< Luka 24 >

1 Da sassafe a ranar farko ta mako, matan suka je kabarin, da kayan ƙanshin da suka shirya.
Nädala esimese päeva hommikul vara läksid naised haua juurde, kaasas valmistatud lõhnaained.
2 Suka iske an riga an gungurar da dutsen daga bakin kabarin.
Nad leidsid, et kivi oli haua sissepääsu eest ära veeretatud,
3 Amma da suka shiga ciki, ba su iske jikin Ubangiji Yesu ba.
aga kui nad sisse läksid, ei leidnud nad Issanda Jeesuse ihu.
4 Yayinda suna cikin tunani a kan wannan, nan take, ga waɗansu mutum biyu tsaye kusa da su, sanye da kaya masu ƙyalli, kamar walƙiya.
Kui nad seal imestasid, mis toimub, ilmus äkitselt kaks meest, kes olid riietatud eredalt hiilgavatesse rõivaetesse.
5 A cikin tsoro, matan suka fāɗi da fuskokinsu a ƙasa, amma mutanen suka ce musu, “Me ya sa kuke neman mai rai a cikin matattu?
Naised kohkusid ja kummardusid näoli maha. Nad ütlesid naistele: „Miks te otsite elavat surnute juurest?
6 Ba ya nan, ya tashi! Ku tuna yadda ya gaya muku tun yana tare da ku a Galili cewa,
Ta ei ole siin, ta on surnuist üles tõusnud! Meenutage, mida ta teile rääkis, kui te olite alles Galileas:
7 ‘Dole a ba da Ɗan Mutum ga hannun masu zunubi, a kuma gicciye shi, a rana ta uku kuma a tashe shi.’”
„Inimese Poeg antakse kurjade inimeste kätte ja lüüakse risti, aga kolmandal päeval tõuseb ta surnuist üles.““
8 Sai suka tuna da maganarsa.
Siis meenus neile, mida ta oli öelnud.
9 Da suka dawo daga kabarin, sai suka faɗa wa Sha Ɗayan nan da sauransu, dukan waɗannan abubuwa.
Kui nad haua juurest tagasi tulid, rääkisid nad kõigest juhtunust üheteistkümnele jüngrile ja kõigile teistele.
10 Matan da suka gaya wa manzannin waɗannan abubuwa su ne, Maryamu Magdalin, da Yowanna, da Maryamu uwar Yaƙub, da waɗansu da suke tare da su.
Need, kes juhtunust apostlitele rääkisid, olid Maarja Magdaleena, Johanna, Jaakobuse ema Maarja ja teised nendega koos olnud naised.
11 Amma ba su gaskata matan ba, domin sun ɗauki kalmominsu wani zancen banza ne.
Kuid neile tundus see rumalusena, seega ei uskunud nad naisi.
12 Duk da haka, Bitrus ya tashi a guje zuwa kabarin. Da ya sunkuya, sai ya ga ƙyallayen lilin kaɗai a kwance. Sai ya koma yana tunani a ransa, a kan abin da ya faru.
Aga Peetrus tõusis ja jooksis haua juurde. Ta kummardus ja vaatas sisse ning nägi ainult haualinu. Nii läks ta tagasi koju, ise imestades, mis küll oli juhtunud.
13 A wannan rana kuma, biyu daga cikinsu suna tafiya zuwa wani ƙauye, da ake kira Emmawus, da suke kusan mil bakwai daga Urushalima.
Samal päeval oli kaks jüngrit teel külasse nimega Emmaus, mis asub Jeruusalemmast umbes seitsme miili kaugusel.
14 Suna magana da juna a kan dukan abubuwan da suka faru.
Nad rääkisid kõigest, mis oli juhtunud.
15 Da suna magana, kuma suna tattauna waɗannan abubuwa da junansu, sai Yesu da kansa ya zo yana tafiya tare da su.
Kui nad arutlesid ja vaidlesid, tuli Jeesus ja hakkas nendega koos kõndima.
16 Amma ba a ba su ikon gane shi ba.
Aga neil ei lastud teda ära tunda.
17 Sai ya tambaye, su ya ce, “Mene ne kuke tattaunawa da juna a cikin tafiyarku?” Suka tsaya shiru, da damuwa a fuskarsu.
„Mille üle te siin teed käies arutlete?“küsis ta neilt. Nad peatusid kurva näoga.
18 Ɗaya daga cikinsu, mai suna Kiliyobas, ya tambaye shi ya ce, “Ashe, kai baƙo ne a Urushalima, da ba ka san abubuwan da suka faru a can, a cikin kwanakin nan ba?”
