< Luka 6 >

1 A wata ranar Asabbaci, Yesu yana bi ta gonakin hatsi, sai almajiran suka fara kakkarya kan hatsi suna murjewa a hannuwansu suna ci.
And it came to pass on the second sabbath after the first, that he was going through grain-fields; and his disciples plucked the ears of grain, and ate them, rubbing them with their hands.
2 Sai waɗansu Farisiyawa suka ce, “Me ya sa kuke yin abin da doka ta hana yi a ranar Asabbaci?”
And some of the Pharisees said, Why are ye doing that which it is not lawful to do on the sabbath?
3 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ashe, ba ku taɓa karanta abin da Dawuda ya yi, sa’ad da shi da abokan tafiyarsa suka ji yunwa ba?
And Jesus answering them, said, Have ye not even read what David did, when he was himself hungry, and they who were with him?
4 Ya shiga gidan Allah, ya ɗauki keɓaɓɓen burodi, sa’an nan ya ci abin da firistoci kaɗai sukan ci bisa ga doka. Ya kuma ba wa abokan tafiyarsa?”
how he went into the house of God, and took and ate the show-bread, and gave it also to those who were with him, which it is not lawful for any to eat but the priests alone?
5 Sai Yesu ya ce musu, “Ai, Ɗan Mutum ne Ubangijin Asabbaci.”
And he said to them, The Son of man is lord even of the sabbath.
6 A wata ranar Asabbaci kuma, Yesu ya shiga majami’a yana koyarwa. To, a nan kuwa akwai wani mutumin da hannun damansa ya shanye.
And it came to pass on another sabbath, that he entered into the synagogue, and taught; and there was a man there whose right hand was withered.
7 Farisiyawa da malaman dokoki suka zuba wa Yesu ido, su ga ko zai warkar a ranar Asabbaci, don su sami dalilin zarginsa.
And the scribes and the Pharisees were watching whether he would heal on the sabbath, that they might find an accusation against him.
8 Amma Yesu ya san abin da suke tunani. Sai ya ce wa mutumin mai shanyayyen hannun, “Tashi ka tsaya a gaban kowa.” Sai ya tashi ya tsaya.
But he knew their thoughts; and he said to the man having the withered hand, Rise, and stand up in the midst. And he arose, and stood up.
9 Yesu ya ce musu, “Ina tambayarku, me ya kamata a yi bisa ga doka, a ranar Asabbaci, a aikata alheri ko a aikata mugunta, a ceci rai, ko a hallaka shi?”
And Jesus said to them, I ask you whether it is lawful on the sabbath to do good, or to do evil; to save life, or to kill?
10 Sai ya kalle su duka, sa’an nan ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Sai ya miƙe, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye.
And looking round on them all, he said to him, Stretch forth thy hand. And he did so; and his hand was restored.
11 Amma Farisiyawa da malaman Doka suka fusata, suka fara tattauna da junansu a kan abin da za su yi wa Yesu.
But they were filled with madness, and conferred with one another as to what they should do to Jesus.
12 Wata rana, a cikin kwanakin nan, Yesu ya je wani dutse domin yă yi addu’a, ya kuma kwana yana addu’a ga Allah.
And it came to pass in those days, that he went out into the mountain to pray; and he continued all night in prayer to God.
13 Da gari ya waye, sai ya kira almajiransa zuwa wurinsa, ya zaɓi guda goma sha biyu daga cikinsu, waɗanda ya kira su, Manzanni.
And when it was day, he called to him his disciples; and he chose from them twelve, whom he also named apostles;
14 Siman (wanda ya kira Bitrus), ɗan’uwansa Andarawus, Yaƙub, Yohanna, Filibus, Bartolomeyu,
Simon, whom he named Peter, and Andrew his brother, and James and John, and Philip and Bartholomew,
15 Mattiyu, Toma, Yaƙub ɗan Alfayus, Siman wanda ake kira Zilot,
and Matthew and Thomas, and James the Son of Alphaeus, and Simon called the zealot,
16 Yahuda ɗan Yaƙub, da kuma Yahuda Iskariyot, wanda ya bashe Yesu.
and Judas the brother of James, and Judas Iscariot, who became a traitor.
17 Sai ya sauko tare da su, ya tsaya a wani fili. A can, akwai taro mai yawa na almajiransa, da kuma mutane masu yawan gaske daga ko’ina a Yahudiya, Urushalima da kuma Taya da Sidon da suke bakin teku,
And he came down with them, and stood on a level place with a great multitude of his disciples, and a great crowd of the people from all Judaea and Jerusalem and the sea-coast of Tyre and Sidon, who came to hear him, and to be healed of their diseases.
