< Luka 24 >

1 Da sassafe a ranar farko ta mako, matan suka je kabarin, da kayan ƙanshin da suka shirya.
Men på den første dag i uken, tidlig i dagningen, kom de til graven, og hadde med sig de velluktende urter som de hadde tilberedt.
2 Suka iske an riga an gungurar da dutsen daga bakin kabarin.
Men de fant stenen veltet fra graven,
3 Amma da suka shiga ciki, ba su iske jikin Ubangiji Yesu ba.
og da de gikk inn i den, fant de ikke den Herre Jesu legeme.
4 Yayinda suna cikin tunani a kan wannan, nan take, ga waɗansu mutum biyu tsaye kusa da su, sanye da kaya masu ƙyalli, kamar walƙiya.
Og det skjedde mens de stod rådville ved dette, se, da stod to menn hos dem i skinnende klædebon;
5 A cikin tsoro, matan suka fāɗi da fuskokinsu a ƙasa, amma mutanen suka ce musu, “Me ya sa kuke neman mai rai a cikin matattu?
og da de blev forferdet og bøide sitt ansikt mot jorden, sa de til dem: Hvorfor søker I den levende blandt de døde?
6 Ba ya nan, ya tashi! Ku tuna yadda ya gaya muku tun yana tare da ku a Galili cewa,
Han er ikke her, han er opstanden; kom i hu hvorledes han talte til eder mens han ennu var i Galilea, da han sa
7 ‘Dole a ba da Ɗan Mutum ga hannun masu zunubi, a kuma gicciye shi, a rana ta uku kuma a tashe shi.’”
at Menneskesønnen skulde overgis i syndige menneskers hender og korsfestes og opstå på den tredje dag!
8 Sai suka tuna da maganarsa.
Da kom de hans ord i hu.
9 Da suka dawo daga kabarin, sai suka faɗa wa Sha Ɗayan nan da sauransu, dukan waɗannan abubuwa.
Og de vendte tilbake fra graven, og fortalte alt dette til de elleve og til alle de andre.
10 Matan da suka gaya wa manzannin waɗannan abubuwa su ne, Maryamu Magdalin, da Yowanna, da Maryamu uwar Yaƙub, da waɗansu da suke tare da su.
Det var Maria Magdalena og Johanna og Maria, Jakobs mor, og de andre kvinner med dem. De sa dette til apostlene,
11 Amma ba su gaskata matan ba, domin sun ɗauki kalmominsu wani zancen banza ne.
og deres ord syntes dem å være løs tale, og de trodde dem ikke.
12 Duk da haka, Bitrus ya tashi a guje zuwa kabarin. Da ya sunkuya, sai ya ga ƙyallayen lilin kaɗai a kwance. Sai ya koma yana tunani a ransa, a kan abin da ya faru.
Men Peter stod op og løp til graven, og da han bøide sig ned, så han bare liksvøpet; og han gikk hjem og undret sig over det som var skjedd.
13 A wannan rana kuma, biyu daga cikinsu suna tafiya zuwa wani ƙauye, da ake kira Emmawus, da suke kusan mil bakwai daga Urushalima.
Og se, to av dem gikk samme dag til en by som ligger seksti stadier fra Jerusalem, og som heter Emmaus,
14 Suna magana da juna a kan dukan abubuwan da suka faru.
og de talte med hverandre om alt dette som hadde hendt.
15 Da suna magana, kuma suna tattauna waɗannan abubuwa da junansu, sai Yesu da kansa ya zo yana tafiya tare da su.
Og det skjedde mens de talte sammen og spurte hverandre, da kom Jesus selv nær til dem og vandret sammen med dem;
16 Amma ba a ba su ikon gane shi ba.
men deres øine blev holdt igjen, så de ikke kjente ham.
17 Sai ya tambaye, su ya ce, “Mene ne kuke tattaunawa da juna a cikin tafiyarku?” Suka tsaya shiru, da damuwa a fuskarsu.
Han sa til dem: Hvad er dette for tale som I fører med hverandre på veien? Og de stod stille med sorgfullt åsyn.
18 Ɗaya daga cikinsu, mai suna Kiliyobas, ya tambaye shi ya ce, “Ashe, kai baƙo ne a Urushalima, da ba ka san abubuwan da suka faru a can, a cikin kwanakin nan ba?”
