< Luka 24 >
1 Da sassafe a ranar farko ta mako, matan suka je kabarin, da kayan ƙanshin da suka shirya.
Etiya hapta laga poila din te, etu mahila khan kobor usorte ahise, mitha sugandh tel aru dawai jugut kori kene anise.
2 Suka iske an riga an gungurar da dutsen daga bakin kabarin.
Kintu taikhan dikhise kobor bondh kori kene rakha pathor to hataikena ase,
3 Amma da suka shiga ciki, ba su iske jikin Ubangiji Yesu ba.
kintu taikhan bhitor te jai kene Probhu Jisu laga gaw to dikha nai.
4 Yayinda suna cikin tunani a kan wannan, nan take, ga waɗansu mutum biyu tsaye kusa da su, sanye da kaya masu ƙyalli, kamar walƙiya.
Aru eneka hoise, jitia kobor te Jisu laga gaw dikha nai, taikhan asurit hoise. Aru achanak pora, duijon manu boga kapra lagai kene taikhan usorte khara hoise.
5 A cikin tsoro, matan suka fāɗi da fuskokinsu a ƙasa, amma mutanen suka ce musu, “Me ya sa kuke neman mai rai a cikin matattu?
Aru, mahila khan bhoi lagikena matha niche kori kene matite girise, etu manu khan pora mahila khan ke hudise, “Tumikhan jinda manu ke mora khan majote kele bisari ase?
6 Ba ya nan, ya tashi! Ku tuna yadda ya gaya muku tun yana tare da ku a Galili cewa,
Tai yate nai, kintu jinda hoise! Yaad koribi kineka Tai tumikhan ke koisele Galilee te thaka homoi te,
7 ‘Dole a ba da Ɗan Mutum ga hannun masu zunubi, a kuma gicciye shi, a rana ta uku kuma a tashe shi.’”
koisele Manu laga Putro kineka paapi manu hathte di dibo aru Taike Cross te morai dibo, aru tin dinte Tai aru bhi jinda hoi jabo.”
8 Sai suka tuna da maganarsa.
Titia mahila khan Jisu laga kotha monte yaad ahise,
9 Da suka dawo daga kabarin, sai suka faɗa wa Sha Ɗayan nan da sauransu, dukan waɗannan abubuwa.
aru jitia kobor pora wapas jaise, taikhan jai kene egaroh jon chela aru sob manu khan ke khobor di dise.
10 Matan da suka gaya wa manzannin waɗannan abubuwa su ne, Maryamu Magdalin, da Yowanna, da Maryamu uwar Yaƙub, da waɗansu da suke tare da su.
Aru Mary Magdalene, Joanna, aru Mary James laga ama aru mahila khan jai kene chela khan ke khobor di dise.
11 Amma ba su gaskata matan ba, domin sun ɗauki kalmominsu wani zancen banza ne.
Kintu etu khobor to chela khan misa bhabise, aru mahila khan kowa kotha to biswas kora nai.
12 Duk da haka, Bitrus ya tashi a guje zuwa kabarin. Da ya sunkuya, sai ya ga ƙyallayen lilin kaɗai a kwance. Sai ya koma yana tunani a ransa, a kan abin da ya faru.
Hoile bhi Peter to uthi kene, Jisu laga kobor te polaikene jaise, aru usor pora saise aru khali Jisu ke bandi rakha mihin kapra he dikhise. Aru tai bahar te ulaikena ki hoise etu bhabise.
13 A wannan rana kuma, biyu daga cikinsu suna tafiya zuwa wani ƙauye, da ake kira Emmawus, da suke kusan mil bakwai daga Urushalima.
Aru ek din, duijon manu ekta bosti te jai thakise. Jerusalem pora sath mil dur thaka Emmaus bosti te.
14 Suna magana da juna a kan dukan abubuwan da suka faru.
Etu din khan te ki hoise eitu khan sob laga kotha khan koi kene jai thakise.
15 Da suna magana, kuma suna tattauna waɗannan abubuwa da junansu, sai Yesu da kansa ya zo yana tafiya tare da su.
Aru eneka hoise, taikhan kotha patikena jai thaka homoi te, Jisu taikhan usorte achanak pora ahi kene taikhan eke logote jai thakise.
16 Amma ba a ba su ikon gane shi ba.
Kintu taikhan suku pora Jisu ke chini bole para nai.
17 Sai ya tambaye, su ya ce, “Mene ne kuke tattaunawa da juna a cikin tafiyarku?” Suka tsaya shiru, da damuwa a fuskarsu.
Titia Jisu taikhan ke hudise, “Tumikhan ki kotha patikena mon dukh pora jai ase?” Taikhan khara hoi jaise, mon dukh pora.
18 Ɗaya daga cikinsu, mai suna Kiliyobas, ya tambaye shi ya ce, “Ashe, kai baƙo ne a Urushalima, da ba ka san abubuwan da suka faru a can, a cikin kwanakin nan ba?”
