< Luka 24 >
1 Da sassafe a ranar farko ta mako, matan suka je kabarin, da kayan ƙanshin da suka shirya.
The however on [the] first [day] of the week dawn very early to the tomb they came bringing that they had prepared spices (and certain with them. *K*)
2 Suka iske an riga an gungurar da dutsen daga bakin kabarin.
They found then the stone rolled away from the tomb.
3 Amma da suka shiga ciki, ba su iske jikin Ubangiji Yesu ba.
(and *k*) Having entered (however *no*) not they found the body of the Lord Jesus.
4 Yayinda suna cikin tunani a kan wannan, nan take, ga waɗansu mutum biyu tsaye kusa da su, sanye da kaya masu ƙyalli, kamar walƙiya.
And it came to pass while (perplexing *N(k)O*) they about this that behold men two stood by them in (garment dazzling. *N(k)O*)
5 A cikin tsoro, matan suka fāɗi da fuskokinsu a ƙasa, amma mutanen suka ce musu, “Me ya sa kuke neman mai rai a cikin matattu?
Terrified then were becoming they and bowing (their faces *N(k)O*) to the ground they said to them; Why seek you the living among the dead?
6 Ba ya nan, ya tashi! Ku tuna yadda ya gaya muku tun yana tare da ku a Galili cewa,
Not He is here but He is risen! do remember how He spoke to you yet being in Galilee
7 ‘Dole a ba da Ɗan Mutum ga hannun masu zunubi, a kuma gicciye shi, a rana ta uku kuma a tashe shi.’”
saying The Son of Man that it behooves to be delivered into hands of men sinful and to be crucified and on the third day to arise.
8 Sai suka tuna da maganarsa.
And they remembered the declarations of Him,
9 Da suka dawo daga kabarin, sai suka faɗa wa Sha Ɗayan nan da sauransu, dukan waɗannan abubuwa.
And having returned from the tomb they related these things all to the eleven and to all the rest.
10 Matan da suka gaya wa manzannin waɗannan abubuwa su ne, Maryamu Magdalin, da Yowanna, da Maryamu uwar Yaƙub, da waɗansu da suke tare da su.
It was now Magdalene Mary and Joanna and Mary the [mother] of James and the other women with them; (who *k*) were telling to the apostles these things,
11 Amma ba su gaskata matan ba, domin sun ɗauki kalmominsu wani zancen banza ne.
And appeared before them like folly the declarations (of them *N(k)O*) and they were not believing in them.
12 Duk da haka, Bitrus ya tashi a guje zuwa kabarin. Da ya sunkuya, sai ya ga ƙyallayen lilin kaɗai a kwance. Sai ya koma yana tunani a ransa, a kan abin da ya faru.
But Peter having risen up he ran to the tomb, and having stooped down he sees the linen strips (lying *k*) alone and he went away in (himself *NK(o)*) wondering at that having come to pass.
13 A wannan rana kuma, biyu daga cikinsu suna tafiya zuwa wani ƙauye, da ake kira Emmawus, da suke kusan mil bakwai daga Urushalima.
And behold two of them on same the day were going to a village being distant stadia sixty from Jerusalem whose name [is] Emmaus.
14 Suna magana da juna a kan dukan abubuwan da suka faru.
and they themselves were talking with one another about all which having taken place these things.
15 Da suna magana, kuma suna tattauna waɗannan abubuwa da junansu, sai Yesu da kansa ya zo yana tafiya tare da su.
And it came to pass during the talking by them and reasoning that Himself (*k*) Jesus having drawn near He was walking along with them.
16 Amma ba a ba su ikon gane shi ba.
but the eyes of them were held not to know Him.
17 Sai ya tambaye, su ya ce, “Mene ne kuke tattaunawa da juna a cikin tafiyarku?” Suka tsaya shiru, da damuwa a fuskarsu.
He said then to them; What words [are] these that you exchange with one another walking? And (they stood still *N(K)O*) looking sad.
18 Ɗaya daga cikinsu, mai suna Kiliyobas, ya tambaye shi ya ce, “Ashe, kai baƙo ne a Urushalima, da ba ka san abubuwan da suka faru a can, a cikin kwanakin nan ba?”
