< Luka 4 >

1 Yesu kuwa cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dawo daga Urdun, Ruhu kuma ya kai shi cikin hamada,
Iesus then full of the holy goost returnyd fro Iordan and was caryed of ye sprete into wildernes
2 inda kwana arba’in, Iblis ya gwada shi. Bai ci kome ba a cikin kwanakin nan, a ƙarshensu kuwa ya ji yunwa.
and was. xl. dayes tempted of the devyll. And in thoose dayes ate he no thinge. And when they were ended he afterward hongred.
3 Iblis ya ce masa, “In kai Ɗan Allah ne, ka faɗa wa wannan dutse yă zama burodi.”
And the devyll sayde vnto him: yf thou be the sonne of God comaunde this stone yt it be breed.
4 Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake, ‘Ba da abinci kaɗai mutum zai rayu ba.’”
And Iesus answered hym sayinge: It is writte: man shall not live by breed only but by every worde of God.
5 Iblis ya kai shi can kan wani wuri mai tsawo, ya nunnuna masa a ƙyiftawar ido dukan mulkokin duniya.
And ye devyll toke him vp into an hye moutayne and shewed him all the kyngdoms of the worlde eve in ye twincklinge of an eye.
6 Ya ce masa, “Zan ba ka dukan ikonsu da darajarsu, gama ni aka danƙa wa, kuma zan bai wa duk wanda na ga dama.
And ye devyll sayde vnto him: all this power will I geve ye every whit and the glory of the: for yt is delyvered to me and to whosoever I will I geve it.
7 Saboda haka in ka yi mini sujada, dukan wannan zai zama naka.”
Yf thou therfore wilt worshippe me they shalbe all thyne.
8 Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake, ‘Ka yi wa Ubangiji Allahnka sujada, kuma shi kaɗai za ka bauta wa.’”
Iesus answered him and sayde: hence from me Sathan. For it is written: Thou shalt honour the Lorde thy God and him only serve.
9 Sai Iblis, ya kai shi Urushalima ya sa ya tsaya a kan wuri mafi tsayi na haikali ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, ka yi tsalle daga nan zuwa ƙasa.
And he caryed him to Ierusalem and set him on a pynacle of the temple and sayd vnto him: Yf thou be the sonne of God cast thy silfe doune from hens.
10 Gama a rubuce yake, “‘Zai umarci mala’ikunsa game da kai, su kiyaye ka da kyau;
For it is written he shall geve his angels charge over the to kepe the
11 za su tallafe ka da hannuwansu, don kada ka buga ƙafarka a kan dutse.’”
and with there hondis they shall stey the vp that thou dasshe not thy fote agaynst a stone.
12 Yesu ya amsa ya ce, “An ce, ‘Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.’”
Iesus answered and sayde to him it is sayd: thou shalt not tempte the Lorde thy God.
13 Da Iblis ya gama dukan wannan gwajin, ya bar shi sai lokacin da wata dama ta samu.
Assone as the devyll had ended all his temptacions he departed from him for a season.
14 Yesu ya koma Galili cikin ikon Ruhu. Labarinsa kuwa ya bazu ko’ina a ƙauyuka.
And Iesus retourned by the power of ye sprete in to Galile and there went a fame of him thorowe oute all the regio roude aboute.
15 Ya yi ta koyarwa a majami’unsu, kowa kuwa ya yabe shi.
And he taught in their synagoges and was commended of all men.
16 Ya tafi Nazaret, inda aka yi renonsa. A ranar Asabbaci kuma, ya shiga majami’a kamar yadda ya saba. Sai ya miƙe don yă yi karatu.
And he came to Nazareth where he was noursed and as hys custome was went in to the synagoge on the Saboth dayes and stode vp for to rede.
17 Aka kuwa ba shi naɗaɗɗen littafin annabi Ishaya. Da ya buɗe, sai ya sami wurin da aka rubuta,
And ther was delyvered vnto him ye boke of ye Prophete Esaias. And when he had opened the boke he founde the place where it was written.
18 “Ruhun Ubangiji yana kaina, domin ya shafe ni, in yi wa matalauta wa’azin bishara. Ya aiko ni in yi shelar’yanci ga’yan kurkuku, in kuma buɗe idanun makafi, in ba da’yanci ga waɗanda aka danne.
The sprete of the lorde vpon me because he hath annoynted me: to preache ye gospell to ye poore he hath sent me: and to heale the broken harted: to preache delyverauce to the captive and sight to the blinde and frely to set at lyberte them that are brused
19 In yi shelar shekarar tagomashin Ubangiji.”
and to preache the acceptable yeare of the Lorde.
20 Sai ya naɗe naɗaɗɗen littafin ya mayar wa mai hidimar, ya kuma zauna. Dukan idanun waɗanda suke a majami’ar, suka koma a kansa.
And he cloosed the booke and gave it agayne to the minister and sate doune. And the eyes of all that were in the synagoge were fastened on him.
21 Sai ya fara ce musu, “A yau, Nassin nan, ya cika a kunnenku.”
And he began to saye vnto them. This daye is this scripture fulfilled in youre eares.
22 Duk suka yabe shi, suka yi mamakin kalmomin alheri da suke fitowa daga bakinsa. Suka yi tambaya, suna cewa, “Anya, wannan ba ɗan Yusuf ba ne?”
And all bare him witnes and wondred at the gracious wordes which proceded oute of his mouth and sayde: Is not this Iosephs sonne?
23 Yesu ya ce musu, “Tabbatacce, na san za ku faɗa mini karin maganan nan, ‘Likita, warkar da kanka! Ka kuma yi abin da muka ji ka yi a Kafarnahum, a nan garinka.’”
And he sayde vnto them: Ye maye very well saye vnto me this proverbe: Phisicion heale thy silfe. Whatsoever we have heard done in Capernaum do the same here lyke wyse in thyne awne countre.
