< Luka 3 >

1 A shekara ta goma sha biyar ta mulkin Kaisar Tiberiyus, a lokacin Buntus Bilatus ne gwamnar Yahudiya, Hiridus kuma yana sarautar Galili, ɗan’uwansa Filibus yana sarautar Ituriya da Tarakunitis, Lisaniyas kuma yana sarautar Abiline.
Now in the fifteenth year of the reign of Tiberius Caesar, when Pontius Pilate was governor of Judea, and Herod was tetrarch of Galilee, his brother Philip, tetrarch of Ituraea and Trachonitis, and Lysanias, tetrarch of Abilene;
2 A lokacin ne Annas da Kayifas suke manyan firistoci. Sai maganar Allah ta zo wa Yohanna, ɗan Zakariya a hamada.
during the high priesthood of Annas and Caiaphas, the word of God came to John, the son of Zachariah, in the Desert.
3 Ya zaga dukan ƙasar da take kewaye da Urdun, yana wa’azin baftismar tuba don gafarar zunubai.
And Johnwent into all the region about the Jordan, preaching a baptism of repentance for the remission of sins.
4 Kamar yadda yake a rubuce a littafin annabi Ishaya. “Muryar mai kira a hamada, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.
As it is written in the book of the prophet Isaiah. The voice of one crying in the desert, Prepare the way for God, make straight paths for him.
5 Za a cike kowane kwari, a farfashe kowane dutse da kowane tudu. Za a miƙe hanyoyin da suka karkace, a gyaggyara hanyoyi masu gargaɗa su zama sumul.
Every ravine shall be filled up, Every hill and mountain shall be laid low, The crooked shall be made straight, And the rough roads smooth;
6 Dukan’yan Adam kuwa za su ga ceton Allah!’”
And all flesh shall see the salvation of God.
7 Yohanna ya ce wa taron da suke zuwa domin yă yi musu baftisma, “Ku macizai! Wa ya gargaɗe ku, ku guje wa fushin nan mai zuwa?
So Johnused to say to the crowd of those who were going out to be baptized by him. "You breed of vipers, who has warned you to flee from the wrath to come?
8 Ku yi ayyukan da suka dace da tuba. Kada ma ku yi tunani za ku iya ce wa kanku, ‘Ai, muna da mahaifinmu Ibrahim.’ Ina gaya muku cewa daga cikin duwatsun nan Allah zai iya tā da’ya’ya wa Ibrahim.
Then bring forth fruit befitting your penitence, and do not begin to say to yourselves, "We have Abraham as our father." I tell you that God is able to raise up sons to Abraham out of these stones.
9 An riga an sa bakin gatari a gindin itatuwa, kuma duk itacen da bai ba da’ya’ya masu kyau ba, za a sare shi a jefa cikin wuta.”
And now truly the axe is already laid at the root of the trees. So every tree which is not bearing good fruit is cut down and thrown into the fire."
10 Sai taron suka tambaye shi, suka ce “Me za mu yi ke nan?”
And the crowd began to ask him questions. "What shall we do then?" they asked. In reply he said to them.
11 Ya amsa ya ce, “Ya kamata, mutumin da yake da riguna biyu, yă raba da wanda ba shi da riga, mai abinci kuma yă yi haka.”
"If you have two shirts share with him who has none; and let him who has food do the same."
12 Masu karɓar haraji ma suka zo, domin a yi musu baftisma. Suka yi tambaya, suka ce “Malam, me ya kamata mu yi?”
There came to him publicans also to be baptized, and they said to him, "Master, what must we do?"
13 Ya ce musu, “Kada ku karɓa fiye da abin da aka ce a karɓa.”
And he said to them, "Exact no more than the sum allowed you."
14 Sai waɗansu sojoji suka tambaye shi, “Mu fa? Me ya kamata mu yi?” Sai ya amsa ya ce, “Kada ku ƙwace kuɗin mutane, kada kuma ku yi shaidar ƙarya. Ku yi haƙuri da abin da ake biyanku.”
The soldiers also repeatedly questioned him, saying, "And we, what shall we do?" "Do not intimidate any one," he replied, "nor lay false charges, and be content with your pay."
15 Mutane suka zuba ido, suna kuma tunani a zuciyarsu, ko Yohanna ne Kiristi wanda ake sauraron zuwansa.
And while the people were in expectation, and all men were debating in their hearts about John,
16 Yohanna ya amsa musu duka ya ce, “Ina muku baftisma da ruwa. Amma wani wanda ya fi ni iko yana zuwa, ban ma isa in kunce igiyar takalmansa ba. Shi zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da wuta kuma.
whether perhaps he were the Christ, Johnanswered, saying to all of them. "I indeed am baptizing you in water, but One is coming after me, mightier than I, whose shoe-latchet I am not worthy to unloose. He shall baptize you in the Holy Ghost and in fire.
17 Matankaɗinsa yana a hannunsa don yă tankaɗe sussukarsa ya kuma tattara alkama cikin rumbunsa, amma zai ƙone yayin da wutar da ba a iya kashewa.”