Kintu ekjon Cleopas pora Jisu ke hudise, “Apuni Jerusalem te ekla ahise naki aru ki hoise etu najane?”
19 Sai ya yi tambaya, “Waɗanne abubuwa?” Suka amsa suka ce, “Game da Yesu Banazare. Shi annabi ne, mai iko ne kuma cikin ayyukansa da maganarsa, a gaban Allah da kuma dukan mutane.
Titia Jisu taikhan ke hudise, “Yate ki hoise?” Taikhan koise, “Nazareth Jisu laga kotha, kun ekjon manu thakise, aru asurit kaam aru kotha para Isor usorte aru sob manu nimite Tai ekjon dangor bhabobadi thakise,
20 Manyan firistoci da masu mulkinmu sun ba da shi a yi masa hukuncin mutuwa, suka kuwa gicciye shi.
Aru mukhyo purohit khan aru cholawta khan pora Taike dhorise aru bodnam kori kene Cross te morai dise.
21 Amma da, muna sa zuciya cewa, shi ne wanda zai fanshi Isra’ila. Bugu da ƙari kuma yau kwana uku ke nan tun da wannan abin ya faru.
Kintu moi khan biswas kori thakise Tai he Israel manu ke mukti dibo. Kintu etu sob pura hoi kene, aji tin din hoi jaise.
22 Har wa yau, waɗansu daga cikin matanmu sun ba mu mamaki. Sun je kabarin da sassafen nan,
Kintu kunba mahila khan kobor te joldi jai kene, amikhan ke ahi kene asurit kotha koise.
23 amma ba su sami jikinsa ba. Sun dawo sun faɗa mana cewa, sun ga wahayi na mala’iku, da suka ce yana da rai.
Aru taikhan Jisu laga gaw to kobor bhitor te dikha nai, taikhan sorgodoth khan ke darshan korise koise aru Jisu jinda ase koise.
24 Sa’an nan, waɗansu abokanmu suka je kabarin, suka kuma tarar da kome kamar yadda matan suka faɗa, amma shi, ba su gan shi ba.”
Kintu amikhan logote thaka kunba kobor sabole jaise aru jineka mahila khan pora koise eneka he dikhise, kintu Jisu ke ta te dikha nai.”
25 Sai ya ce musu, “Ashe, ku marasa azanci ne, masu nauyin zuciyar gaskata, da dukan abin da annabawa suka faɗa!
Titia Jisu taikhan ke koise, “O murkho aru mon chutu kori thaka khan jun khan bhabobadi khan pora ki koise etu sobke biswas kore!
26 Ai, dole Kiristi yă sha waɗannan wahalolin, kafin yă shiga ɗaukakarsa.
Etu dorkar thaka nai naki Khrista dukh paikena, aru bhi Isor laga mohima te huma bole?”
27 Sai ya fara bayyana musu daga Musa da dukan Annabawa, abin da dukan Nassi ya faɗa a kansa.”
Moses pora suru kori kene aru kiman bhabobadi khan thakise, taikhan ke ki pobitro kotha te Tai nimite likha ase etu bujhi bole dise.
28 Da suka yi kusa da ƙauyen da za su, sai Yesu ya yi kamar zai ci gaba.
Taikhan jabole thaka bosti te ponchise, aru Jisu age te jabo nisena korise.
29 Amma suka matsa masa suka ce, “Sauka wurinmu, don dare ya kusa, rana ta kusa fāɗuwa.” Sai ya sauka wurinsu.
Kintu taikhan pora Taike anurodh kori kene koise, “Amikhan logote thakibi, aji laga din to khotom hobole hoise.” Aru Jisu taikhan logote thaki bole jaise.
30 Da ya zauna a tebur tare da su, sai ya ɗauki burodi, ya yi godiya, ya kakkarya ya fara ba su.
Aru eneka hoise, jitia taikhan eke logote bohise, Tai roti loise, aru asirbad korise, aru bhangi kene taikhan ke dise.
31 Sa’an nan idanunsu suka buɗe, suka gane shi. Sai ya ɓace musu.
Titia taikhan laga suku khuli se, aru taikhan Taike chini paise, aru Jisu taikhan usor pora Atma hoi kene jai jaise.
32 Suka tambayi juna, “Ashe, shi ya sa zukatanmu suka kuna a cikinmu, sa’ad da yake magana da mu a hanya, yana bayyana mana Nassi.”
Taikhan ekjon-ekjon logote kotha patise, “Moi khan laga mon to joli thaka nai naki, jitia Tai amikhan logote ahi thakise, aru jitia Isor laga kotha to puri kene hunai sile?”
33 Suka tashi nan da nan suka koma Urushalima. A can suka sami Sha Ɗayan nan da waɗanda suke tare da su a wuri ɗaya,
Etu homoi te taikhan uthise, aru Jerusalem te wapas jaise. Egaroh chela khan eke logote joma hoi thakise, aru dusra khan bhi eke logote thakise.
34 suna cewa, “Gaskiya ne! Ubangiji ya tashi, ya kuma bayyana ga Siman”
Aru koise, “Hosa pora Probhu jinda hoise, aru Simon usorte ahise.”
