< Luka 3 >
1 A shekara ta goma sha biyar ta mulkin Kaisar Tiberiyus, a lokacin Buntus Bilatus ne gwamnar Yahudiya, Hiridus kuma yana sarautar Galili, ɗan’uwansa Filibus yana sarautar Ituriya da Tarakunitis, Lisaniyas kuma yana sarautar Abiline.
And in the fifteenth year of the government of Tiberius Caesar — Pontius Pilate being governor of Judea, and Herod tetrarch of Galilee, and Philip his brother, tetrarch of Ituraea and of the region of Trachonitis, and Lysanias tetrarch of Abilene —
2 A lokacin ne Annas da Kayifas suke manyan firistoci. Sai maganar Allah ta zo wa Yohanna, ɗan Zakariya a hamada.
Annas and Caiaphas being chief priests — there came a word of God unto John the son of Zacharias, in the wilderness,
3 Ya zaga dukan ƙasar da take kewaye da Urdun, yana wa’azin baftismar tuba don gafarar zunubai.
and he came to all the region round the Jordan, proclaiming a baptism of reformation — to remission of sins,
4 Kamar yadda yake a rubuce a littafin annabi Ishaya. “Muryar mai kira a hamada, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.
as it hath been written in the scroll of the words of Isaiah the prophet, saying, 'A voice of one crying in the wilderness, Prepare ye the way of the Lord, straight make ye His paths;
5 Za a cike kowane kwari, a farfashe kowane dutse da kowane tudu. Za a miƙe hanyoyin da suka karkace, a gyaggyara hanyoyi masu gargaɗa su zama sumul.
every valley shall be filled, and every mountain and hill shall be made low, and the crooked shall become straightness, and the rough become smooth ways;
6 Dukan’yan Adam kuwa za su ga ceton Allah!’”
and all flesh shall see the salvation of God.'
7 Yohanna ya ce wa taron da suke zuwa domin yă yi musu baftisma, “Ku macizai! Wa ya gargaɗe ku, ku guje wa fushin nan mai zuwa?
Then said he to the multitudes coming forth to be baptised by him, 'Brood of vipers! who did prompt you to flee from the coming wrath?
8 Ku yi ayyukan da suka dace da tuba. Kada ma ku yi tunani za ku iya ce wa kanku, ‘Ai, muna da mahaifinmu Ibrahim.’ Ina gaya muku cewa daga cikin duwatsun nan Allah zai iya tā da’ya’ya wa Ibrahim.
make, therefore, fruits worthy of the reformation, and begin not to say within yourselves, We have a father — Abraham; for I say to you, that God is able out of these stones to raise children to Abraham;
9 An riga an sa bakin gatari a gindin itatuwa, kuma duk itacen da bai ba da’ya’ya masu kyau ba, za a sare shi a jefa cikin wuta.”
and already also the axe unto the root of the trees is laid, every tree, therefore, not making good fruit is cut down, and to fire it is cast.'
10 Sai taron suka tambaye shi, suka ce “Me za mu yi ke nan?”
And the multitudes were questioning him, saying, 'What, then, shall we do?'
11 Ya amsa ya ce, “Ya kamata, mutumin da yake da riguna biyu, yă raba da wanda ba shi da riga, mai abinci kuma yă yi haka.”
and he answering saith to them, 'He having two coats — let him impart to him having none, and he having victuals — in like manner let him do.'
12 Masu karɓar haraji ma suka zo, domin a yi musu baftisma. Suka yi tambaya, suka ce “Malam, me ya kamata mu yi?”
And there came also tax-gatherers to be baptised, and they said unto him, 'Teacher, what shall we do?'
13 Ya ce musu, “Kada ku karɓa fiye da abin da aka ce a karɓa.”
and he said unto them, 'Exact no more than that directed you.'
14 Sai waɗansu sojoji suka tambaye shi, “Mu fa? Me ya kamata mu yi?” Sai ya amsa ya ce, “Kada ku ƙwace kuɗin mutane, kada kuma ku yi shaidar ƙarya. Ku yi haƙuri da abin da ake biyanku.”
And questioning him also were those warring, saying, 'And we, what shall we do?' and he said unto them, 'Do violence to no one, nor accuse falsely, and be content with your wages.'
15 Mutane suka zuba ido, suna kuma tunani a zuciyarsu, ko Yohanna ne Kiristi wanda ake sauraron zuwansa.
And the people are looking forward, and all are reasoning in their hearts concerning John, whether or not he may be the Christ;
16 Yohanna ya amsa musu duka ya ce, “Ina muku baftisma da ruwa. Amma wani wanda ya fi ni iko yana zuwa, ban ma isa in kunce igiyar takalmansa ba. Shi zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da wuta kuma.
John answered, saying to all, 'I indeed with water do baptise you, but he cometh who is mightier than I, of whom I am not worthy to loose the latchet of his sandals — he shall baptise you with the Holy Spirit and with fire;
17 Matankaɗinsa yana a hannunsa don yă tankaɗe sussukarsa ya kuma tattara alkama cikin rumbunsa, amma zai ƙone yayin da wutar da ba a iya kashewa.”
whose winnowing shovel [is] in his hand, and he will thoroughly cleanse his floor, and will gather the wheat to his storehouse, and the chaff he will burn with fire unquenchable.'
