< Luka 24 >

1 Da sassafe a ranar farko ta mako, matan suka je kabarin, da kayan ƙanshin da suka shirya.
atha saptāhaprathamadine'tipratyūṣe tā yoṣitaḥ sampāditaṁ sugandhidravyaṁ gṛhītvā tadanyābhiḥ kiyatībhiḥ strībhiḥ saha śmaśānaṁ yayuḥ|
2 Suka iske an riga an gungurar da dutsen daga bakin kabarin.
kintu śmaśānadvārāt pāṣāṇamapasāritaṁ dṛṣṭvā
3 Amma da suka shiga ciki, ba su iske jikin Ubangiji Yesu ba.
tāḥ praviśya prabho rdehamaprāpya
4 Yayinda suna cikin tunani a kan wannan, nan take, ga waɗansu mutum biyu tsaye kusa da su, sanye da kaya masu ƙyalli, kamar walƙiya.
vyākulā bhavanti etarhi tejomayavastrānvitau dvau puruṣau tāsāṁ samīpe samupasthitau
5 A cikin tsoro, matan suka fāɗi da fuskokinsu a ƙasa, amma mutanen suka ce musu, “Me ya sa kuke neman mai rai a cikin matattu?
tasmāttāḥ śaṅkāyuktā bhūmāvadhomukhyasyasthuḥ| tadā tau tā ūcatu rmṛtānāṁ madhye jīvantaṁ kuto mṛgayatha?
6 Ba ya nan, ya tashi! Ku tuna yadda ya gaya muku tun yana tare da ku a Galili cewa,
sotra nāsti sa udasthāt|
7 ‘Dole a ba da Ɗan Mutum ga hannun masu zunubi, a kuma gicciye shi, a rana ta uku kuma a tashe shi.’”
pāpināṁ kareṣu samarpitena kruśe hatena ca manuṣyaputreṇa tṛtīyadivase śmaśānādutthātavyam iti kathāṁ sa galīli tiṣṭhan yuṣmabhyaṁ kathitavān tāṁ smarata|
8 Sai suka tuna da maganarsa.
tadā tasya sā kathā tāsāṁ manaḥsu jātā|
9 Da suka dawo daga kabarin, sai suka faɗa wa Sha Ɗayan nan da sauransu, dukan waɗannan abubuwa.
anantaraṁ śmaśānād gatvā tā ekādaśaśiṣyādibhyaḥ sarvvebhyastāṁ vārttāṁ kathayāmāsuḥ|
10 Matan da suka gaya wa manzannin waɗannan abubuwa su ne, Maryamu Magdalin, da Yowanna, da Maryamu uwar Yaƙub, da waɗansu da suke tare da su.
magdalīnīmariyam, yohanā, yākūbo mātā mariyam tadanyāḥ saṅginyo yoṣitaśca preritebhya etāḥ sarvvā vārttāḥ kathayāmāsuḥ
11 Amma ba su gaskata matan ba, domin sun ɗauki kalmominsu wani zancen banza ne.
kintu tāsāṁ kathām anarthakākhyānamātraṁ buddhvā kopi na pratyait|
12 Duk da haka, Bitrus ya tashi a guje zuwa kabarin. Da ya sunkuya, sai ya ga ƙyallayen lilin kaɗai a kwance. Sai ya koma yana tunani a ransa, a kan abin da ya faru.
tadā pitara utthāya śmaśānāntikaṁ dadhāva, tatra ca prahvo bhūtvā pārśvaikasthāpitaṁ kevalaṁ vastraṁ dadarśa; tasmādāścaryyaṁ manyamāno yadaghaṭata tanmanasi vicārayan pratasthe|
13 A wannan rana kuma, biyu daga cikinsu suna tafiya zuwa wani ƙauye, da ake kira Emmawus, da suke kusan mil bakwai daga Urushalima.
