< Luka 4 >
1 Yesu kuwa cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dawo daga Urdun, Ruhu kuma ya kai shi cikin hamada,
And, Jesus, full of Holy Spirit, returned from the Jordan, and was led in the Spirit in the desert,
2 inda kwana arba’in, Iblis ya gwada shi. Bai ci kome ba a cikin kwanakin nan, a ƙarshensu kuwa ya ji yunwa.
forty days, —being tempted by the adversary; and he did eat nothing in those days, —and, when they were concluded, he hungered.
3 Iblis ya ce masa, “In kai Ɗan Allah ne, ka faɗa wa wannan dutse yă zama burodi.”
And the adversary said to him—If thou art God’s, Son, speak unto this stone; that it become bread.
4 Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake, ‘Ba da abinci kaɗai mutum zai rayu ba.’”
And Jesus made answer unto him—It is written: Not, on bread alone, shall, man, live.
5 Iblis ya kai shi can kan wani wuri mai tsawo, ya nunnuna masa a ƙyiftawar ido dukan mulkokin duniya.
And, leading him up, he shewed him all the kingdoms of the inhabited earth, in a moment of time.
6 Ya ce masa, “Zan ba ka dukan ikonsu da darajarsu, gama ni aka danƙa wa, kuma zan bai wa duk wanda na ga dama.
And the adversary said to him—Unto thee, will I give this authority, all together, and their glory; because, unto me, hath it been delivered up, and, to whomsoever I please, I give it:
7 Saboda haka in ka yi mini sujada, dukan wannan zai zama naka.”
Thou, therefore, if thou wilt worship before me, it shall all, be thine.
8 Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake, ‘Ka yi wa Ubangiji Allahnka sujada, kuma shi kaɗai za ka bauta wa.’”
And, answering, Jesus said to him—It is written: The Lord thy God, shalt thou worship, and, unto him alone, render divine service.
9 Sai Iblis, ya kai shi Urushalima ya sa ya tsaya a kan wuri mafi tsayi na haikali ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, ka yi tsalle daga nan zuwa ƙasa.
And he led him into Jerusalem, and set him upon the pinnacle of the temple, —and said [to him]—If thou art God’s, Son, cast thyself, from hence, down;
10 Gama a rubuce yake, “‘Zai umarci mala’ikunsa game da kai, su kiyaye ka da kyau;
for it is written—Unto his messengers, will he give command concerning thee, to keep vigilant watch over thee, —
11 za su tallafe ka da hannuwansu, don kada ka buga ƙafarka a kan dutse.’”
And, On hands, will they take thee up, lest once thou strike, against a stone, thy foot.
12 Yesu ya amsa ya ce, “An ce, ‘Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.’”
And Jesus, answering, said to him—It is said: Thou shalt not put to the test the Lord thy God.
13 Da Iblis ya gama dukan wannan gwajin, ya bar shi sai lokacin da wata dama ta samu.
And, having concluded every temptation, the adversary departed from him until a fitting season.
14 Yesu ya koma Galili cikin ikon Ruhu. Labarinsa kuwa ya bazu ko’ina a ƙauyuka.
And Jesus returned, in the power of the Spirit, into Galilee; and, a report, went out along the whole of the region, concerning him;
15 Ya yi ta koyarwa a majami’unsu, kowa kuwa ya yabe shi.
and, he, began teaching in their synagogues, being glorified by all.
16 Ya tafi Nazaret, inda aka yi renonsa. A ranar Asabbaci kuma, ya shiga majami’a kamar yadda ya saba. Sai ya miƙe don yă yi karatu.
And he came into Nazareth, where he had been brought up, and entered, according to his custom, on the sabbath day, into the synagogue, —and stood up to read.
17 Aka kuwa ba shi naɗaɗɗen littafin annabi Ishaya. Da ya buɗe, sai ya sami wurin da aka rubuta,
And there was handed to him a scroll of the prophet Isaiah; and unfolding the scroll, he found the place where it was written:
18 “Ruhun Ubangiji yana kaina, domin ya shafe ni, in yi wa matalauta wa’azin bishara. Ya aiko ni in yi shelar’yanci ga’yan kurkuku, in kuma buɗe idanun makafi, in ba da’yanci ga waɗanda aka danne.
The Spirit of the Lord, is upon me, because he hath anointed me—to tell glad tidings unto the destitute; He hath sent me forth, —To proclaim, to captives, a release, and, to the blind, a recovering of sight, —to send away the crushed, with a release;
19 In yi shelar shekarar tagomashin Ubangiji.”
To proclaim the welcome year of the Lord.
20 Sai ya naɗe naɗaɗɗen littafin ya mayar wa mai hidimar, ya kuma zauna. Dukan idanun waɗanda suke a majami’ar, suka koma a kansa.
And, folding up the scroll, he handed it to the attendant, and sat down; and, the eyes of all, in the synagogue, were intently fixed upon him;
21 Sai ya fara ce musu, “A yau, Nassin nan, ya cika a kunnenku.”
and he began to be saying to them—This day, is fulfilled this scripture, in your ears.
22 Duk suka yabe shi, suka yi mamakin kalmomin alheri da suke fitowa daga bakinsa. Suka yi tambaya, suna cewa, “Anya, wannan ba ɗan Yusuf ba ne?”
And, all, were bearing witness to him, and marvelling at the words of favour which were proceeding out of his mouth; and they were saying—Is not, this, the, son of Joseph?
23 Yesu ya ce musu, “Tabbatacce, na san za ku faɗa mini karin maganan nan, ‘Likita, warkar da kanka! Ka kuma yi abin da muka ji ka yi a Kafarnahum, a nan garinka.’”
And he said unto them—By all means, ye will speak to me this similitude: Physician! heal, thyself, —Whatsoever things we have heard of coming to pass in Capernaum, do here also, in thine own country.
