< Luka 5 >

1 Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah,
One day while many people were crowding around him to hear the message from God, Jesus was standing on the shore of Gennesaret Lake, [which is also called Lake Galilee].
2 sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu.
He saw two [fishing] boats at the edge of the lake. The fishermen had gone out of the boats and were washing their [fishing] nets [on the shore]. One of the boats belonged to Simon.
3 Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.
Jesus got in that boat and asked Simon to push the boat a little bit away from the shore [so that he could speak to the crowd more easily. Jesus] sat in the boat and taught the people [who were on the shore].
4 Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”
After he finished speaking [to them], he said to Simon, “Push the boat out to where the water is deep. Then let your nets down [into the water] to catch [some fish]!”
5 Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”
Simon replied, “Master, we [(exc)] worked hard all night but we did not catch any [fish]. But because you [(sg)] tell me to do it, I will let down the nets.”
6 Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa.
When Peter [and the men with him] had done that, they caught so many fish that their nets were breaking.
7 Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.
They motioned to their partners in the other boat to come and help them. So they came and filled both the boats [with fish from the net]. The result was that the boats were so full that they began to sink.
8 Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!”
Simon and all the men who were with him were amazed at how many fish they had taken. James and John, the two sons of Zebedee, who were Simon’s partners, were among those who were amazed. When Simon, [whose other name was] Peter, saw [the fish, feeling ashamed to be in the presence of someone who obviously had God’s power], he prostrated himself before Jesus and said, “Lord, you should go away from me, because I am a sinful man!”
9 Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama.
10 Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.”
But Jesus said to Simon, “Do not be afraid! [Up until now you(sg) have been gathering fish] [MET], but from now on you will gather people [to become my disciples].”
11 Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.
So after they brought the boats to the shore, they left their business [HYP] [in the hands of others] and went with Jesus.
12 Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”
While [Jesus] was in one of the cities [there in the district of Galilee], there was a man there who was very severely affected by leprosy. When he saw Jesus, he prostrated himself before him and, [wanting Jesus to heal him], pleaded with him, “Lord/Sir, [please heal me, because] you are able to heal me if you are willing to!”
13 Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.
[Then Jesus, disregarding the religious law that forbade people to come close to lepers], reached out his hand and touched the man. He said, “I am willing [to heal you]; and I heal you now!” Immediately the man [was healed]. He was no longer a leper [PRS]!
14 Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”
Then Jesus told him, “Make sure that you do not report [your healing immediately. First, go to a priest in Jerusalem] and show yourself to him [so that he can examine you and verify that you no longer have leprosy]. After the priest tells [the local people], they will know that [you have been healed, and you will be able to associate with them again]. Also take to the priest [the offering] that Moses commanded [that people who have been healed from leprosy should offer].”
15 Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu.
But many people heard the man’s report of what [Jesus had done]. The result was that large crowds came to Jesus to hear his [message] and to be healed of their sicknesses {so that he would heal their sicknesses}.
16 Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.
But he often would go away from them to the desolate area and pray.
17 Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo.
One day when [Jesus] was teaching, some men from the Pharisee [sect] were sitting there. Some of them were men who taught the [Jewish] laws. They had come from many [HYP] villages in Galilee [district] and also from Jerusalem and from [other] villages in Judea [district]. [At that time while] God was giving Jesus power to heal people,
18 Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu.
several men brought on a sleeping pad a man who was paralyzed. They wanted to bring him into [the house] and lay him in front of Jesus.
19 Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.
But there was no way to do that because of the large crowd of people, so they went up [the steps] onto the roof. They tied ropes onto the sleeping pad and, after [removing some of] the tiles on the roof, they lowered the man [on] the sleeping pad. They lowered him through the opening into the midst of the crowd in front of Jesus.
20 Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
When Jesus perceived that they believed that [he could heal the man], he said to him, “My friend, [I] forgive your sins!”
21 Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
The men who taught the [Jewish] laws and the rest of the Pharisees began to think within themselves, “Who does this man [think he is, saying] that? He is insulting God! (Nobody can forgive sins!/What person can forgive sins?) [RHQ] Only God can do that!”