tasminneva dine dvau śiyyau yirūśālamaścatuṣkrośāntaritam immāyugrāmaṁ gacchantau
14 Suna magana da juna a kan dukan abubuwan da suka faru.
tāsāṁ ghaṭanānāṁ kathāmakathayatāṁ
15 Da suna magana, kuma suna tattauna waɗannan abubuwa da junansu, sai Yesu da kansa ya zo yana tafiya tare da su.
tayorālāpavicārayoḥ kāle yīśurāgatya tābhyāṁ saha jagāma
16 Amma ba a ba su ikon gane shi ba.
kintu yathā tau taṁ na paricinutastadarthaṁ tayo rdṛṣṭiḥ saṁruddhā|
17 Sai ya tambaye, su ya ce, “Mene ne kuke tattaunawa da juna a cikin tafiyarku?” Suka tsaya shiru, da damuwa a fuskarsu.
sa tau pṛṣṭavān yuvāṁ viṣaṇṇau kiṁ vicārayantau gacchathaḥ?
18 Ɗaya daga cikinsu, mai suna Kiliyobas, ya tambaye shi ya ce, “Ashe, kai baƙo ne a Urushalima, da ba ka san abubuwan da suka faru a can, a cikin kwanakin nan ba?”
tatastayoḥ kliyapānāmā pratyuvāca yirūśālamapure'dhunā yānyaghaṭanta tvaṁ kevalavideśī kiṁ tadvṛttāntaṁ na jānāsi?
19 Sai ya yi tambaya, “Waɗanne abubuwa?” Suka amsa suka ce, “Game da Yesu Banazare. Shi annabi ne, mai iko ne kuma cikin ayyukansa da maganarsa, a gaban Allah da kuma dukan mutane.
sa papraccha kā ghaṭanāḥ? tadā tau vaktumārebhāte yīśunāmā yo nāsaratīyo bhaviṣyadvādī īśvarasya mānuṣāṇāñca sākṣāt vākye karmmaṇi ca śaktimānāsīt
20 Manyan firistoci da masu mulkinmu sun ba da shi a yi masa hukuncin mutuwa, suka kuwa gicciye shi.
tam asmākaṁ pradhānayājakā vicārakāśca kenāpi prakāreṇa kruśe viddhvā tasya prāṇānanāśayan tadīyā ghaṭanāḥ;
21 Amma da, muna sa zuciya cewa, shi ne wanda zai fanshi Isra’ila. Bugu da ƙari kuma yau kwana uku ke nan tun da wannan abin ya faru.
kintu ya isrāyelīyalokān uddhārayiṣyati sa evāyam ityāśāsmābhiḥ kṛtā|tadyathā tathāstu tasyā ghaṭanāyā adya dinatrayaṁ gataṁ|
22 Har wa yau, waɗansu daga cikin matanmu sun ba mu mamaki. Sun je kabarin da sassafen nan,
adhikantvasmākaṁ saṅginīnāṁ kiyatstrīṇāṁ mukhebhyo'sambhavavākyamidaṁ śrutaṁ;
23 amma ba su sami jikinsa ba. Sun dawo sun faɗa mana cewa, sun ga wahayi na mala’iku, da suka ce yana da rai.
tāḥ pratyūṣe śmaśānaṁ gatvā tatra tasya deham aprāpya vyāghuṭyetvā proktavatyaḥ svargīsadūtau dṛṣṭāvasmābhistau cāvādiṣṭāṁ sa jīvitavān|
24 Sa’an nan, waɗansu abokanmu suka je kabarin, suka kuma tarar da kome kamar yadda matan suka faɗa, amma shi, ba su gan shi ba.”
tatosmākaṁ kaiścit śmaśānamagamyata te'pi strīṇāṁ vākyānurūpaṁ dṛṣṭavantaḥ kintu taṁ nāpaśyan|
25 Sai ya ce musu, “Ashe, ku marasa azanci ne, masu nauyin zuciyar gaskata, da dukan abin da annabawa suka faɗa!
tadā sa tāvuvāca, he abodhau he bhaviṣyadvādibhiruktavākyaṁ pratyetuṁ vilambamānau;
26 Ai, dole Kiristi yă sha waɗannan wahalolin, kafin yă shiga ɗaukakarsa.
etatsarvvaduḥkhaṁ bhuktvā svabhūtiprāptiḥ kiṁ khrīṣṭasya na nyāyyā?