24 Ya ci gaba, da ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, babu annabin da ake yarda da shi a garinsa.
And he said—Verily, I say unto you, No prophet, is, welcome, in his own country,
25 Ina tabbatar muku a zamanin Iliya, akwai gwauraye da yawa a Isra’ila, sa’ad da aka rufe sararin sama har shekara uku da rabi, aka kuma yi yunwa mai tsanani ko’ina a ƙasar.
And, of a truth, I say unto you—Many widows, were in the days of Elijah, in Israel, when the heaven was shut up three years and six months, when there came a great famine upon all the land;
26 Duk da haka, ba a aiki Iliya ga ko ɗaya a cikinsu ba. Sai dai zuwa ga wata gwauruwa da take a Zarefat, a yankin Sidon.
And, unto none of them, was Elijah sent, save unto Sarepta of Sidonia, unto a woman that was a widow.
27 Akwai kuma mutane da yawa a Isra’ila masu kuturta a zamanin annabi Elisha, amma ba ko ɗayansu da aka tsarkake sai Na’aman mutumin Suriyan nan kaɗai.”
And, many lepers, were in Israel, in the time of Elisha the prophet, and, not one of them, was cleansed, save Naaman the Syrian.
28 Dukan mutanen da suke cikin majami’a suka fusata ƙwarai da jin wannan.
And all were filled with wrath, in the synagogue, as they heard these things.
29 Suka tashi, suka fitar da Yesu bayan gari, suka kai shi goshin tudun da aka gina garin, don su ture shi ƙasa,
And, rising up, they thrust him forth outside the city, and led him as far as a brow of the hill on which their city was built, —so that they might throw him down headlong.
30 amma sai ya bi ta tsakiyar taron ya yi tafiyarsa.
But, he, passing through the midst of them, went his way.
31 Sai ya tafi Kafarnahum, wani gari a Galili, a ranar Asabbaci kuma, ya fara koya wa mutane.
And he came down into Capernaum, a city of Galilee. And he was teaching them on the sabbath;
32 Suka yi ta mamakin koyarwarsa, domin saƙonsa yana da iko.
and they were being struck with astonishment at his teaching, because, with authority, was his word.
33 A cikin majami’ar, akwai wani mutum mai aljani, wani mugun ruhu. Mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce,
And, in the synagogue, was a man having a spirit of an impure demon; and he cried out with a loud voice—
34 “Wayyo! Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne don ka hallaka mu? Na san wane ne kai, Mai Tsarki na Allah!”
Let be! What have we in common with thee, O Jesus, Nazarene! Hast thou come to destroy us? I know thee, who thou art, —The Holy One of God.
35 Yesu ya tsawata masa da ƙarfin cewa, “Yi shiru! Ka fita daga cikinsa!” Sai aljanin ya fyaɗa mutumin da ƙasa a gabansu duka, sa’an nan ya fita, ya bar shi ba wani rauni.
And Jesus rebuked it, saying—Hold thy peace! and go forth from him. And the demon, throwing him into the midst, went forth from him, doing him no hurt.
36 Dukan mutanen suka yi mamaki, suka ce wa junansu, “Wace irin koyarwa ce haka? Da ƙarfi da iko, yana ba wa mugayen ruhohin umarni suna kuma fita!”
And amazement came upon all, and they began to converse one with another, saying—What is this word, that, with authority and power, he giveth orders unto the impure spirits, and they go forth?
37 Labarinsa kuwa ya bazu ko’ina a cikin ƙasar.
And a noise concerning him began to go out into every place of the country around.
38 Yesu ya fita daga majami’ar, ya tafi gidan Siman. Surukar Siman kuwa tana fama da zazzaɓi mai tsanani, sai suka roƙi Yesu yă taimake ta.
And, rising up, from the synagogue, he went into the house of Simon. Now, the mother-in-law of Simon, was in distress with a great fever; and they made request to him concerning her.
39 Sai ya sunkuya kusa da ita, ya kuma tsawata wa zazzaɓin, sai zazzaɓin ya sāke ta. Nan take ta tashi, ta yi musu hidima.
And, standing over her, he rebuked the fever, and it left her; and, instantly arising, she began to minister unto them.
40 Rana tana fāɗuwa, sai mutane suka yi ta kawo wa Yesu dukan waɗanda suke da cuta iri-iri, sai ya ɗibiya wa kowannensu hannuwansa, ya warkar da su.
But, as the sun was going in, they one and all, as many as had any sick with divers diseases, brought them unto him; and, he, upon each one of them laying, his hands, was curing them.
41 Bugu da ƙari, aljanu suka fiffita daga cikin mutane da yawa suna ihu suna cewa, “Kai Ɗan Allah ne!” Amma ya kwaɓe su, ya hana su magana, don sun san cewa shi ne Kiristi.
And demons also were going forth from many; crying aloud, and saying—Thou, art the Son of God. And, rebuking them, he suffered them not be talking; because they knew him to be, The Christ.
42 Da gari yana wayewa, sai Yesu ya je inda ba kowa. Mutane suka yi ta nemansa, da suka zo inda yake, sai suka yi ƙoƙari su hana shi barinsu.
And, when it was day, going forth, he journeyed into a desert place; and, the multitudes, were seeking after him, and they came unto him, and would have detained him, that he might not depart from them.
43 Amma ya ce, “Dole in yi wa’azin bisharar mulkin Allah ga sauran garuruwa, saboda wannan ne aka aiko ni.”
But, he, said unto them—To the other cities also, I must needs tell the good-news of the kingdom of God, because, hereunto, was I sent forth.
44 Sai ya dinga yin wa’azi a majami’un Yahudiya.
And he was proclaiming in the cities of Judaea.