< Luka 6 >

1 A wata ranar Asabbaci, Yesu yana bi ta gonakin hatsi, sai almajiran suka fara kakkarya kan hatsi suna murjewa a hannuwansu suna ci.
Och det begaf sig på en Eftersabbath, att han gick igenom säd; och hans Lärjungar ryckte upp ax, och gnuggade sönder med händerna, och åto.
2 Sai waɗansu Farisiyawa suka ce, “Me ya sa kuke yin abin da doka ta hana yi a ranar Asabbaci?”
Då sade somlige af de Phariseer till dem: Hvi gören I det som icke är lofligit göra om Sabbatherna?
3 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ashe, ba ku taɓa karanta abin da Dawuda ya yi, sa’ad da shi da abokan tafiyarsa suka ji yunwa ba?
Svarade Jesus, och sade till dem: Hafven I icke läsit hvad David gjorde, då han hungrade, och de med honom voro?
4 Ya shiga gidan Allah, ya ɗauki keɓaɓɓen burodi, sa’an nan ya ci abin da firistoci kaɗai sukan ci bisa ga doka. Ya kuma ba wa abokan tafiyarsa?”
Huru han gick in i Guds hus, och tog skådobröden, och åt, och gaf desslikes dem som med honom voro; hvilket ingom lofligit var att äta, utan allenast Prestomen.
5 Sai Yesu ya ce musu, “Ai, Ɗan Mutum ne Ubangijin Asabbaci.”
Och sade han till dem: Menniskones Son är en Herre, desslikes ock öfver Sabbathen.
6 A wata ranar Asabbaci kuma, Yesu ya shiga majami’a yana koyarwa. To, a nan kuwa akwai wani mutumin da hannun damansa ya shanye.
Och det begaf sig på en annan Sabbath, att han gick in uti Synagogon, och lärde; och der var en menniska, hvilkens högra hand var borttvinad.
7 Farisiyawa da malaman dokoki suka zuba wa Yesu ido, su ga ko zai warkar a ranar Asabbaci, don su sami dalilin zarginsa.
Och de Skriftlärde och Phariseer vaktade på honom, om han någon helbregda gjorde på Sabbathen, att de måtte finna något, der de kunde anklagan före.
8 Amma Yesu ya san abin da suke tunani. Sai ya ce wa mutumin mai shanyayyen hannun, “Tashi ka tsaya a gaban kowa.” Sai ya tashi ya tsaya.
Men han förstod deras tankar, och sade till menniskona, som den tvinada handen hade: Statt upp, och gack fram. Han stod upp, och gick fram.
9 Yesu ya ce musu, “Ina tambayarku, me ya kamata a yi bisa ga doka, a ranar Asabbaci, a aikata alheri ko a aikata mugunta, a ceci rai, ko a hallaka shi?”
Då sade Jesus till dem: Jag skall spörja eder: Må man göra väl om Sabbatherna, eller göra illa; hjelpa lifvet, eller förspillat?
10 Sai ya kalle su duka, sa’an nan ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Sai ya miƙe, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye.
Och han såg sig om på dem alla, och sade till menniskona: Räck ut dina hand. Han ock så gjorde. Och hans hand vardt honom färdig, såsom den andra.
11 Amma Farisiyawa da malaman Doka suka fusata, suka fara tattauna da junansu a kan abin da za su yi wa Yesu.
Men de vordo ursinnige, och talades vid emellan sig, hvad de skulle göra åt Jesus.
12 Wata rana, a cikin kwanakin nan, Yesu ya je wani dutse domin yă yi addu’a, ya kuma kwana yana addu’a ga Allah.
Så hände det uti de dagar, att han utgick uppå ett berg till att bedja; och blef der öfver nattena i bönen till Gud.
13 Da gari ya waye, sai ya kira almajiransa zuwa wurinsa, ya zaɓi guda goma sha biyu daga cikinsu, waɗanda ya kira su, Manzanni.