35 Sai su biyun nan suka ba da labarin abin da ya faru a hanya, da kuma yadda suka gane Yesu yayinda ya kakkarya burodin.
Titia rasta te ki hoise etu sob taikhan ke koi dise, kineka Jisu amikhan ke dikhai dise jitia Tai roti bhangise.
36 Suna cikin wannan zance, sai ga Yesu da kansa tsaye a tsakiyarsu. Sai ya ce musu, “Salama a gare ku!”
Jitia taikhan etu kotha khan koi thakise, Jisu taikhan majote ahikena khara hoi kene koise, “Tumikhan uporte shanti thakibi.”
37 Suka firgita, suka tsorota, suna tsammani fatalwa ce suka gani.
Kintu taikhan asurit hoise, aru bisi bhoi lagise, taikhan bhabise ekjon bhoot taikhan laga usorte ahise.
38 Sai ya ce musu, “Don me kuke damuwa, kuke kuma shakka a zuciyarku?
Titia Jisu taikhan ke koise, “Tumikhan kele bhoi lagise, aru kele monte alag bhabona kori ase?
39 Ku duba hannuwana da ƙafafuna. Ai, ni ne da kaina! Ku taɓa ni ku ji, ai, fatalwa ba ta da nama da ƙashi, yadda kuke gani nake da su.”
Ami laga hath aru theng to sabi, etu Moi he ase. Moike chui kene sabi kele atma to mangso aru hardi nathake, kintu Moi logot eitu khan thaka tumikhan dikhi ase.”
40 Da ya faɗi haka, sai ya nuna musu hannuwansa da ƙafafunsa.
Jitia Tai etu kotha koise, Tai laga hath aru theng taikhan ke dikhai dise.
41 Kuma har yanzu, suna cikin rashin gaskatawa, saboda murna da mamaki, sai ya tambaye su, “Kuna da abinci a nan?”
Aru etu homoi te taikhan bisi asurit aru khushi pora biswas nakora nisena hoi jaise, Tai aru taikhan ke koise, “Tumikhan logote kiba khabole ase naki?”
42 Suka ba shi ɗan gasasshen kifi,
Titia taikhan Jisu ke jolai rakha maas khabole dise,
43 ya karɓa ya ci a gabansu.
aru taikhan usorte Jisu etu loi kene khaise.
44 Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da na gaya muku tun ina tare da ku cewa, dole a cika kome da aka rubuta game da ni, a cikin Dokar Musa, da Annabawa, da kuma Zabura.”
Titia tai koise, “Etu Ami laga kotha ase, Ami jinda thaka homoi te tumikhan ke ki koisele, Moses laga kitab te aru bhabobadi khan aru Bhajan Geet te Ami nimite ki likha ase, etu sob pura hobo lage.”
45 Sai ya wayar da tunaninsu don su fahimci Nassi.
Titia Isor laga kotha bujhi bole taikhan laga dimag khuli dise, etu pichete Jisu taikhan ke koise,
46 Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da aka rubuta, cewa dole Kiristi yă sha wahala, a rana ta uku kuma yă tashi daga matattu.
“Etu nimite Isor kotha te eneka likha ase: Khrista dukh pabo, aru mora pora tin dinte jee uthibo;
47 Kuma a cikin sunansa za a yi wa’azin tuba da gafarar zunubai, ga dukan ƙasashe. Za a kuwa fara daga Urushalima.
aru mon ghura bole aru paap pora khyama pabole sob desh te prochar koribo, Jerusalem pora shuru hobo.
48 Ku ne shaidun waɗannan abubuwa.
Tumikhan etu sob laga gawahi hobo.
49 Zan aika muku da abin da Ubana ya yi alkawari. Amma ku dakata a birnin tukuna, sai an rufe ku da iko daga sama.”
Moi tumikhan ke Baba pora ki kosom dise, etu te pathai ase. Kintu tumikhan Jerusalem chari kene najabi jitia tak sorgo laga takot tumikhan uporte nahe.”
50 Bayan ya kai su waje kusa da Betani, sai ya ɗaga hannuwansa ya sa musu albarka.
Aru Jisu taikhan ke olop dur Bethany te loi jaise, aru Tai laga hath uthaikene, taikhan ke asirbad korise.
51 Yana cikin sa musu albarka, sai ya rabu da su. Aka ɗauke shi zuwa cikin sama.
Etiya eneka hoise, jitia Tai pora taikhan ke asirbad kori thakise, etu somoite badal ahikena Jisu ke uthaikene sorgote loi jaise.
52 Sai suka yi masa sujada, suka koma Urushalima cike da murna sosai.
Taikhan Jisu ke mohima kori thakise, aru khushi anondo pora Jerusalem te wapas jaise,
53 Sai suka ci gaba da zama a cikin haikalin, suna yabon Allah.
aru taikhan mondoli te jai kene Isor ke dhanyavad aru aradhana kori thakise.