Men en av dem, som hette Kleopas, tok til orde og sa til ham: Er du alene fremmed i Jerusalem og vet ikke det som er skjedd der i disse dager?
19 Sai ya yi tambaya, “Waɗanne abubuwa?” Suka amsa suka ce, “Game da Yesu Banazare. Shi annabi ne, mai iko ne kuma cikin ayyukansa da maganarsa, a gaban Allah da kuma dukan mutane.
Han sa til dem: Hvad da? Og de sa til ham: Det med Jesus fra Nasaret, som var en profet, mektig i gjerning og ord for Gud og alt folket,
20 Manyan firistoci da masu mulkinmu sun ba da shi a yi masa hukuncin mutuwa, suka kuwa gicciye shi.
og hvorledes våre yppersteprester og rådsherrer har overgitt ham til dødsdom og korsfestet ham.
21 Amma da, muna sa zuciya cewa, shi ne wanda zai fanshi Isra’ila. Bugu da ƙari kuma yau kwana uku ke nan tun da wannan abin ya faru.
Men vi håpet at han var den som skulde forløse Israel. Og dog - med alt dette er det idag den tredje dag siden dette skjedde.
22 Har wa yau, waɗansu daga cikin matanmu sun ba mu mamaki. Sun je kabarin da sassafen nan,
Men så har og nogen av våre kvinner forferdet oss; de kom tidlig imorges til graven,
23 amma ba su sami jikinsa ba. Sun dawo sun faɗa mana cewa, sun ga wahayi na mala’iku, da suka ce yana da rai.
og da de ikke fant hans legeme, kom de og sa at de hadde sett et syn av engler, som sa at han lever;
24 Sa’an nan, waɗansu abokanmu suka je kabarin, suka kuma tarar da kome kamar yadda matan suka faɗa, amma shi, ba su gan shi ba.”
og nogen av dem som var med oss, gikk bort til graven og fant det så som kvinnene hadde sagt; men ham så de ikke.
25 Sai ya ce musu, “Ashe, ku marasa azanci ne, masu nauyin zuciyar gaskata, da dukan abin da annabawa suka faɗa!
Da sa han til dem: I dårer og senhjertede til å tro alt det profetene har talt!
26 Ai, dole Kiristi yă sha waɗannan wahalolin, kafin yă shiga ɗaukakarsa.
Måtte ikke Messias lide dette og så gå inn til sin herlighet?
27 Sai ya fara bayyana musu daga Musa da dukan Annabawa, abin da dukan Nassi ya faɗa a kansa.”
Og han begynte fra Moses og fra alle profetene og utla for dem i alle skriftene det som er skrevet om ham.
28 Da suka yi kusa da ƙauyen da za su, sai Yesu ya yi kamar zai ci gaba.
Og de var nær ved byen som de gikk til, og han lot som han vilde gå videre.
29 Amma suka matsa masa suka ce, “Sauka wurinmu, don dare ya kusa, rana ta kusa fāɗuwa.” Sai ya sauka wurinsu.
Da nødde de ham og sa: Bli hos oss; for det stunder til aften, og dagen heller! Og han gikk inn og blev hos dem.
30 Da ya zauna a tebur tare da su, sai ya ɗauki burodi, ya yi godiya, ya kakkarya ya fara ba su.
Og det skjedde da han satt til bords med dem, da tok han brødet og velsignet det, og brøt det og gav dem;
31 Sa’an nan idanunsu suka buɗe, suka gane shi. Sai ya ɓace musu.
da blev deres øine åpnet, og de kjente ham; og han blev usynlig for dem.
32 Suka tambayi juna, “Ashe, shi ya sa zukatanmu suka kuna a cikinmu, sa’ad da yake magana da mu a hanya, yana bayyana mana Nassi.”
Og de sa til hverandre: Brente ikke vårt hjerte i oss da han talte til oss på veien og oplot skriftene for oss?
33 Suka tashi nan da nan suka koma Urushalima. A can suka sami Sha Ɗayan nan da waɗanda suke tare da su a wuri ɗaya,
Og de stod op i samme stund og vendte tilbake til Jerusalem, og de fant de elleve samlet, og dem som var med dem, og disse sa:
34 suna cewa, “Gaskiya ne! Ubangiji ya tashi, ya kuma bayyana ga Siman”
Herren er sannelig opstanden, og er sett av Simon!
