< Luka 4 >

1 Yesu kuwa cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dawo daga Urdun, Ruhu kuma ya kai shi cikin hamada,
Then Jesus, full of the Holy Spirit, returned from the Jordan, and was led about by the Spirit in the Desert for forty days,
2 inda kwana arba’in, Iblis ya gwada shi. Bai ci kome ba a cikin kwanakin nan, a ƙarshensu kuwa ya ji yunwa.
tempted all the while by the Devil. During those days He ate nothing, and at the close of them He suffered from hunger.
3 Iblis ya ce masa, “In kai Ɗan Allah ne, ka faɗa wa wannan dutse yă zama burodi.”
Then the Devil said to Him, "If you are God's Son, tell this stone to become bread."
4 Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake, ‘Ba da abinci kaɗai mutum zai rayu ba.’”
"It is written," replied Jesus, "'It is not on bread alone that a man shall live.'"
5 Iblis ya kai shi can kan wani wuri mai tsawo, ya nunnuna masa a ƙyiftawar ido dukan mulkokin duniya.
The Devil next led Him up and caused Him to see at a glance all the kingdoms of the world.
6 Ya ce masa, “Zan ba ka dukan ikonsu da darajarsu, gama ni aka danƙa wa, kuma zan bai wa duk wanda na ga dama.
And the Devil said to Him, "To you will I give all this authority and this splendour; for it has been handed over to me, and on whomsoever I will I bestow it.
7 Saboda haka in ka yi mini sujada, dukan wannan zai zama naka.”
If therefore you do homage to me, it shall all be yours.'
8 Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake, ‘Ka yi wa Ubangiji Allahnka sujada, kuma shi kaɗai za ka bauta wa.’”
Jesus answered him, "It is written, 'To the Lord thy God thou shalt do homage, and to Him alone shalt thou render worship.'"
9 Sai Iblis, ya kai shi Urushalima ya sa ya tsaya a kan wuri mafi tsayi na haikali ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, ka yi tsalle daga nan zuwa ƙasa.
Then he brought Him to Jerusalem and caused Him to stand on the roof of the Temple, and said to Him, "If you are God's Son, throw yourself down from here; for it is written,
10 Gama a rubuce yake, “‘Zai umarci mala’ikunsa game da kai, su kiyaye ka da kyau;
'He will give orders to His angels concerning thee, to guard thee safely;'
11 za su tallafe ka da hannuwansu, don kada ka buga ƙafarka a kan dutse.’”
and 'On their hands they shall bear thee up, Lest at any moment thou shouldst strike thy foot against a stone.'"
12 Yesu ya amsa ya ce, “An ce, ‘Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.’”
The reply of Jesus was, "It is said, 'Thou shalt not put the Lord they God to the proof.'"
13 Da Iblis ya gama dukan wannan gwajin, ya bar shi sai lokacin da wata dama ta samu.
So the Devil, having fully tried every kind of temptation on Him, left Him for a time.
14 Yesu ya koma Galili cikin ikon Ruhu. Labarinsa kuwa ya bazu ko’ina a ƙauyuka.
Then Jesus returned in the Spirit's power to Galilee; and His fame spread through all the adjacent districts.
15 Ya yi ta koyarwa a majami’unsu, kowa kuwa ya yabe shi.
And He proceeded to teach in their synagogues, winning praise from all.
16 Ya tafi Nazaret, inda aka yi renonsa. A ranar Asabbaci kuma, ya shiga majami’a kamar yadda ya saba. Sai ya miƙe don yă yi karatu.
He came to Nazareth also, where He had been brought up; and, as was His custom, He went to the synagogue on the Sabbath, and stood up to read.
17 Aka kuwa ba shi naɗaɗɗen littafin annabi Ishaya. Da ya buɗe, sai ya sami wurin da aka rubuta,
And there was handed to Him the book of the Prophet Isaiah, and, opening the book, He found the place where it was written,
18 “Ruhun Ubangiji yana kaina, domin ya shafe ni, in yi wa matalauta wa’azin bishara. Ya aiko ni in yi shelar’yanci ga’yan kurkuku, in kuma buɗe idanun makafi, in ba da’yanci ga waɗanda aka danne.
"The Spirit of the Lord is upon me, because He has anointed me to proclaim Good News to the poor; He has sent me to announce release to the prisoners of war and recovery of sight to the blind: to send away free those whom tyranny has crushed,
19 In yi shelar shekarar tagomashin Ubangiji.”
to proclaim the year of acceptance with the Lord."
20 Sai ya naɗe naɗaɗɗen littafin ya mayar wa mai hidimar, ya kuma zauna. Dukan idanun waɗanda suke a majami’ar, suka koma a kansa.
And rolling up the book, He returned it to the attendant, and sat down--to speak. And the eyes of all in the synagogue were fixed on Him.
21 Sai ya fara ce musu, “A yau, Nassin nan, ya cika a kunnenku.”
Then He proceeded to say to them, "To-day is this Scripture fulfilled in your hearing."
22 Duk suka yabe shi, suka yi mamakin kalmomin alheri da suke fitowa daga bakinsa. Suka yi tambaya, suna cewa, “Anya, wannan ba ɗan Yusuf ba ne?”
And they all spoke well of Him, wondering at the sweet words of kindness which fell from His lips, while they asked one another, "Is not this Joseph's son?"
23 Yesu ya ce musu, “Tabbatacce, na san za ku faɗa mini karin maganan nan, ‘Likita, warkar da kanka! Ka kuma yi abin da muka ji ka yi a Kafarnahum, a nan garinka.’”
"Doubtless," said He, "you will quote to me the proverb, 'Physician, cure yourself: all that we hear that you have done at Capernaum, do here also in your native place.'"
