< Luka 4 >

1 Yesu kuwa cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dawo daga Urdun, Ruhu kuma ya kai shi cikin hamada,
Kwathi uJesu egcwele uMoya oNgcwele wabuya evela eJordani, wakhokhelelwa nguMoya enkangala,
2 inda kwana arba’in, Iblis ya gwada shi. Bai ci kome ba a cikin kwanakin nan, a ƙarshensu kuwa ya ji yunwa.
walingwa ngudiyabhola insuku ezingamatshumi amane. Njalo kadlanga lutho ngalezonsuku; kwathi seziphelile, ekucineni walamba.
3 Iblis ya ce masa, “In kai Ɗan Allah ne, ka faɗa wa wannan dutse yă zama burodi.”
Udiyabhola wasesithi kuye: Uba uyiNdodana kaNkulunkulu, tshono kulelilitshe ukuthi libe yisinkwa.
4 Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake, ‘Ba da abinci kaɗai mutum zai rayu ba.’”
UJesu wasemphendula, wathi: Kulotshiwe, ukuthi umuntu kayikuphila ngesinkwa sodwa, kodwa ngalo lonke ilizwi likaNkulunkulu.
5 Iblis ya kai shi can kan wani wuri mai tsawo, ya nunnuna masa a ƙyiftawar ido dukan mulkokin duniya.
Udiyabhola wasemkhokhelela entabeni ende wamtshengisa yonke imibuso yomhlaba ngesikhatshana.
6 Ya ce masa, “Zan ba ka dukan ikonsu da darajarsu, gama ni aka danƙa wa, kuma zan bai wa duk wanda na ga dama.
Udiyabhola wasesithi kuye: Amandla wonke la lobukhosi bayo ngizakunika; ngoba anikwe mina, njalo ngiwanika loba ngubani engithandayo.
7 Saboda haka in ka yi mini sujada, dukan wannan zai zama naka.”
Ngakho wena uba ukhonza phambi kwami, konke kuzakuba ngokwakho.
8 Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake, ‘Ka yi wa Ubangiji Allahnka sujada, kuma shi kaɗai za ka bauta wa.’”
UJesu wasemphendula wathi: Suka ngemva kwami, Sathane; ngoba kulotshiwe ukuthi: Uzakhothamela eNkosini uNkulunkulu wakho, njalo umkhonze yena yedwa.
9 Sai Iblis, ya kai shi Urushalima ya sa ya tsaya a kan wuri mafi tsayi na haikali ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, ka yi tsalle daga nan zuwa ƙasa.
Wasemkhokhelela eJerusalema, wammisa engqongeni yethempeli, wasesithi kuye: Uba uyiNdodana kaNkulunkulu, ziwisele phansi usuka lapha;
10 Gama a rubuce yake, “‘Zai umarci mala’ikunsa game da kai, su kiyaye ka da kyau;
ngoba kulotshiwe ukuthi: Uzalaya ingilosi zakhe ngawe, ukukulondoloza;
11 za su tallafe ka da hannuwansu, don kada ka buga ƙafarka a kan dutse.’”
lokuthi: Zizakuphatha ngezandla, hlezi loba nini ukhube unyawo lwakho elitsheni.
12 Yesu ya amsa ya ce, “An ce, ‘Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.’”
UJesu wasephendula wathi kuye: Kuthiwa: Ungayilingi iNkosi uNkulunkulu wakho.
13 Da Iblis ya gama dukan wannan gwajin, ya bar shi sai lokacin da wata dama ta samu.
Udiyabhola eseqedile ukulinga konke, wasuka kuye kwaze kwaba ngesinye isikhathi.
14 Yesu ya koma Galili cikin ikon Ruhu. Labarinsa kuwa ya bazu ko’ina a ƙauyuka.
UJesu wasebuyela eGalili ngamandla kaMoya; lendumela yakhe yaphuma kuso sonke isigaba esizingelezeleyo.
15 Ya yi ta koyarwa a majami’unsu, kowa kuwa ya yabe shi.
Yena wasefundisa emasinagogeni abo, edunyiswa yibo bonke.
16 Ya tafi Nazaret, inda aka yi renonsa. A ranar Asabbaci kuma, ya shiga majami’a kamar yadda ya saba. Sai ya miƙe don yă yi karatu.
Wasefika eNazaretha, lapho ayondliwe khona; njengokwejwayela kwakhe wasengena esinagogeni ngosuku lwesabatha, wasukuma ukuze afunde.