24 Ya ci gaba, da ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, babu annabin da ake yarda da shi a garinsa.
And he sayde verely I saye vnto you: No Prophet is accepted in his awne countre.
25 Ina tabbatar muku a zamanin Iliya, akwai gwauraye da yawa a Isra’ila, sa’ad da aka rufe sararin sama har shekara uku da rabi, aka kuma yi yunwa mai tsanani ko’ina a ƙasar.
But I tell you of a truth many wyddowes were in Israell in the dayes of Helias when hevyn was shet thre yeres and syxe monethes when greate fammisshemet was throughoute all the londe
26 Duk da haka, ba a aiki Iliya ga ko ɗaya a cikinsu ba. Sai dai zuwa ga wata gwauruwa da take a Zarefat, a yankin Sidon.
and vnto none of them was Helias sent save in to Sarephta besydes Sidon vnto a woma that was a widow.
27 Akwai kuma mutane da yawa a Isra’ila masu kuturta a zamanin annabi Elisha, amma ba ko ɗayansu da aka tsarkake sai Na’aman mutumin Suriyan nan kaɗai.”
And many lepers were in Israel in the tyme of Heliseus the Prophete: and yet none of them was healed savinge Naaman of Siria.
28 Dukan mutanen da suke cikin majami’a suka fusata ƙwarai da jin wannan.
And as many as were in ye sinagoge when they herde that were filled with wrath:
29 Suka tashi, suka fitar da Yesu bayan gari, suka kai shi goshin tudun da aka gina garin, don su ture shi ƙasa,
and roose vp and thrust him oute of the cite and ledde him eve vnto the edge of the hill wher on their cite was bilte to cast him doune hedlynge.
30 amma sai ya bi ta tsakiyar taron ya yi tafiyarsa.
But he went his waye eve thorow the myddes of them:
31 Sai ya tafi Kafarnahum, wani gari a Galili, a ranar Asabbaci kuma, ya fara koya wa mutane.
and came in to Capernaum a cyte of Galile and there taught the on the Saboth dayes.
32 Suka yi ta mamakin koyarwarsa, domin saƙonsa yana da iko.
And they were astonyed at his doctrine: for his preachige was wt power.
33 A cikin majami’ar, akwai wani mutum mai aljani, wani mugun ruhu. Mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce,
And in the synagoge ther was a ma which had a sprete of an vncleane devell and cryed with aloude voyce
34 “Wayyo! Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne don ka hallaka mu? Na san wane ne kai, Mai Tsarki na Allah!”
sayinge: let me alone what hast thou to do with vs thou Iesus of Nazareth? Arte thou come to destroye vs? I knowe the what thou arte eve the holy of God.
35 Yesu ya tsawata masa da ƙarfin cewa, “Yi shiru! Ka fita daga cikinsa!” Sai aljanin ya fyaɗa mutumin da ƙasa a gabansu duka, sa’an nan ya fita, ya bar shi ba wani rauni.
And Iesus rebuked him sayinge: holde thy peace and come oute of him. And the devyll threwe him in the myddes of them and came oute of him and hurt him not.
36 Dukan mutanen suka yi mamaki, suka ce wa junansu, “Wace irin koyarwa ce haka? Da ƙarfi da iko, yana ba wa mugayen ruhohin umarni suna kuma fita!”
And feare came on them all and they spake amonge them selves sayinge: what maner a thinge is this? For with auctorite and power he commaundeth the foule spretes and they come out?
37 Labarinsa kuwa ya bazu ko’ina a cikin ƙasar.
And ye fame of him spreed abroode thorowoute all places of the countre round aboute.
38 Yesu ya fita daga majami’ar, ya tafi gidan Siman. Surukar Siman kuwa tana fama da zazzaɓi mai tsanani, sai suka roƙi Yesu yă taimake ta.
And he roose vp and came oute of ye sinagoge and entred in to Simons housse. And Simos motherelawe was take with a greate fever and they made intercession to him for her.
39 Sai ya sunkuya kusa da ita, ya kuma tsawata wa zazzaɓin, sai zazzaɓin ya sāke ta. Nan take ta tashi, ta yi musu hidima.
And he stode over her and rebuked the fever: and it leeft her. And immediatly she arose and ministred vnto them.
40 Rana tana fāɗuwa, sai mutane suka yi ta kawo wa Yesu dukan waɗanda suke da cuta iri-iri, sai ya ɗibiya wa kowannensu hannuwansa, ya warkar da su.
When the sonne was doune all they that had sicke take with divers deseases brought them vnto him: and he layde his hondes on every one of them and healed them.
41 Bugu da ƙari, aljanu suka fiffita daga cikin mutane da yawa suna ihu suna cewa, “Kai Ɗan Allah ne!” Amma ya kwaɓe su, ya hana su magana, don sun san cewa shi ne Kiristi.
And devils also cam out of many of them crying and saying: thou arte Christ the sonne of God. And he rebuked them and suffered them not to speake: for they knewe that he was Christ.
42 Da gari yana wayewa, sai Yesu ya je inda ba kowa. Mutane suka yi ta nemansa, da suka zo inda yake, sai suka yi ƙoƙari su hana shi barinsu.
Assone as it was daye he departed and went awaye into a desert place and ye people sought him and came to him and kept him that he shuld not departe from the.
43 Amma ya ce, “Dole in yi wa’azin bisharar mulkin Allah ga sauran garuruwa, saboda wannan ne aka aiko ni.”
And he sayde vnto the: I muste to other cities also preache the kyngdome of God: for therfore am I sent.
44 Sai ya dinga yin wa’azi a majami’un Yahudiya.
And he preached in the synagoges of Galile.

< Luka 4 >