24 Ya ci gaba, da ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, babu annabin da ake yarda da shi a garinsa.
"I tell you in solemn truth," He added, "that no Prophet is welcomed among his own people.
25 Ina tabbatar muku a zamanin Iliya, akwai gwauraye da yawa a Isra’ila, sa’ad da aka rufe sararin sama har shekara uku da rabi, aka kuma yi yunwa mai tsanani ko’ina a ƙasar.
But I tell you in truth that there was many a widow in Israel in the time of Elijah, when there was no rain for three years and six months and there came a severe famine over all the land;
26 Duk da haka, ba a aiki Iliya ga ko ɗaya a cikinsu ba. Sai dai zuwa ga wata gwauruwa da take a Zarefat, a yankin Sidon.
and yet to not one of them was Elijah sent: he was only sent to a widow at Zarephath in the Sidonian country.
27 Akwai kuma mutane da yawa a Isra’ila masu kuturta a zamanin annabi Elisha, amma ba ko ɗayansu da aka tsarkake sai Na’aman mutumin Suriyan nan kaɗai.”
And there was also many a leper in Israel in the time of the Prophet Elisha, and yet not one of them was cleansed, but Naaman the Syrian was."
28 Dukan mutanen da suke cikin majami’a suka fusata ƙwarai da jin wannan.
Then all in the synagogue, while listening to these words, were filled with fury.
29 Suka tashi, suka fitar da Yesu bayan gari, suka kai shi goshin tudun da aka gina garin, don su ture shi ƙasa,
They rose, hurried Him outside the town, and brought Him to the brow of the hill on which their town was built, to throw Him down the cliff;
30 amma sai ya bi ta tsakiyar taron ya yi tafiyarsa.
but He passed through the midst of them and went His way.
31 Sai ya tafi Kafarnahum, wani gari a Galili, a ranar Asabbaci kuma, ya fara koya wa mutane.
So He came down to Capernaum, a town in Galilee, where He frequently taught the people on the Sabbath days.
32 Suka yi ta mamakin koyarwarsa, domin saƙonsa yana da iko.
And they were greatly impressed by His teaching, because He spoke with the language of authority.
33 A cikin majami’ar, akwai wani mutum mai aljani, wani mugun ruhu. Mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce,
But in the synagogue there was a man possessed by the spirit of a foul demon. In a loud voice he cried out,
34 “Wayyo! Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne don ka hallaka mu? Na san wane ne kai, Mai Tsarki na Allah!”
"Ha! Jesus the Nazarene, what have you to do with us? I know who you are--God's Holy One!"
35 Yesu ya tsawata masa da ƙarfin cewa, “Yi shiru! Ka fita daga cikinsa!” Sai aljanin ya fyaɗa mutumin da ƙasa a gabansu duka, sa’an nan ya fita, ya bar shi ba wani rauni.
But Jesus rebuked the demon. "Silence!" He exclaimed; "come out of him." Upon this, the demon hurled the man into the midst of them, and came out of him without doing him any harm.
36 Dukan mutanen suka yi mamaki, suka ce wa junansu, “Wace irin koyarwa ce haka? Da ƙarfi da iko, yana ba wa mugayen ruhohin umarni suna kuma fita!”
All were astonished and awe-struck; and they asked one another, "What sort of language is this? For with authority and real power He gives orders to the foul spirits and they come out."
37 Labarinsa kuwa ya bazu ko’ina a cikin ƙasar.
And the talk about Him spread into every part of the neighbouring country.
38 Yesu ya fita daga majami’ar, ya tafi gidan Siman. Surukar Siman kuwa tana fama da zazzaɓi mai tsanani, sai suka roƙi Yesu yă taimake ta.
Now when He rose and left the synagogue He went to Simon's house. Simon's mother-in-law was suffering from an acute attack of fever; and they consulted Him about her.
39 Sai ya sunkuya kusa da ita, ya kuma tsawata wa zazzaɓin, sai zazzaɓin ya sāke ta. Nan take ta tashi, ta yi musu hidima.
Then standing over her He rebuked the fever, and it left her; and she at once rose and waited on them.
40 Rana tana fāɗuwa, sai mutane suka yi ta kawo wa Yesu dukan waɗanda suke da cuta iri-iri, sai ya ɗibiya wa kowannensu hannuwansa, ya warkar da su.
At sunset all who had friends suffering from any illness brought them to Him, and He laid His hands on them all, one by one, and cured them.
41 Bugu da ƙari, aljanu suka fiffita daga cikin mutane da yawa suna ihu suna cewa, “Kai Ɗan Allah ne!” Amma ya kwaɓe su, ya hana su magana, don sun san cewa shi ne Kiristi.
Demons also came out of many, loudly calling out, "You are the Son of God." But He rebuked them and forbad them to speak, because they knew Him to be the Christ.
42 Da gari yana wayewa, sai Yesu ya je inda ba kowa. Mutane suka yi ta nemansa, da suka zo inda yake, sai suka yi ƙoƙari su hana shi barinsu.
Next morning, at daybreak, He left the town and went away to a solitary place; but the people flocked out to find Him, and, coming to the place where He was, they endeavoured to detain Him that He might not leave them.
43 Amma ya ce, “Dole in yi wa’azin bisharar mulkin Allah ga sauran garuruwa, saboda wannan ne aka aiko ni.”
But He said to them, "I have to tell the Good News of the Kingdom of God to the other towns also, because for this purpose I was sent."
44 Sai ya dinga yin wa’azi a majami’un Yahudiya.
And for some time He preached in the synagogues in Galilee.

< Luka 4 >