18 waɗanda suka zo domin su ji shi, a kuma warkar da cututtukansu. Waɗanda suke fama da mugayen ruhohi kuwa aka warkar da su.
And they that were harassed with unclean spirits were cured.
19 Kuma dukan mutane suka yi ƙoƙari su taɓa shi, domin iko yana fitowa daga gare shi, ya kuwa warkar da su duka.
And the whole multitude sought to touch him, because power went out of him and healed all.
20 Da ya dubi almajiransa, sai ya ce, “Masu albarka ne ku da kuke matalauta, gama mulkin Allah naku ne.
And raising his eyes toward his disciples, he said, Blessed are ye poor; for yours is the kingdom of God.
21 Masu albarka ne ku da kuke jin yunwa yanzu, gama za ku ƙoshi. Masu albarka ne ku da kuke kuka yanzu, gama za ku yi dariya.
Blessed are ye that hunger now; for ye will be filled. Blessed are ye that weep now; for ye will laugh.
22 Masu albarka ne sa’ad da mutane suka ƙi ku, suka ware ku, suka zage ku, suna ce da ku mugaye, saboda Ɗan Mutum.
Blessed are ye when men hate you, and when they exclude you, and revile and cast out your name as evil, on account of the Son of man.
23 “Ku yi farin ciki a wannan rana, ku kuma yi tsalle don murna, saboda ladarku yana da yawa a sama. Gama haka kakanninsu suka yi wa annabawa.
Rejoice in that day, and leap for joy; for lo! your reward is great in heaven; for thus their fathers did to the prophets.
24 “Amma kaitonku da kuke da arziki, gama kun riga kun sami ta’aziyyarku.
But woe to you that are rich! for ye have received your consolation.
25 Kaitonku da kuke ƙosassu yanzu, gama za ku zauna da yunwa. Kaitonku da kuke dariya yanzu, gama za ku yi makoki da kuka.
Woe to you that are full now! for ye will hunger. Woe to you that laugh now! for ye will mourn and weep.
26 Kaitonku sa’ad da dukan mutane suna magana mai kyau a kanku, gama haka kakanninsu suka yi da annabawan ƙarya.
Woe, when all men speak well of you! for so did their fathers of the false prophets.
27 “Amma ina faɗa muku, ku da kuke ji na, ku ƙaunaci abokan gābanku, ku yi wa masu ƙinku alheri.
But I say to you who hear: Love your enemies; do good to those who hate you;
28 Ku albarkaci waɗanda suke la’anta ku, ku kuma yi wa waɗanda suke wulaƙanta ku addu’a.
bless those who curse you; pray for those who are spiteful to you.
29 In wani ya mare ka a wannan kumatu, juya masa ɗayan ma, in wani ya ƙwace maka babban riga, kada ma ka hana masa’yar cikin ma.
To him that smiteth thee on one cheek, offer also the other; and him that taketh away thy cloak, forbid not to take thy coat also.
30 Duk wanda ya roƙe ka abu, ka ba shi. In kuma wani ya yi maka ƙwace, kada ka nema yă mayar maka.
Give to every one that asketh of thee; and from him that taketh away thy goods, demand them not again.
31 Ka yi wa waɗansu abin da kai kake so su yi maka.
And as ye would that men should do to you, do ye also in like manner to them.
32 “In kana ƙaunar masu ƙaunarka ne kawai, ina ribar wannan? Ko masu zunubi ma suna ƙaunar waɗanda suke ƙaunarsu.
And if ye love those who love you, what thanks do ye deserve? for sinners also love those who love them.
33 In kuma kana yin alheri ga masu yi maka ne kaɗai, ina ribar wannan? Ko masu zunubi ma suna yin haka.
For if ye do good to those who do good to you, what thanks do ye deserve? even sinners do the same.
34 In kana ba da bashi ga mutanen da za su iya biyan ka ne kawai, ina ribar wannan? Ko masu zunubi ma, suna ba da bashi ga masu zunubi, da fata za a biya su tsab.
And if ye lend to those from whom ye expect to receive, what thanks do ye deserve? even sinners lend to sinners, to receive as much in return.
35 Amma, ku ƙaunaci abokan gābanku, ku kuma yi musu alheri, ku ba su bashi, ba da sa zuciya sai an biya ku ba. Ta yin haka ne kawai, za ku sami lada mai yawa, ku kuma zama’ya’yan Mafi Ɗaukaka, gama shi mai alheri ne ga marasa godiya da mugaye.
But love your enemies, and do good and lend, despairing of no one; and your reward will be great, and ye will be sons of the Most High; for he is kind to the unthankful and wicked.