27 Sai ya fara bayyana musu daga Musa da dukan Annabawa, abin da dukan Nassi ya faɗa a kansa.”
tataḥ sa mūsāgranthamārabhya sarvvabhaviṣyadvādināṁ sarvvaśāstre svasmin likhitākhyānābhiprāyaṁ bodhayāmāsa|
28 Da suka yi kusa da ƙauyen da za su, sai Yesu ya yi kamar zai ci gaba.
atha gamyagrāmābhyarṇaṁ prāpya tenāgre gamanalakṣaṇe darśite
29 Amma suka matsa masa suka ce, “Sauka wurinmu, don dare ya kusa, rana ta kusa fāɗuwa.” Sai ya sauka wurinsu.
tau sādhayitvāvadatāṁ sahāvābhyāṁ tiṣṭha dine gate sati rātrirabhūt; tataḥ sa tābhyāṁ sārddhaṁ sthātuṁ gṛhaṁ yayau|
30 Da ya zauna a tebur tare da su, sai ya ɗauki burodi, ya yi godiya, ya kakkarya ya fara ba su.
paścādbhojanopaveśakāle sa pūpaṁ gṛhītvā īśvaraguṇān jagāda tañca bhaṁktvā tābhyāṁ dadau|
31 Sa’an nan idanunsu suka buɗe, suka gane shi. Sai ya ɓace musu.
tadā tayo rdṛṣṭau prasannāyāṁ taṁ pratyabhijñatuḥ kintu sa tayoḥ sākṣādantardadhe|
32 Suka tambayi juna, “Ashe, shi ya sa zukatanmu suka kuna a cikinmu, sa’ad da yake magana da mu a hanya, yana bayyana mana Nassi.”
tatastau mithobhidhātum ārabdhavantau gamanakāle yadā kathāmakathayat śāstrārthañcabodhayat tadāvayo rbuddhiḥ kiṁ na prājvalat?
33 Suka tashi nan da nan suka koma Urushalima. A can suka sami Sha Ɗayan nan da waɗanda suke tare da su a wuri ɗaya,
tau tatkṣaṇādutthāya yirūśālamapuraṁ pratyāyayatuḥ, tatsthāne śiṣyāṇām ekādaśānāṁ saṅgināñca darśanaṁ jātaṁ|
34 suna cewa, “Gaskiya ne! Ubangiji ya tashi, ya kuma bayyana ga Siman”
te procuḥ prabhurudatiṣṭhad iti satyaṁ śimone darśanamadācca|
35 Sai su biyun nan suka ba da labarin abin da ya faru a hanya, da kuma yadda suka gane Yesu yayinda ya kakkarya burodin.
tataḥ pathaḥ sarvvaghaṭanāyāḥ pūpabhañjanena tatparicayasya ca sarvvavṛttāntaṁ tau vaktumārebhāte|
36 Suna cikin wannan zance, sai ga Yesu da kansa tsaye a tsakiyarsu. Sai ya ce musu, “Salama a gare ku!”
itthaṁ te parasparaṁ vadanti tatkāle yīśuḥ svayaṁ teṣāṁ madhya protthaya yuṣmākaṁ kalyāṇaṁ bhūyād ityuvāca,
37 Suka firgita, suka tsorota, suna tsammani fatalwa ce suka gani.
kintu bhūtaṁ paśyāma ityanumāya te samudvivijire treṣuśca|
38 Sai ya ce musu, “Don me kuke damuwa, kuke kuma shakka a zuciyarku?
sa uvāca, kuto duḥkhitā bhavatha? yuṣmākaṁ manaḥsu sandeha udeti ca kutaḥ?