Och då dager vardt, kallade han sina Lärjungar; och utvalde tolf af dem, hvilka han ock kallade Apostlar.
14 Siman (wanda ya kira Bitrus), ɗan’uwansa Andarawus, Yaƙub, Yohanna, Filibus, Bartolomeyu,
Simon, den han ock kallade Petrus, och Andreas, hans broder, Jacobus och Johannes, Philippus och Bartholomeus,
15 Mattiyu, Toma, Yaƙub ɗan Alfayus, Siman wanda ake kira Zilot,
Mattheus och Thomas, Jacobus, Alphei son, och Simon, som kallas Zelotes,
16 Yahuda ɗan Yaƙub, da kuma Yahuda Iskariyot, wanda ya bashe Yesu.
Och Judas, Jacobs ( son ), och Judas Ischariothes, den ock förrädaren var.
17 Sai ya sauko tare da su, ya tsaya a wani fili. A can, akwai taro mai yawa na almajiransa, da kuma mutane masu yawan gaske daga ko’ina a Yahudiya, Urushalima da kuma Taya da Sidon da suke bakin teku,
Och han gick neder med dem, och stod på en plats i markene, och hele hopen af hans Lärjungar, och ganska mycket folk utaf allt Judiska landet, och Jerusalem, och ifrå Tyrus och Sidon, som vid hafvet ligga;
18 waɗanda suka zo domin su ji shi, a kuma warkar da cututtukansu. Waɗanda suke fama da mugayen ruhohi kuwa aka warkar da su.
Hvilke komne voro, på det de ville höra honom, och varda botade af sina sjukdomar. Och de, som qvalde voro af de orena andar, vordo helbregda.
19 Kuma dukan mutane suka yi ƙoƙari su taɓa shi, domin iko yana fitowa daga gare shi, ya kuwa warkar da su duka.
Och allt folket for efter att taga på honom; ty af honom gick kraft, som alla botade.
20 Da ya dubi almajiransa, sai ya ce, “Masu albarka ne ku da kuke matalauta, gama mulkin Allah naku ne.
Och han lyfte upp sin ögon öfver sina Lärjungar, och sade: Salige ären I fattige; ty Guds rike hörer eder till.
21 Masu albarka ne ku da kuke jin yunwa yanzu, gama za ku ƙoshi. Masu albarka ne ku da kuke kuka yanzu, gama za ku yi dariya.
Salige ären I, som nu hungren; ty I skolen blifva mättade. Salige ären I, som nu gråten; ty I skolen le.
22 Masu albarka ne sa’ad da mutane suka ƙi ku, suka ware ku, suka zage ku, suna ce da ku mugaye, saboda Ɗan Mutum.
Salige varden I, då menniskorna hata eder, och afskilja eder, och banna eder, och bortkasta edart namn, såsom det ondt vore, för menniskones Sons skull.
23 “Ku yi farin ciki a wannan rana, ku kuma yi tsalle don murna, saboda ladarku yana da yawa a sama. Gama haka kakanninsu suka yi wa annabawa.
Glädjens och fröjdens på den dagen; ty si, edor lön är mycken i himmelen; sammalunda hafva deras fäder ock gjort Prophetomen.
24 “Amma kaitonku da kuke da arziki, gama kun riga kun sami ta’aziyyarku.
Men ve eder, som rike ären; ty I hafven edar hugnad.
25 Kaitonku da kuke ƙosassu yanzu, gama za ku zauna da yunwa. Kaitonku da kuke dariya yanzu, gama za ku yi makoki da kuka.
Ve eder, som mätte ären; ty I skolen hungra. Ve eder, som nu len; ty I skolen gråta och sörja.
26 Kaitonku sa’ad da dukan mutane suna magana mai kyau a kanku, gama haka kakanninsu suka yi da annabawan ƙarya.
Ve eder, då alla menniskor lofva eder; ty sammalunda hafva ock deras fäder gjort dem falska Prophetomen.