36 Ku zama masu jinƙai, kamar yadda Ubanku mai jinƙai ne.
Be merciful, as your Father is merciful.
37 “Kada ku ɗora wa wani, ku ma ba za a ɗora muku ba. Kada ku yanke wa wani hukunci, ku ma ba za a yanke muku ba. Ku gafarta, ku ma za a gafarta muku.
And judge not, and ye will not be judged; and condemn not, and ye will not be condemned; forgive, and ye will be forgiven;
38 Ku bayar, ku ma sai a ba ku mudu a cike, a danƙare, har yă yi tozo, yana zuba, za a juye muku a hannun riga. Mudun da kuka auna da shi, da shi za a auna muku.”
give, and it will be given to you; good measure, pressed down, shaken together, running over, will men give into your bosom; for with what measure ye mete, it will be measured to you in return.
39 Ya kuma faɗa musu wannan misali cewa, “Makaho yana iya jagoran makaho ne? Ba sai dukansu biyu su fāɗa a rami ba?
And he spoke also a parable to them: Can the blind lead the blind? Will they not both fall into a ditch?
40 Ɗalibi bai fi malaminsa ba, sai dai kowane ɗalibi wanda ya sami cikakkiyar koyarwa, zai zama kamar malaminsa.
A disciple is not above his teacher; but every one when fully instructed will be as his teacher.
41 “Don me kake duban ɗan tsinke da yake idon ɗan’uwanka, amma ba ka kula da gungumen da yake a naka ido ba?
And why dost thou look at the mote in thy brother's eye, and not perceive the beam that is in thine own eye?
42 Yaya za ka ce wa ɗan’uwanka, ‘Ɗan’uwa, bari in cire maka ɗan tsinke da yake idonka,’ alhali kuwa, kai kanka ka kāsa ganin gungumen da yake a naka ido? Kai munafuki! Ka fara cire gungumen daga idonka, sa’an nan za ka iya gani sosai, ka kuma cire ɗan tsinken da yake a idon ɗan’uwanka.”
How canst thou say to thy brother, Brother, let me take out the mote that is in thine eye, when thou thyself perceivest not the beam in thine own eye? Hypocrite! first cast the beam out of thine own eye, and then thou wilt see clearly to take out the mote that is in thy brother's eye.
43 “Ba itace mai kyau da yake ba da munanan’ya’ya. Mummunan itace kuma ba ya ba da’ya’ya masu kyau.
For there is no good tree that beareth bad fruit; and again, there is no bad tree that beareth good fruit.
44 Kowane itace da irin’ya’yansa ne ake saninsa. Mutane ba sa tsinke’ya’yan ɓaure daga ƙaya, ko kuwa’ya’yan inabi daga sarƙaƙƙiya.
For every tree is known by its own fruit; for from thorns men do not gather figs, nor from a bramble-bush do they gather grapes.
45 Mutumin nagari yakan nuna abubuwa nagari daga cikin nagarta da yake a ɓoye a zuciyarsa, mugun mutum kuwa yakan nuna mugayen abubuwa daga muguntar da take a ɓoye a zuciyarsa. Gama baki yakan faɗa abin da ya cika zuciya ne.”
The good man out of the good treasure of his heart bringeth forth that which is good; and the evil man out of the evil treasure bringeth forth that which is evil; for out of the abundance of his heart his mouth speaketh.
46 “Don me kuke ce da ni, ‘Ubangiji, Ubangiji,’ amma ba kwa yin abin da na faɗa?
But why call ye me Lord, Lord, and do not the things which I say?
47 Zan nuna muku kwatancin mutumin da yakan zo wurina, yă ji kalmomina, yă kuma aikata.
Every one that cometh to me and heareth my sayings and doeth them, I will show you whom he is like.
48 Yana kama da mutumin da ya gina gida, wanda ya haƙa ƙasa da zurfi, sa’an nan ya kafa tushen ginin a kan dutse. Da ambaliyar ruwa ta taso, ƙarfin ruwa kuwa ya buga gidan, wannan bai jijjiga shi ba, domin an yi masa tushen gini na ainihi.
He is like a man building a house, who dug deep, and laid its foundation on a rock; and when a flood arose, the stream dashed against that house, and could not shake it; because it was well built.
49 Amma wanda yakan ji kalmomina, ba ya kuma aikata su, yana kama da mutumin da ya gina gida a ƙasa, ba tare da ya kafa tushen gini ba. A sa’ad da ƙarfin ruwa ya buga gidan, sai gidan yă rushe, mummunar rushewa kuwa.”
But he that heareth and doeth not, is like a man that built a house upon the earth without a foundation; against which the stream dashed, and it fell at once, and the ruin of that house was great.

< Luka 6 >