< Luka 24 >

1 Da sassafe a ranar farko ta mako, matan suka je kabarin, da kayan ƙanshin da suka shirya.
But at early morning dawn on the first day of the week (Nissan 17, the day of First Fruits #1), they and some others came to the tomb, bringing the spices which they had prepared.
2 Suka iske an riga an gungurar da dutsen daga bakin kabarin.
They found the stone rolled away from the tomb.
3 Amma da suka shiga ciki, ba su iske jikin Ubangiji Yesu ba.
They entered in, and didn’t find the Master Yeshua's [Salvation]'s body.
4 Yayinda suna cikin tunani a kan wannan, nan take, ga waɗansu mutum biyu tsaye kusa da su, sanye da kaya masu ƙyalli, kamar walƙiya.
While they were greatly perplexed about this, behold, two men stood by them in dazzling clothing.
5 A cikin tsoro, matan suka fāɗi da fuskokinsu a ƙasa, amma mutanen suka ce musu, “Me ya sa kuke neman mai rai a cikin matattu?
Becoming terrified, they bowed their faces down to the earth. They said to them, “Why do you seek the living among the dead?
6 Ba ya nan, ya tashi! Ku tuna yadda ya gaya muku tun yana tare da ku a Galili cewa,
He is not here, but is risen. Remember what he told you when he was still in Galilee [District, Circuit],
7 ‘Dole a ba da Ɗan Mutum ga hannun masu zunubi, a kuma gicciye shi, a rana ta uku kuma a tashe shi.’”
saying that the Son of Man must be delivered up into the hands of sinners devoted to sin ·miss the marks and be without share in the goal (and stained by definite crime vice)·, and be executed on the stake, and the third day rise again?”
8 Sai suka tuna da maganarsa.
They remembered his words,
9 Da suka dawo daga kabarin, sai suka faɗa wa Sha Ɗayan nan da sauransu, dukan waɗannan abubuwa.
teshuvah ·completely returned· from the tomb, and told all these things to the eleven, and to all the rest.
10 Matan da suka gaya wa manzannin waɗannan abubuwa su ne, Maryamu Magdalin, da Yowanna, da Maryamu uwar Yaƙub, da waɗansu da suke tare da su.
Now they were Mary of Magdala [Rebellion of City tower], Joanna, and Mary [Rebellion] the mother of James [Surplanter]. The other women with them told these things to the apostles.
11 Amma ba su gaskata matan ba, domin sun ɗauki kalmominsu wani zancen banza ne.
These words seemed to them to be nonsense, and they didn’t trust them.
12 Duk da haka, Bitrus ya tashi a guje zuwa kabarin. Da ya sunkuya, sai ya ga ƙyallayen lilin kaɗai a kwance. Sai ya koma yana tunani a ransa, a kan abin da ya faru.
But Peter [Rock] got up and ran to the tomb. Stooping and looking in, he saw the strips of linen lying by themselves, and he departed to his home, wondering what had happened.
13 A wannan rana kuma, biyu daga cikinsu suna tafiya zuwa wani ƙauye, da ake kira Emmawus, da suke kusan mil bakwai daga Urushalima.
Behold, two of them were going that same day (Nissan 17) to a village named Emmaus, which was sixty stadia [7.93 mi; 11.1 km] from Jerusalem [City of peace].
14 Suna magana da juna a kan dukan abubuwan da suka faru.
They talked with each other about all of these things which had happened.
15 Da suna magana, kuma suna tattauna waɗannan abubuwa da junansu, sai Yesu da kansa ya zo yana tafiya tare da su.
While they talked and questioned together, Yeshua [Salvation] himself came near, and went with them.
16 Amma ba a ba su ikon gane shi ba.
But their eyes were kept from recognizing him.
17 Sai ya tambaye, su ya ce, “Mene ne kuke tattaunawa da juna a cikin tafiyarku?” Suka tsaya shiru, da damuwa a fuskarsu.
He said to them, “What are you talking about as you walk, and are sad?”
18 Ɗaya daga cikinsu, mai suna Kiliyobas, ya tambaye shi ya ce, “Ashe, kai baƙo ne a Urushalima, da ba ka san abubuwan da suka faru a can, a cikin kwanakin nan ba?”
One of them, named Cleopas, answered him, “Are you the only stranger in Jerusalem [City of peace] who does not know the things which have happened there in these days?”
19 Sai ya yi tambaya, “Waɗanne abubuwa?” Suka amsa suka ce, “Game da Yesu Banazare. Shi annabi ne, mai iko ne kuma cikin ayyukansa da maganarsa, a gaban Allah da kuma dukan mutane.