He has his fan in his hand to cleanse his threshing-floor thoroughly, and to gather the wheat into his storehouse, but the chaff will he burn with unquenchable fire."
18 Da kalmomi masu yawa Yohanna ya yi wa mutane gargaɗi, ya kuma yi musu wa’azin bishara.
With many other exhortations then Johndeclared the gospel to the people;
19 Amma da Yohanna ya tsawata wa Hiridus mai mulki saboda Hiridiyas, matar ɗan’uwansa, da kuma dukan sauran mugayen abubuwan da ya yi,
but Herod, the Tetrarch, when reproved by him because of Herodias, his brother’s wife, and because of all the wicked deeds that he had done,
20 Hiridus dai ya ƙara ɓata al’amarin. Ya sa a kulle Yohanna a kurkuku.
added yet this above them all that he shut up Johnin prison.
21 Sa’ad da ake wa dukan mutane baftisma, sai aka yi wa Yesu shi ma. Da yana cikin addu’a, sai sama ya buɗe,
Now after all the people had been baptized, and Jesus himself had been baptized and was praying,
22 Ruhu Mai Tsarki kuma ya sauko masa a wata siffa, kamar kurciya. Sai murya ta fito daga sama, ta ce, “Kai ne Ɗana, wanda nake ƙauna, kai ne kuma kana faranta mini zuciya ƙwarai.”
heaven opened, and the Holy Spirit, in bodily form like a dove, descended upon him. and a voice came out of heaven, saying. "Thou art my Son, dearly beloved; in thee is my delight."
23 To, Yesu kansa yana da shekaru kusan talatin da haihuwa sa’ad da ya fara aikinsa. An ɗauka shi ɗan Yusuf ne, ɗan Heli,
And Jesus himself when he began to teach was about thirty years of age. He was the son (as it was supposed) of Joseph, the son of Heli,
24 ɗan Mattat, ɗan Lawi, ɗan Melki, ɗan Yannai, ɗan Yusuf,
son of Matthat, son of Levi, son of Melchi,
25 ɗan Mattatiyas, ɗan Amos, ɗan Nahum, ɗan Esli, ɗan Naggai,
son of Matthias, son of Nahum, son of Esli,
26 ɗan Ma’at, ɗan Mattatiyas, ɗan Semeyin, ɗan Yosek, ɗan Yoda,
son of Mahath, son of Matthias, son of Semein, son of Joseph, son of Joda,
27 ɗan Yowanan, ɗan Resa, ɗan Zerubbabel, ɗan Sheyaltiyel, ɗan Neri,
son of Johann, son of Resa, son of Zerubbabel, son of Shealtiel, son of Neri,
28 ɗan Melki, ɗan Addi, ɗan Kosam, ɗan Elmadam, ɗan Er,
son of Melchi, son of Addi, son of Cosam, son of Elmadam, son of Er,
29 ɗan Yoshuwa, ɗan Eliyezer, ɗan Yorim, ɗan Mattat, ɗan Lawi,
son of Joshua, son of Eliezar, son of Jorim, son of Mathat, son of Levi,
30 ɗan Simeyon, ɗan Yahuda, ɗan Yusuf, ɗan Yonam, ɗan Eliyakim,
son of Symeon, son of Judah, son of Joseph, son of Jonan, son of Eliakim,
31 ɗan Meleya, ɗan Menna, ɗan Mattata, ɗan Natan, ɗan Dawuda,
son of Melea, son of Menna, son of Mattatha, son of Nathan, son of David,
32 ɗan Yesse, ɗan Obed, ɗan Bowaz, ɗan Salmon, ɗan Nashon,
son of Jesse, son of Obed, son of Boaz, son of Salmon, son of Nahshon,
33 ɗan Amminadab, ɗan Ram, ɗan Hezron, ɗan Ferez, ɗan Yahuda,
son of Amminadab, son of Admin, son of Arni, son of Hezron, son of Perez, son of Judah,
34 ɗan Yaƙub, ɗan Ishaku, ɗan Ibrahim, ɗan Tera, ɗan Nahor,
son of Jacob, son of Isaac, son of Abraham, son of Terah, son of Nahor,
35 ɗan Serug, ɗan Reyu, ɗan Feleg, ɗan Eber, ɗan Sala,
son of Serug, son of Reu, son of Peleg, son of Eber, son of Shelah,
36 ɗan Kainan, ɗan Arfakshad, ɗan Shem, ɗan Nuhu, ɗan Lamek,
son of Cainan, son of Arpachshad, son of Shem, son of Noah, son of Lamech,
37 ɗan Metusela, ɗan Enok, ɗan Yared, ɗan Mahalalel, ɗan Kainan,
son of Methuselah, son of Enoch, son of Jared, son of Mahalel, son of Kenan,
38 ɗan Enosh, ɗan Shitu, ɗan Adamu, ɗan Allah.
son of Enos, son of Seth, son of Adam, son of God.

< Luka 3 >