Answering now (the *k*) one (from of them *O*) (whose *k*) (name *NK(o)*) Cleopas said to Him; You yourself alone visit (in *k*) Jerusalem and not have known the [things] having come to pass in it in days these?
19 Sai ya yi tambaya, “Waɗanne abubuwa?” Suka amsa suka ce, “Game da Yesu Banazare. Shi annabi ne, mai iko ne kuma cikin ayyukansa da maganarsa, a gaban Allah da kuma dukan mutane.
And He said to them; What things? And they said to Him; The [things] concerning Jesus (of Nazareth, *N(k)O*) who was a man a prophet mighty in deed and word before God and all the people,
20 Manyan firistoci da masu mulkinmu sun ba da shi a yi masa hukuncin mutuwa, suka kuwa gicciye shi.
that then delivered up him the chief priests and the rulers of us to [the] judgment of death and crucified Him.
21 Amma da, muna sa zuciya cewa, shi ne wanda zai fanshi Isra’ila. Bugu da ƙari kuma yau kwana uku ke nan tun da wannan abin ya faru.
We ourselves however were hoping that He himself it is who is about to redeem Israel. But indeed (also *no*) with all these things [the] third this day brings (today *ko*) away from which these things came to pass.
22 Har wa yau, waɗansu daga cikin matanmu sun ba mu mamaki. Sun je kabarin da sassafen nan,
However also women certain out from us amazed us Having been (at dawn *N(k)O*) to the tomb
23 amma ba su sami jikinsa ba. Sun dawo sun faɗa mana cewa, sun ga wahayi na mala’iku, da suka ce yana da rai.
and not having found the body of Him they came declaring also a vision of angels to have seen who say He [is] living.
24 Sa’an nan, waɗansu abokanmu suka je kabarin, suka kuma tarar da kome kamar yadda matan suka faɗa, amma shi, ba su gan shi ba.”
And went some of those with us to the tomb and found [it] so even as also the women said, Him however not they saw.
25 Sai ya ce musu, “Ashe, ku marasa azanci ne, masu nauyin zuciyar gaskata, da dukan abin da annabawa suka faɗa!
And He himself said to them; O foolish and slow of heart to believe in all that spoke the prophets;
26 Ai, dole Kiristi yă sha waɗannan wahalolin, kafin yă shiga ɗaukakarsa.
Surely these things it was necessary for to suffer the Christ and to enter into the glory of Him?
27 Sai ya fara bayyana musu daga Musa da dukan Annabawa, abin da dukan Nassi ya faɗa a kansa.”
And having begun from Moses and from all the Prophets (He interpreted *N(k)O*) to them in all the Scriptures the [things] concerning (of Himself. *NK(o)*)
28 Da suka yi kusa da ƙauyen da za su, sai Yesu ya yi kamar zai ci gaba.
And they drew near to the village where they were going, and He himself (appeared *N(k)O*) farther to be going.
29 Amma suka matsa masa suka ce, “Sauka wurinmu, don dare ya kusa, rana ta kusa fāɗuwa.” Sai ya sauka wurinsu.
And they constrained Him saying; do abide with us, for toward evening it is and has declined (now *no*) the day. And He entered in to abide with them.
30 Da ya zauna a tebur tare da su, sai ya ɗauki burodi, ya yi godiya, ya kakkarya ya fara ba su.
And it came to pass during the reclining of Him with them having taken the bread He blessed [it] and having broken [it] He was giving [it] to them.
31 Sa’an nan idanunsu suka buɗe, suka gane shi. Sai ya ɓace musu.
Of them then were opened the eyes and they knew Him; And He himself vanished being seen from them.
32 Suka tambayi juna, “Ashe, shi ya sa zukatanmu suka kuna a cikinmu, sa’ad da yake magana da mu a hanya, yana bayyana mana Nassi.”
And they said to one another; Surely the heart of us burning it was within us as He was speaking with us on the road (and *k*) as He was opening to us the Scriptures?
33 Suka tashi nan da nan suka koma Urushalima. A can suka sami Sha Ɗayan nan da waɗanda suke tare da su a wuri ɗaya,
And having risen up on [that] same hour they returned to Jerusalem and they found (gathered *N(k)O*) the eleven and those with them
34 suna cewa, “Gaskiya ne! Ubangiji ya tashi, ya kuma bayyana ga Siman”
saying that Indeed has risen the Lord and He has appeared to Simon.
