shi kuwa ya ce, “Malam sai ka faɗa.”
于是耶稣开口说:“西门,我有话要对你说。”他说:“老师,请讲。”
41 Yesu ya ce, “An yi waɗansu mutum biyu da suke riƙe bashin mai ba da rance. Ana bin guda dinari ɗari biyar, ɗayan kuma hamsin.
耶稣说:“有两个人欠了一个债主的钱,一人欠 500 银币,一人欠 50 银币。
42 Dukan biyun suka gagara biyansa, sai ya yafe musu. To, a ganinka, wa zai fi ƙaunar mutumin nan?”
他们都无力偿还,于是债主就免了两人的债务。这两个人哪一个人会更爱他?”
43 Siman ya amsa ya ce, “A ganina, wanda aka yafe wa mai yawa ne.” Sai Yesu ya ce, “Ka faɗa daidai.”
西门回答:“我想是那个欠债多的人会更爱他。”耶稣说:“你说对了。”
44 Sai ya juya wajen macen, ya ce wa Siman, “Ka ga macen nan? Na shigo gidanka, ba ka ba ni ruwa don ƙafafuna ba, amma ta wanke ƙafafuna da hawayenta, ta kuma goge su da gashin kanta.
于是他转身向着那女人,对西门说:“你看到这女人吗?我走进你家,你没有给我水洗脚,但她却用眼泪湿了我的脚,用头发擦干。
45 Ba ka yi mini sumba ba, amma tun shigowata a nan, macen nan ba tă daina sumbar ƙafafuna ba.
你没有亲吻我,但这女人自我进来,就一直在亲吻我的脚。
46 Ba ka shafa mai a kaina ba, amma ta zubo turare a ƙafafuna.
你没有在我的头上涂抹香膏,但这女人却用香膏抹我的脚。
47 “Saboda haka ina gaya maka, zunubanta masu yawa, an gafarta mata, gama ƙaunarta mai yawa ce. Amma wanda aka gafarta wa kaɗan kuwa, yakan nuna ƙauna kaɗan.”
所以我告诉你,因为她的很多罪都被赦免了,所以她心中的爱多。如果被赦免的少,心中爱的也少。”
48 Sai Yesu ya ce mata, “An gafarta miki zunubanki.”
然后耶稣对女人说:“你的罪被赦免了。”
49 Sauran baƙin suka fara ce wa juna, “Wane ne wannan, wanda har yake gafarta zunubai?”
一同进餐之人心里说:“这是谁啊?竟然可以宽恕罪过?”
50 Yesu ya ce wa macen, “Bangaskiyarki ta cece ki, ki sauka lafiya.”
耶稣对那女人说:“你的信任已经拯救了你,安心地去吧。”

< Luka 7 >