27 “Amma ina faɗa muku, ku da kuke ji na, ku ƙaunaci abokan gābanku, ku yi wa masu ƙinku alheri.
Men eder, som hören, säger jag: Älsker edra ovänner; görer dem godt, som hata eder;
28 Ku albarkaci waɗanda suke la’anta ku, ku kuma yi wa waɗanda suke wulaƙanta ku addu’a.
Välsigner dem som eder banna, och beder för dem som eder orätt göra.
29 In wani ya mare ka a wannan kumatu, juya masa ɗayan ma, in wani ya ƙwace maka babban riga, kada ma ka hana masa’yar cikin ma.
Den dig slår på det ena kindbenet, dem håll ock det andra till; och den dig tager mantelen ifrå, honom förhåll icke heller kjortelen.
30 Duk wanda ya roƙe ka abu, ka ba shi. In kuma wani ya yi maka ƙwace, kada ka nema yă mayar maka.
Hvarjom och enom, som något begärar af dig, honom gif; och af den, som dina ting tager ifrå dig, beds intet igen.
31 Ka yi wa waɗansu abin da kai kake so su yi maka.
Och såsom I viljen att menniskorna skola göra eder, görer ock I dem sammalunda.
32 “In kana ƙaunar masu ƙaunarka ne kawai, ina ribar wannan? Ko masu zunubi ma suna ƙaunar waɗanda suke ƙaunarsu.
Och om I älsken dem, som eder älska, hvad tack hafven I derföre? Ty syndarena älska ock dem, af hvilka de älskade varda.
33 In kuma kana yin alheri ga masu yi maka ne kaɗai, ina ribar wannan? Ko masu zunubi ma suna yin haka.
Och om I gören dem godt, som eder godt göra, hvad tack hafven I derföre? Ty syndarena göra det ock.
34 In kana ba da bashi ga mutanen da za su iya biyan ka ne kawai, ina ribar wannan? Ko masu zunubi ma, suna ba da bashi ga masu zunubi, da fata za a biya su tsab.
Och om I lånen dem, der I hoppens få något igen, hvad tack hafven I derföre? Ty syndarena låna ock syndarom, på det de skola få lika igen.
35 Amma, ku ƙaunaci abokan gābanku, ku kuma yi musu alheri, ku ba su bashi, ba da sa zuciya sai an biya ku ba. Ta yin haka ne kawai, za ku sami lada mai yawa, ku kuma zama’ya’yan Mafi Ɗaukaka, gama shi mai alheri ne ga marasa godiya da mugaye.
Utan heldre älsker edra ovänner, och görer väl, och låner, förhoppandes der intet af; och edor lön skall vara mycken, och I skolen vara dens Högstas barn; ty han är mild emot de otacksamma och onda.
36 Ku zama masu jinƙai, kamar yadda Ubanku mai jinƙai ne.
Varer fördenskull barmhertige, såsom edar Fader ock barmhertig är.
37 “Kada ku ɗora wa wani, ku ma ba za a ɗora muku ba. Kada ku yanke wa wani hukunci, ku ma ba za a yanke muku ba. Ku gafarta, ku ma za a gafarta muku.
Dömer icke så varden I icke dömde; fördömer icke, så varden I icke fördömde; förlåter, så varder eder förlåtet.
38 Ku bayar, ku ma sai a ba ku mudu a cike, a danƙare, har yă yi tozo, yana zuba, za a juye muku a hannun riga. Mudun da kuka auna da shi, da shi za a auna muku.”
Gifver, så varder eder gifvet; ett godt mått, väl stoppadt, skakadt och öfverflödande, skall man gifva uti edart sköt; ty med samma mått, som I mäten, skola andre mäta eder.
39 Ya kuma faɗa musu wannan misali cewa, “Makaho yana iya jagoran makaho ne? Ba sai dukansu biyu su fāɗa a rami ba?
Och han sade till dem en liknelse: Kan ock en blinder leda en blindan? Falla de icke både i gropena?