22 Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku?
Jesus perceived what they were thinking. So he said to them, “(You should not think that way [about what I said]!/Why do you question within yourselves [about what I said]?) [RHQ] [Consider this]:
23 Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’?
It would [not] be risky [for someone] to say [to this man], ‘[I] forgive your sins,’ [because no one could see whether or not his sins were really forgiven. But no one] [RHQ], [without having the power to heal], would say to [him], ‘Get up and walk!’ [because people could easily see whether he was healed or not].
24 Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
But [as a result of my healing this man] you [(pl)] will know that [God] has authorized [me], the one who came from heaven, to forgive the sins [of people while I am on] the earth, [as well as to heal people].” Then he said to the man who was paralyzed, “To you I say, ‘Get up, pick up your sleeping pad, and go home!’”
25 Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah.
Immediately the man [was healed]. He stood up in front of them. He picked up the [sleeping pad] on which he had been lying, and went home, praising God.
26 Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”
All the people [there] were amazed! They praised God and were completely awestruck. They kept saying, “We [(inc)] have seen wonderful things today!”
27 Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.”
Then [Jesus] left [the town] and saw a man who collected taxes [for the Roman government]. His name was Levi. He was sitting in the booth where he collected the taxes. Jesus said to him, “Come with me [and become my disciple]!”
28 Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.
So Levi left his work [HYP] and went with Jesus.
29 Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su.
Afterwards, Levi prepared a big feast in his own house [for Jesus and his disciples]. There was a large group of tax collectors and others eating together with them.
30 Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
The men who were there who taught the [Jewish] laws, ones who belonged to the Pharisee [sect], complained to Jesus’ disciples, saying, “([It is disgusting that] you are eating with tax collectors and [others who we(exc) consider to be] sinners!/Why are you eating with tax collectors [and others who we(exc) consider to be] sinners?)” [RHQ]
31 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
Then, [to indicate that it was those who knew that they had sinned who were coming to him for help], Jesus said to them, “[It is] people who are sick who need a doctor, not those who are well [MET].
32 Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”
[Similarly], I did not come [from heaven] to invite [those who think they are] righteous [to come to me]. On the contrary, [I came to invite those who know that they are] sinners to turn from their sinful behavior [and come to me].”
33 Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”
[Those Jewish leaders] said to Jesus, “The disciples of John [the Baptizer] often abstain from food [to show that they want to please God], and the disciples of the Pharisees do that, too. But your disciples keep on eating and drinking! [Why do not they fast like the others]?”
34 Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su?
[To show them that it was not appropriate for his disciples to be sad and abstain from food while he was still with them] [MET], Jesus said to them, “When (the bridegroom/man who is getting married) is with [his friends at the time of the wedding], you certainly do not make his friends abstain from food, do you [RHQ]? [No, you do not do that].
35 Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”
[But] some day he will be taken away {[his enemies] will take him away} from them. Then, at that time, his friends will abstain from food, [because they will be sad].”
36 Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba.
Then Jesus told them two parables [to show them that those who desire to live according to God’s new message should not be forced to obey the old religious traditions like] ([fasting/abstaining from food]), [and that those who know only the old traditions are not eager to accept new ones] [MET]. He said, “People never tear a piece of cloth from a new garment and attach it to an old garment [to mend it]. If they did that, not only would they be ruining the new garment by tearing it, but the new piece of cloth would not match the old garment.
37 Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace.
Neither does anyone put freshly-[squeezed] grape juice into old skin bags [to store it]. If anyone did that, the grape juice would burst the skin bags [because they would not stretch when the] new [wine ferments and expands. Then] the skin bags would be ruined, and [the wine] would [also] be spilled.
38 A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna.
On the contrary, new wine must be put into new wineskins.
39 Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’”
Furthermore, those who have drunk [only] old wine [are content with that]. They do not want to drink the new wine, because they say, ‘The old wine is [MET] fine!’”

< Luka 5 >