18 Da kalmomi masu yawa Yohanna ya yi wa mutane gargaɗi, ya kuma yi musu wa’azin bishara.
And, therefore, indeed with many other things, exhorting, he was proclaiming good news to the people,
19 Amma da Yohanna ya tsawata wa Hiridus mai mulki saboda Hiridiyas, matar ɗan’uwansa, da kuma dukan sauran mugayen abubuwan da ya yi,
and Herod the tetrarch, being reproved by him concerning Herodias the wife of Philip his brother, and concerning all the evils that Herod did,
20 Hiridus dai ya ƙara ɓata al’amarin. Ya sa a kulle Yohanna a kurkuku.
added also this to all, that he shut up John in the prison.
21 Sa’ad da ake wa dukan mutane baftisma, sai aka yi wa Yesu shi ma. Da yana cikin addu’a, sai sama ya buɗe,
And it came to pass, in all the people being baptised, Jesus also being baptised, and praying, the heaven was opened,
22 Ruhu Mai Tsarki kuma ya sauko masa a wata siffa, kamar kurciya. Sai murya ta fito daga sama, ta ce, “Kai ne Ɗana, wanda nake ƙauna, kai ne kuma kana faranta mini zuciya ƙwarai.”
and the Holy Spirit came down in a bodily appearance, as if a dove, upon him, and a voice came out of heaven, saying, 'Thou art My Son — the Beloved, in thee I did delight.'
23 To, Yesu kansa yana da shekaru kusan talatin da haihuwa sa’ad da ya fara aikinsa. An ɗauka shi ɗan Yusuf ne, ɗan Heli,
And Jesus himself was beginning to be about thirty years of age, being, as was supposed, son of Joseph,
24 ɗan Mattat, ɗan Lawi, ɗan Melki, ɗan Yannai, ɗan Yusuf,
the [son] of Eli, the [son] of Matthat, the [son] of Levi, the [son] of Melchi, the [son] of Janna, the [son] of Joseph,
25 ɗan Mattatiyas, ɗan Amos, ɗan Nahum, ɗan Esli, ɗan Naggai,
the [son] of Mattathias, the [son] of Amos, the [son] of Naum, the [son] of Esli,
26 ɗan Ma’at, ɗan Mattatiyas, ɗan Semeyin, ɗan Yosek, ɗan Yoda,
the [son] of Naggai, the [son] of Maath, the [son] of Mattathias, the [son] of Semei, the [son] of Joseph, the [son] of Juda,
27 ɗan Yowanan, ɗan Resa, ɗan Zerubbabel, ɗan Sheyaltiyel, ɗan Neri,
the [son] of Joanna, the [son] of Rhesa, the [son] of Zerubbabel, the [son] of Shealtiel,
28 ɗan Melki, ɗan Addi, ɗan Kosam, ɗan Elmadam, ɗan Er,
the [son] of Neri, the [son] of Melchi, the [son] of Addi, the [son] of Cosam, the [son] of Elmodam, the [son] of Er,
29 ɗan Yoshuwa, ɗan Eliyezer, ɗan Yorim, ɗan Mattat, ɗan Lawi,
the [son] of Jose, the [son] of Eliezer, the [son] of Jorim, the [son] of Matthat,
30 ɗan Simeyon, ɗan Yahuda, ɗan Yusuf, ɗan Yonam, ɗan Eliyakim,
the [son] of Levi, the [son] of Simeon, the [son] of Juda, the [son] of Joseph, the [son] of Jonan, the [son] of Eliakim,
31 ɗan Meleya, ɗan Menna, ɗan Mattata, ɗan Natan, ɗan Dawuda,
the [son] of Melea, the [son] of Mainan, the [son] of Mattatha, the [son] of Nathan,
32 ɗan Yesse, ɗan Obed, ɗan Bowaz, ɗan Salmon, ɗan Nashon,
the [son] of David, the [son] of Jesse, the [son] of Obed, the [son] of Booz, the [son] of Salmon, the [son] of Nahshon,
33 ɗan Amminadab, ɗan Ram, ɗan Hezron, ɗan Ferez, ɗan Yahuda,
the [son] of Amminadab, the [son] of Aram, the [son] of Esrom, the [son] of Pharez,
34 ɗan Yaƙub, ɗan Ishaku, ɗan Ibrahim, ɗan Tera, ɗan Nahor,
the [son] of Judah, the [son] of Jacob, the [son] of Isaac, the [son] of Abraham, the [son] of Terah, the [son] of Nahor,
35 ɗan Serug, ɗan Reyu, ɗan Feleg, ɗan Eber, ɗan Sala,
the [son] of Serug, the [son] of Reu, the [son] of Peleg, the [son] of Eber,
36 ɗan Kainan, ɗan Arfakshad, ɗan Shem, ɗan Nuhu, ɗan Lamek,
the [son] of Salah, the [son] of Cainan, the [son] of Arphaxad, the [son] of Shem, the [son] of Noah, the [son] of Lamech,
37 ɗan Metusela, ɗan Enok, ɗan Yared, ɗan Mahalalel, ɗan Kainan,
the [son] of Methuselah, the [son] of Enoch, the [son] of Jared, the [son] of Mahalaleel,
38 ɗan Enosh, ɗan Shitu, ɗan Adamu, ɗan Allah.
the [son] of Cainan, the [son] of Enos, the [son] of Seth, the [son] of Adam, the [son] of God.