39 Ku duba hannuwana da ƙafafuna. Ai, ni ne da kaina! Ku taɓa ni ku ji, ai, fatalwa ba ta da nama da ƙashi, yadda kuke gani nake da su.”
eṣohaṁ, mama karau paśyata varaṁ spṛṣṭvā paśyata, mama yādṛśāni paśyatha tādṛśāni bhūtasya māṁsāsthīni na santi|
40 Da ya faɗi haka, sai ya nuna musu hannuwansa da ƙafafunsa.
ityuktvā sa hastapādān darśayāmāsa|
41 Kuma har yanzu, suna cikin rashin gaskatawa, saboda murna da mamaki, sai ya tambaye su, “Kuna da abinci a nan?”
te'sambhavaṁ jñātvā sānandā na pratyayan| tataḥ sa tān papraccha, atra yuṣmākaṁ samīpe khādyaṁ kiñcidasti?
42 Suka ba shi ɗan gasasshen kifi,
tataste kiyaddagdhamatsyaṁ madhu ca daduḥ
43 ya karɓa ya ci a gabansu.
sa tadādāya teṣāṁ sākṣād bubhuje
44 Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da na gaya muku tun ina tare da ku cewa, dole a cika kome da aka rubuta game da ni, a cikin Dokar Musa, da Annabawa, da kuma Zabura.”
kathayāmāsa ca mūsāvyavasthāyāṁ bhaviṣyadvādināṁ grantheṣu gītapustake ca mayi yāni sarvvāṇi vacanāni likhitāni tadanurūpāṇi ghaṭiṣyante yuṣmābhiḥ sārddhaṁ sthitvāhaṁ yadetadvākyam avadaṁ tadidānīṁ pratyakṣamabhūt|
45 Sai ya wayar da tunaninsu don su fahimci Nassi.
atha tebhyaḥ śāstrabodhādhikāraṁ datvāvadat,
46 Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da aka rubuta, cewa dole Kiristi yă sha wahala, a rana ta uku kuma yă tashi daga matattu.
khrīṣṭenetthaṁ mṛtiyātanā bhoktavyā tṛtīyadine ca śmaśānādutthātavyañceti lipirasti;
47 Kuma a cikin sunansa za a yi wa’azin tuba da gafarar zunubai, ga dukan ƙasashe. Za a kuwa fara daga Urushalima.
tannāmnā yirūśālamamārabhya sarvvadeśe manaḥparāvarttanasya pāpamocanasya ca susaṁvādaḥ pracārayitavyaḥ,
48 Ku ne shaidun waɗannan abubuwa.
eṣu sarvveṣu yūyaṁ sākṣiṇaḥ|
49 Zan aika muku da abin da Ubana ya yi alkawari. Amma ku dakata a birnin tukuna, sai an rufe ku da iko daga sama.”
aparañca paśyata pitrā yat pratijñātaṁ tat preṣayiṣyāmi, ataeva yāvatkālaṁ yūyaṁ svargīyāṁ śaktiṁ na prāpsyatha tāvatkālaṁ yirūśālamnagare tiṣṭhata|
50 Bayan ya kai su waje kusa da Betani, sai ya ɗaga hannuwansa ya sa musu albarka.
atha sa tān baithanīyāparyyantaṁ nītvā hastāvuttolya āśiṣa vaktumārebhe
51 Yana cikin sa musu albarka, sai ya rabu da su. Aka ɗauke shi zuwa cikin sama.
āśiṣaṁ vadanneva ca tebhyaḥ pṛthag bhūtvā svargāya nīto'bhavat|
52 Sai suka yi masa sujada, suka koma Urushalima cike da murna sosai.
tadā te taṁ bhajamānā mahānandena yirūśālamaṁ pratyājagmuḥ|
53 Sai suka ci gaba da zama a cikin haikalin, suna yabon Allah.
tato nirantaraṁ mandire tiṣṭhanta īśvarasya praśaṁsāṁ dhanyavādañca karttam ārebhire| iti||

< Luka 24 >