35 Sai su biyun nan suka ba da labarin abin da ya faru a hanya, da kuma yadda suka gane Yesu yayinda ya kakkarya burodin.
And they themselves were relating the [things] on the road and how He was known to them in the breaking of the bread.
36 Suna cikin wannan zance, sai ga Yesu da kansa tsaye a tsakiyarsu. Sai ya ce musu, “Salama a gare ku!”
These things now when they are telling He Himself (*k*) (Jesus *K*) stood in midst of them and says to them; Peace to you.
37 Suka firgita, suka tsorota, suna tsammani fatalwa ce suka gani.
Having been terrified however and filled with fear having been they were thinking [themselves] a spirit to see.
38 Sai ya ce musu, “Don me kuke damuwa, kuke kuma shakka a zuciyarku?
And He said to them; Why troubled are you and through why doubts do come up in (the heart *N(k)O*) of you?
39 Ku duba hannuwana da ƙafafuna. Ai, ni ne da kaina! Ku taɓa ni ku ji, ai, fatalwa ba ta da nama da ƙashi, yadda kuke gani nake da su.”
do see the hands of Me and the feet of Me that I myself am He himself; do touch Me and do see for a spirit flesh and bones not has even as Me myself you see having.
40 Da ya faɗi haka, sai ya nuna musu hannuwansa da ƙafafunsa.
And this having said (He showed *N(k)O*) to them the hands and the feet.
41 Kuma har yanzu, suna cikin rashin gaskatawa, saboda murna da mamaki, sai ya tambaye su, “Kuna da abinci a nan?”
Still now while are disbelieving they for the joy and amazement He said to them; Have you anything to eat here?
42 Suka ba shi ɗan gasasshen kifi,
And they gave to Him of a fish broiled part (and from honeycomb tablet. *KO*)
43 ya karɓa ya ci a gabansu.
And having taken [it] before them He ate [it].
44 Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da na gaya muku tun ina tare da ku cewa, dole a cika kome da aka rubuta game da ni, a cikin Dokar Musa, da Annabawa, da kuma Zabura.”
He said now (unto *no*) (to them; *N(k)O*) These [are] the words (of mine *NO*) which I spoke to you still being with you that it behooves to be fulfilled all things which written in the law of Moses and (in the *no*) Prophets and in [the] Psalms concerning Me.
45 Sai ya wayar da tunaninsu don su fahimci Nassi.
Then He opened their mind to understand the Scriptures
46 Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da aka rubuta, cewa dole Kiristi yă sha wahala, a rana ta uku kuma yă tashi daga matattu.
And He said to them that Thus it has been written (and thus it was necessary for *K*) Was to suffer the Christ and to rise out from [the] dead on the third day
47 Kuma a cikin sunansa za a yi wa’azin tuba da gafarar zunubai, ga dukan ƙasashe. Za a kuwa fara daga Urushalima.
and to be proclaimed in the name of Him repentance (to *N(K)O*) forgiveness of sins to all nations (having begun *N(k)O*) from Jerusalem.
48 Ku ne shaidun waɗannan abubuwa.
You yourselves (now *k*) (are *ko*) witnesses of these things,
49 Zan aika muku da abin da Ubana ya yi alkawari. Amma ku dakata a birnin tukuna, sai an rufe ku da iko daga sama.”
And behold (I myself am sending *NK(o)*) the promise of the Father of Mine upon you. you yourselves however do remain in the city (Jerusalem *k*) until that you may be clothed with from on high power.
50 Bayan ya kai su waje kusa da Betani, sai ya ɗaga hannuwansa ya sa musu albarka.
He led now them out until (to *N(k)O*) Bethany, and having lifted up the hands of Him He blessed them.
51 Yana cikin sa musu albarka, sai ya rabu da su. Aka ɗauke shi zuwa cikin sama.
And it came to pass during the blessing by Him them He was separated from them and was carried up into heaven.
52 Sai suka yi masa sujada, suka koma Urushalima cike da murna sosai.
And they themselves having worshiped Him returned to Jerusalem with joy great
53 Sai suka ci gaba da zama a cikin haikalin, suna yabon Allah.
and were (through *N(K)O*) (all [times] *N(k)O*) in the temple (praising and *KO*) blessing God. (Amen *K*)