35 Sai su biyun nan suka ba da labarin abin da ya faru a hanya, da kuma yadda suka gane Yesu yayinda ya kakkarya burodin.
Og de fortalte hvad som var skjedd på veien, og hvorledes han blev kjent av dem da han brøt brødet.
36 Suna cikin wannan zance, sai ga Yesu da kansa tsaye a tsakiyarsu. Sai ya ce musu, “Salama a gare ku!”
Mens de talte om dette, stod han selv midt iblandt dem og sa til dem: Fred være med eder!
37 Suka firgita, suka tsorota, suna tsammani fatalwa ce suka gani.
Men de blev forferdet og fulle av frykt, og trodde at de så en ånd.
38 Sai ya ce musu, “Don me kuke damuwa, kuke kuma shakka a zuciyarku?
Og han sa til dem: Hvorfor er I forferdet, og hvorfor opstiger tvilende tanker i eders hjerte?
39 Ku duba hannuwana da ƙafafuna. Ai, ni ne da kaina! Ku taɓa ni ku ji, ai, fatalwa ba ta da nama da ƙashi, yadda kuke gani nake da su.”
Se mine hender og mine føtter, og se at det er mig selv! Kjenn på mig og se! En ånd har jo ikke kjøtt og ben, som I ser at jeg har.
40 Da ya faɗi haka, sai ya nuna musu hannuwansa da ƙafafunsa.
Og da han hadde sagt dette, viste han dem sine hender og sine føtter.
41 Kuma har yanzu, suna cikin rashin gaskatawa, saboda murna da mamaki, sai ya tambaye su, “Kuna da abinci a nan?”
Men da de ennu ikke trodde for glede, og undret sig, sa han til dem: Har I her noget å ete?
42 Suka ba shi ɗan gasasshen kifi,
Da gav de ham et stykke av en stekt fisk og noget av en honningkake,
43 ya karɓa ya ci a gabansu.
og han tok det og åt for deres øine.
44 Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da na gaya muku tun ina tare da ku cewa, dole a cika kome da aka rubuta game da ni, a cikin Dokar Musa, da Annabawa, da kuma Zabura.”
Og han sa til dem: Dette er mine ord som jeg talte til eder mens jeg ennu var hos eder, at alt det måtte opfylles som er skrevet i Mose lov og profetene og salmene om mig.
45 Sai ya wayar da tunaninsu don su fahimci Nassi.
Da oplot han deres forstand, så de kunde forstå skriftene.
46 Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da aka rubuta, cewa dole Kiristi yă sha wahala, a rana ta uku kuma yă tashi daga matattu.
Og han sa til dem: Så står skrevet, at Messias skal lide og opstå fra de døde på den tredje dag,
47 Kuma a cikin sunansa za a yi wa’azin tuba da gafarar zunubai, ga dukan ƙasashe. Za a kuwa fara daga Urushalima.
og at i hans navn skal omvendelse og syndenes forlatelse forkynnes for alle folkeslag, fra Jerusalem av.
48 Ku ne shaidun waɗannan abubuwa.
I er vidner om dette.
49 Zan aika muku da abin da Ubana ya yi alkawari. Amma ku dakata a birnin tukuna, sai an rufe ku da iko daga sama.”
Og jeg sender over eder det som min Fader har lovt; men I skal bli i byen inntil I blir iklædd kraft fra det høie.
50 Bayan ya kai su waje kusa da Betani, sai ya ɗaga hannuwansa ya sa musu albarka.
Og han førte dem ut imot Betania, og han løftet op sine hender og velsignet dem;
51 Yana cikin sa musu albarka, sai ya rabu da su. Aka ɗauke shi zuwa cikin sama.
og det skjedde da han velsignet dem, at han skiltes fra dem og blev optatt til himmelen.
52 Sai suka yi masa sujada, suka koma Urushalima cike da murna sosai.
Og de tilbad ham og vendte tilbake til Jerusalem med stor glede,
53 Sai suka ci gaba da zama a cikin haikalin, suna yabon Allah.
Og de var alltid i templet og lovet og priste Gud.

< Luka 24 >