40 Ɗalibi bai fi malaminsa ba, sai dai kowane ɗalibi wanda ya sami cikakkiyar koyarwa, zai zama kamar malaminsa.
Lärjungen är icke öfver sin Mästare; men hvar och en är fullkommen, då han är såsom hans Mästare.
41 “Don me kake duban ɗan tsinke da yake idon ɗan’uwanka, amma ba ka kula da gungumen da yake a naka ido ba?
Hvad ser du ett grand uti dins broders öga; men en bjelka uti ditt eget öga varder du intet varse?
42 Yaya za ka ce wa ɗan’uwanka, ‘Ɗan’uwa, bari in cire maka ɗan tsinke da yake idonka,’ alhali kuwa, kai kanka ka kāsa ganin gungumen da yake a naka ido? Kai munafuki! Ka fara cire gungumen daga idonka, sa’an nan za ka iya gani sosai, ka kuma cire ɗan tsinken da yake a idon ɗan’uwanka.”
Eller huru kan du säga till din broder: Broder, håll, jag vill borttaga grandet, som uti ditt öga är; och du ser icke sjelf bjelkan uti ditt öga? Du skrymtare, tag först bort bjelkan utu ditt öga, och sedan se till att du kan uttaga grandet, som är i dins broders öga.
43 “Ba itace mai kyau da yake ba da munanan’ya’ya. Mummunan itace kuma ba ya ba da’ya’ya masu kyau.
Ty det är icke godt trä, som gör onda frukt; ej heller ondt trä, som gör goda frukt.
44 Kowane itace da irin’ya’yansa ne ake saninsa. Mutane ba sa tsinke’ya’yan ɓaure daga ƙaya, ko kuwa’ya’yan inabi daga sarƙaƙƙiya.
Ty hvart och ett trä varder kändt af sine frukt; ty icke hemtar man heller fikon af törne; ej heller hemtar man vinbär af tistelen.
45 Mutumin nagari yakan nuna abubuwa nagari daga cikin nagarta da yake a ɓoye a zuciyarsa, mugun mutum kuwa yakan nuna mugayen abubuwa daga muguntar da take a ɓoye a zuciyarsa. Gama baki yakan faɗa abin da ya cika zuciya ne.”
En god menniska bär godt fram utaf sins hjertas goda fatabur, och en ond menniska bär ondt fram utaf sins hjertas onda fatabur; ty deraf hjertat fullt är, det talar munnen af.
46 “Don me kuke ce da ni, ‘Ubangiji, Ubangiji,’ amma ba kwa yin abin da na faɗa?
Hvad kallen I mig Herra, Herra; och gören dock icke hvad jag säger eder?
47 Zan nuna muku kwatancin mutumin da yakan zo wurina, yă ji kalmomina, yă kuma aikata.
Hvilken som kommer till mig, och hörer min ord, och gör derefter, jag vill låta eder se, hvem han lik är.
48 Yana kama da mutumin da ya gina gida, wanda ya haƙa ƙasa da zurfi, sa’an nan ya kafa tushen ginin a kan dutse. Da ambaliyar ruwa ta taso, ƙarfin ruwa kuwa ya buga gidan, wannan bai jijjiga shi ba, domin an yi masa tushen gini na ainihi.
Han är lik enom man, som bygger ett hus; hvilken grof djupt, och lade grundvalen på hälleberget; då floden kom, strömmade hon in på huset, och kunde dock intet röra det; ty det var grundadt på hälleberget.
49 Amma wanda yakan ji kalmomina, ba ya kuma aikata su, yana kama da mutumin da ya gina gida a ƙasa, ba tare da ya kafa tushen gini ba. A sa’ad da ƙarfin ruwa ya buga gidan, sai gidan yă rushe, mummunar rushewa kuwa.”
Men den der hörer, och icke gör, han är lik enom man, som byggde sitt hus på jordena, utan grundval; der strömmade floden in på, och straxt föll det; och dess hus fall var stort.

< Luka 6 >