17 Aka kuwa ba shi naɗaɗɗen littafin annabi Ishaya. Da ya buɗe, sai ya sami wurin da aka rubuta,
Wasenikwa ugwalo lomprofethi uIsaya. Waseluvula ugwalo, wayithola indawo okubhalwe kuyo ukuthi:
18 “Ruhun Ubangiji yana kaina, domin ya shafe ni, in yi wa matalauta wa’azin bishara. Ya aiko ni in yi shelar’yanci ga’yan kurkuku, in kuma buɗe idanun makafi, in ba da’yanci ga waɗanda aka danne.
UMoya weNkosi uphezu kwami, ngakho ingigcobile ukuthi ngitshumayele ivangeli kubayanga; ingithumile ukusilisa abadabukileyo enhliziyweni; ukumemezela ukukhululwa kwabathunjiweyo, lokubona kwabayiziphofu, ukukhulula ababandezelweyo,
19 In yi shelar shekarar tagomashin Ubangiji.”
ukumemezela umnyaka womusa weNkosi.
20 Sai ya naɗe naɗaɗɗen littafin ya mayar wa mai hidimar, ya kuma zauna. Dukan idanun waɗanda suke a majami’ar, suka koma a kansa.
Waselugoqa ugwalo, walubuyisela encekwini, wahlala phansi; lamehlo abo bonke ababesesinagogeni amjolozela.
21 Sai ya fara ce musu, “A yau, Nassin nan, ya cika a kunnenku.”
Waseqala ukuthi kubo: Lamuhla lumbhalo ugcwalisekile endlebeni zenu.
22 Duk suka yabe shi, suka yi mamakin kalmomin alheri da suke fitowa daga bakinsa. Suka yi tambaya, suna cewa, “Anya, wannan ba ɗan Yusuf ba ne?”
Labo bonke bafakaza ngaye, bamangala ngamazwi omusa aphuma emlonyeni wakhe, basebesithi: Lo kayisiyo indodana kaJosefa yini?
23 Yesu ya ce musu, “Tabbatacce, na san za ku faɗa mini karin maganan nan, ‘Likita, warkar da kanka! Ka kuma yi abin da muka ji ka yi a Kafarnahum, a nan garinka.’”
Wasesithi kubo: Isibili lizakutsho kimi lesisaga: Melaphi, zelaphe wena; konke lokho esikuzwileyo okwenzeke eKapenawume, kwenze lalapha emzini wakini.
24 Ya ci gaba, da ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, babu annabin da ake yarda da shi a garinsa.
Wathi-ke: Ngiqinisile ngithi kini: Kakho umprofethi owemukelekayo elizweni lakibo.
25 Ina tabbatar muku a zamanin Iliya, akwai gwauraye da yawa a Isra’ila, sa’ad da aka rufe sararin sama har shekara uku da rabi, aka kuma yi yunwa mai tsanani ko’ina a ƙasar.
Kodwa ngeqiniso ngithi kini: Abafelokazi abanengi babekhona koIsrayeli ensukwini zikaElija, lapho izulu lalivalekile iminyaka emithathu lenyanga eziyisithupha, kwaze kwaba khona indlala enkulu emhlabeni wonke;
26 Duk da haka, ba a aiki Iliya ga ko ɗaya a cikinsu ba. Sai dai zuwa ga wata gwauruwa da take a Zarefat, a yankin Sidon.
kodwa uElija kathunyelwanga lakomunye wabo, ngaphandle kweSarepita yeSidoni kowesifazana ongumfelokazi.
27 Akwai kuma mutane da yawa a Isra’ila masu kuturta a zamanin annabi Elisha, amma ba ko ɗayansu da aka tsarkake sai Na’aman mutumin Suriyan nan kaɗai.”
Futhi amalephero amanengi ayekhona koIsrayeli ngesikhathi sikaElisha umprofethi; kodwa kakuhlanjululwanga lamunye wawo, ngaphandle kukaNamani umSiriya.
28 Dukan mutanen da suke cikin majami’a suka fusata ƙwarai da jin wannan.
Kwathi bonke ababesesinagogeni bagcwala ulaka, bezizwa lezizinto,
29 Suka tashi, suka fitar da Yesu bayan gari, suka kai shi goshin tudun da aka gina garin, don su ture shi ƙasa,
basebesukuma, bamkhuphela ngaphandle komuzi, bamqhubela eliweni lentaba umuzi wabo owawakhiwe phezu kwayo, ukuze bamphosele phansi eliweni.
30 amma sai ya bi ta tsakiyar taron ya yi tafiyarsa.