Üks neist, keda hüüti Kleopaseks, vastas: „Kas sa oled Jeruusalemmas ainult külas? Sa oled ilmselt ainus inimene, kes ei tea viimastel päevadel juhtunust.“
19 Sai ya yi tambaya, “Waɗanne abubuwa?” Suka amsa suka ce, “Game da Yesu Banazare. Shi annabi ne, mai iko ne kuma cikin ayyukansa da maganarsa, a gaban Allah da kuma dukan mutane.
„Millest siis?“küsis Jeesus. „Naatsareti Jeesusest, “vastasid nad. „Ta oli prohvet, kes rääkis mõjuvõimsalt ning tegi suuri imetegusid Jumala ja kogu rahva ees.
20 Manyan firistoci da masu mulkinmu sun ba da shi a yi masa hukuncin mutuwa, suka kuwa gicciye shi.
Kuid meie ülempreestrid ja juhid andsid ta surmamõistmiseks ja lõid ta risti.
21 Amma da, muna sa zuciya cewa, shi ne wanda zai fanshi Isra’ila. Bugu da ƙari kuma yau kwana uku ke nan tun da wannan abin ya faru.
Me lootsime, et tema on see, kes päästab Iisraeli. Kõigest juhtunust on nüüd möödas kolm päeva.
22 Har wa yau, waɗansu daga cikin matanmu sun ba mu mamaki. Sun je kabarin da sassafen nan,
Aga mõned naised meie grupist üllatasid meid.
23 amma ba su sami jikinsa ba. Sun dawo sun faɗa mana cewa, sun ga wahayi na mala’iku, da suka ce yana da rai.
Nad läksid koidikul haua juurde ega leidnud tema surnukeha. Nad tulid tagasi ja ütlesid, et olid näinud nägemust inglitest, kes ütlesid neile, et ta elab.
24 Sa’an nan, waɗansu abokanmu suka je kabarin, suka kuma tarar da kome kamar yadda matan suka faɗa, amma shi, ba su gan shi ba.”
Mõned meist läksid haua juurde ja leidsid, et kõik oli täpselt nii, nagu naised ütlesid, kuid nad ei näinud teda.“
25 Sai ya ce musu, “Ashe, ku marasa azanci ne, masu nauyin zuciyar gaskata, da dukan abin da annabawa suka faɗa!
Jeesus ütles neile: „Te olete nii töntsi arusaamisega! Kui pikaldased olete te uskuma kõike seda, mida prohvetid on öelnud!
26 Ai, dole Kiristi yă sha waɗannan wahalolin, kafin yă shiga ɗaukakarsa.
Kas Messias ei pidanud kannatama enne, kui sai hiilgusesse minna?“
27 Sai ya fara bayyana musu daga Musa da dukan Annabawa, abin da dukan Nassi ya faɗa a kansa.”
Seejärel alustas ta Moosesest ja kõigist prohvetitest ning selgitas neile kõike, mida oli tema kohta Pühakirjas öeldud.
28 Da suka yi kusa da ƙauyen da za su, sai Yesu ya yi kamar zai ci gaba.
Kui nad lähenesid külale, kuhu nad teel olid, tegi Jeesus, nagu läheks ta edasi.
29 Amma suka matsa masa suka ce, “Sauka wurinmu, don dare ya kusa, rana ta kusa fāɗuwa.” Sai ya sauka wurinsu.
Aga nad käisid talle peale, öeldes: „Tule ja jää meie juurde. On juba hilja, päev on peaaegu õhtus.“Nii läks ta siis nende juurde sisse.
30 Da ya zauna a tebur tare da su, sai ya ɗauki burodi, ya yi godiya, ya kakkarya ya fara ba su.
Kui ta istus koos nendega sööma, võttis ta leiva, tänas, murdis ja andis neile.
31 Sa’an nan idanunsu suka buɗe, suka gane shi. Sai ya ɓace musu.
Nende silmad avati ja nad tundsid ta ära. Siis kadus ta nende silmist.
32 Suka tambayi juna, “Ashe, shi ya sa zukatanmu suka kuna a cikinmu, sa’ad da yake magana da mu a hanya, yana bayyana mana Nassi.”
Kaks jüngrit ütlesid teineteisele: „Kui ta meile Pühakirja selgitas, kas see ei sütitanud siis meid?“
33 Suka tashi nan da nan suka koma Urushalima. A can suka sami Sha Ɗayan nan da waɗanda suke tare da su a wuri ɗaya,
Nad tõusid kohe püsti ja läksid Jeruusalemma tagasi. Nad leidsid üksteist jüngrid ja need, kes olid nendega koos,
34 suna cewa, “Gaskiya ne! Ubangiji ya tashi, ya kuma bayyana ga Siman”
ütlesid: „Issand on tõesti surnuist üles tõusnud! Ta ilmus Siimonale.“
35 Sai su biyun nan suka ba da labarin abin da ya faru a hanya, da kuma yadda suka gane Yesu yayinda ya kakkarya burodin.