Kodwa yena edabula phakathi kwabo wahamba.
31 Sai ya tafi Kafarnahum, wani gari a Galili, a ranar Asabbaci kuma, ya fara koya wa mutane.
Wasesehlela eKapenawume umuzi weGalili; njalo wayebafundisa ngamasabatha.
32 Suka yi ta mamakin koyarwarsa, domin saƙonsa yana da iko.
Basebebabaza ngemfundiso yakhe, ngoba ilizwi lakhe lalilamandla.
33 A cikin majami’ar, akwai wani mutum mai aljani, wani mugun ruhu. Mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce,
Futhi kwakukhona esinagogeni umuntu owayelomoya wedimoni ongcolileyo, wasememeza ngelizwi elikhulu,
34 “Wayyo! Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne don ka hallaka mu? Na san wane ne kai, Mai Tsarki na Allah!”
wathi: Yekela! Silani lawe, Jesu mNazaretha? Uze ukusibhubhisa yini? Ngiyakwazi wena ukuthi ungubani: ONgcwele kaNkulunkulu.
35 Yesu ya tsawata masa da ƙarfin cewa, “Yi shiru! Ka fita daga cikinsa!” Sai aljanin ya fyaɗa mutumin da ƙasa a gabansu duka, sa’an nan ya fita, ya bar shi ba wani rauni.
UJesu wasemkhuza, esithi: Thula, uphume kuye! Ledimoni selimwisele phakathi laphuma kuye, lingamlimazanga.
36 Dukan mutanen suka yi mamaki, suka ce wa junansu, “Wace irin koyarwa ce haka? Da ƙarfi da iko, yana ba wa mugayen ruhohin umarni suna kuma fita!”
Kwasekubafikela bonke ukumangala, bakhulumisana, besithi: Yilizwi bani leli, ukuthi ngegunya langamandla uyalaya omoya abangcolileyo, baphume?
37 Labarinsa kuwa ya bazu ko’ina a cikin ƙasar.
Yasiphuma indumela yakhe kuyo yonke indawo yesigaba esizingelezeleyo.
38 Yesu ya fita daga majami’ar, ya tafi gidan Siman. Surukar Siman kuwa tana fama da zazzaɓi mai tsanani, sai suka roƙi Yesu yă taimake ta.
Wasesukuma waphuma esinagogeni, wayangena endlini kaSimoni; njalo uninazala kaSimoni wayebanjwe luqhuqho olukhulu; basebemcelela kuye.
39 Sai ya sunkuya kusa da ita, ya kuma tsawata wa zazzaɓin, sai zazzaɓin ya sāke ta. Nan take ta tashi, ta yi musu hidima.
Wasemengama, wakhuza uqhuqho, khona lwamyekela; njalo wahle wasukuma wabasebenzela.
40 Rana tana fāɗuwa, sai mutane suka yi ta kawo wa Yesu dukan waɗanda suke da cuta iri-iri, sai ya ɗibiya wa kowannensu hannuwansa, ya warkar da su.
Kwathi ekutshoneni kwelanga, bonke ababelababegula izifo ezitshiyeneyo babaletha kuye; wasebeka izandla kulowo lalowo wabo wabasilisa.
41 Bugu da ƙari, aljanu suka fiffita daga cikin mutane da yawa suna ihu suna cewa, “Kai Ɗan Allah ne!” Amma ya kwaɓe su, ya hana su magana, don sun san cewa shi ne Kiristi.
Kwasekuphuma lamadimoni kwabanengi, ememeza esithi: Wena unguKristu iNdodana kaNkulunkulu. Wasewakhuza engawavumeli ukuthi akhulume, ngoba ayemazi ukuthi unguKristu.
42 Da gari yana wayewa, sai Yesu ya je inda ba kowa. Mutane suka yi ta nemansa, da suka zo inda yake, sai suka yi ƙoƙari su hana shi barinsu.
Kwathi sekusile, waphuma waya endaweni eyinkangala, lamaxuku amdinga, eza kuye, amvimbela ukuthi angasuki kiwo.
43 Amma ya ce, “Dole in yi wa’azin bisharar mulkin Allah ga sauran garuruwa, saboda wannan ne aka aiko ni.”
Kodwa wathi kuwo: Ngimele ukutshumayela ivangeli lombuso kaNkulunkulu lakweminye imizi; ngoba ngithunyelwe lokho.
44 Sai ya dinga yin wa’azi a majami’un Yahudiya.
Wayesetshumayela emasinagogeni eGalili.

< Luka 4 >