Siis need, kes olid just saabunud, jutustasid teistele jüngritele, mis oli nendega teed käies juhtunud ja kuidas nad olid Jeesuse ära tundnud, kui ta leiba murdis.
36 Suna cikin wannan zance, sai ga Yesu da kansa tsaye a tsakiyarsu. Sai ya ce musu, “Salama a gare ku!”
Kui nad alles rääkisid, seisis Jeesus ise nende keskel ja ütles: „Rahu olgu teile!“
37 Suka firgita, suka tsorota, suna tsammani fatalwa ce suka gani.
Nad olid jahmunud ja ehmunud ning arvasid, et näevad kummitust.
38 Sai ya ce musu, “Don me kuke damuwa, kuke kuma shakka a zuciyarku?
„Miks te olete kohkunud? Miks te kahtlete?“küsis ta neilt.
39 Ku duba hannuwana da ƙafafuna. Ai, ni ne da kaina! Ku taɓa ni ku ji, ai, fatalwa ba ta da nama da ƙashi, yadda kuke gani nake da su.”
„Vaadake mu käsi ja jalgu – te näete, et see olen mina. Katsuge mind, siis olete kindlad, sest kummitusel ei ole liha ega luid, nagu näete minul olevat.“
40 Da ya faɗi haka, sai ya nuna musu hannuwansa da ƙafafunsa.
Kui ta seda oli öelnud, näitas ta neile oma käsi ja jalgu.
41 Kuma har yanzu, suna cikin rashin gaskatawa, saboda murna da mamaki, sai ya tambaye su, “Kuna da abinci a nan?”
Kuid nad ei suutnud ikka veel uskuda, sest nad olid elevil ja hämmastuses. Ta küsis neilt: „Kas teil on midagi süüa?“
42 Suka ba shi ɗan gasasshen kifi,
Nad andsid talle tüki küpsetatud kala,
43 ya karɓa ya ci a gabansu.
ta võttis selle ja sõi seda nende silme all.
44 Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da na gaya muku tun ina tare da ku cewa, dole a cika kome da aka rubuta game da ni, a cikin Dokar Musa, da Annabawa, da kuma Zabura.”
Siis ütles Jeesus neile: „Seda ma selgitasin teile siis, kui olin veel teie juures. Kõik, mis minust on kirjutatud Moosese seaduses, prohvetites ja psalmides, pidi täide minema.“
45 Sai ya wayar da tunaninsu don su fahimci Nassi.
Seejärel avas ta nende mõistuse, nii et nad suutsid Pühakirja mõista.
46 Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da aka rubuta, cewa dole Kiristi yă sha wahala, a rana ta uku kuma yă tashi daga matattu.
Ta ütles neile: „Kirjutatud on, et Messias kannatab ja tõuseb kolmandal päeval surnuist üles ning tema nimel
47 Kuma a cikin sunansa za a yi wa’azin tuba da gafarar zunubai, ga dukan ƙasashe. Za a kuwa fara daga Urushalima.
kuulutatakse meeleparandust pattude andeksandmiseks kõigile rahvastele, alates Jeruusalemmast.
48 Ku ne shaidun waɗannan abubuwa.
Te olete kõige selle tunnistajad.
49 Zan aika muku da abin da Ubana ya yi alkawari. Amma ku dakata a birnin tukuna, sai an rufe ku da iko daga sama.”
Nüüd saadan ma teile selle, mida mu Isa on tõotanud, aga oodake linnas, kuni saate väe taevast.“
50 Bayan ya kai su waje kusa da Betani, sai ya ɗaga hannuwansa ya sa musu albarka.
Siis viis ta nad välja, kuni nad olid Betaania lähedal, ning tõstnud käed, õnnistas ta neid.
51 Yana cikin sa musu albarka, sai ya rabu da su. Aka ɗauke shi zuwa cikin sama.
Sel ajal kui ta neid õnnistas, lahkus ta neist ja ta võeti üles taevasse.
52 Sai suka yi masa sujada, suka koma Urushalima cike da murna sosai.
Nad kummardasid teda ja läksid siis rõõmsana Jeruusalemma tagasi.
53 Sai suka ci gaba da zama a cikin haikalin, suna yabon Allah.
Nad veetsid kogu oma aja templis Jumalat ülistades.

< Luka 24 >