He said to them, “What things?” They said to him, “The things concerning Yeshua [Salvation], the Nazarene [person from Branch, Separated one], who was a prophet mighty in deed and word before God and all the people;
20 Manyan firistoci da masu mulkinmu sun ba da shi a yi masa hukuncin mutuwa, suka kuwa gicciye shi.
and how the chief priests and our rulers delivered him up to be condemned to death, and nailed him to the stake.
21 Amma da, muna sa zuciya cewa, shi ne wanda zai fanshi Isra’ila. Bugu da ƙari kuma yau kwana uku ke nan tun da wannan abin ya faru.
But we were hoping that it was he who would redeem Israel [God prevails]. Yes, and besides all this, it is now the third day since these things happened.
22 Har wa yau, waɗansu daga cikin matanmu sun ba mu mamaki. Sun je kabarin da sassafen nan,
Also, certain women of our company amazed us, having arrived early at the tomb;
23 amma ba su sami jikinsa ba. Sun dawo sun faɗa mana cewa, sun ga wahayi na mala’iku, da suka ce yana da rai.
and when they didn’t find his body, they came saying that they had also seen a vision of angels, who said that he was alive.
24 Sa’an nan, waɗansu abokanmu suka je kabarin, suka kuma tarar da kome kamar yadda matan suka faɗa, amma shi, ba su gan shi ba.”
Some of us went to the tomb, and found it just like the women had said, but they didn’t see him.”
25 Sai ya ce musu, “Ashe, ku marasa azanci ne, masu nauyin zuciyar gaskata, da dukan abin da annabawa suka faɗa!
He said to them, “Foolish men, and slow of heart to trust in all that the prophets have spoken!
26 Ai, dole Kiristi yă sha waɗannan wahalolin, kafin yă shiga ɗaukakarsa.
Didn’t the Messiah [Anointed one] have to suffer these things and to enter into his glory?”
27 Sai ya fara bayyana musu daga Musa da dukan Annabawa, abin da dukan Nassi ya faɗa a kansa.”
Beginning from Moses [Drawn out] and from all the prophets, he explained to them in all the Scriptures the things concerning himself.
28 Da suka yi kusa da ƙauyen da za su, sai Yesu ya yi kamar zai ci gaba.
They came near to the village, where they were going, and he acted like he would go further.
29 Amma suka matsa masa suka ce, “Sauka wurinmu, don dare ya kusa, rana ta kusa fāɗuwa.” Sai ya sauka wurinsu.
They urged him, saying, “Stay with us, for it is almost evening, and the day is almost over. (Finish of Nissan 17, nearing to the start of Nissan 18.)” He went in to stay with them.
30 Da ya zauna a tebur tare da su, sai ya ɗauki burodi, ya yi godiya, ya kakkarya ya fara ba su.
When he had sat down at the table with them, he took the matzah ·unleavened bread· and gave thanks. Breaking it, he gave to them.
31 Sa’an nan idanunsu suka buɗe, suka gane shi. Sai ya ɓace musu.
Their eyes were opened, and they recognized him, and he vanished out of their sight.
32 Suka tambayi juna, “Ashe, shi ya sa zukatanmu suka kuna a cikinmu, sa’ad da yake magana da mu a hanya, yana bayyana mana Nassi.”
They said to one another, “Did not our hearts burn within us, while he spoke to us along the way, and while he opened the Scriptures to us?”
33 Suka tashi nan da nan suka koma Urushalima. A can suka sami Sha Ɗayan nan da waɗanda suke tare da su a wuri ɗaya,
They rose up that very hour, teshuvah ·completely returned· to Jerusalem [City of peace], and found the eleven gathered together, and those who were with them,
34 suna cewa, “Gaskiya ne! Ubangiji ya tashi, ya kuma bayyana ga Siman”
saying, “The Master is risen indeed, and has appeared to Simeon [Hearing]!”
35 Sai su biyun nan suka ba da labarin abin da ya faru a hanya, da kuma yadda suka gane Yesu yayinda ya kakkarya burodin.
They related the things that happened along the way, and how he was recognized by them in the breaking of the matzah ·unleavened bread·.
36 Suna cikin wannan zance, sai ga Yesu da kansa tsaye a tsakiyarsu. Sai ya ce musu, “Salama a gare ku!”
As they said these things, Yeshua [Salvation] himself stood among them, and said to them, “Peace be to you; Ena Na [I AM (the Living God)], do not be afraid.”
37 Suka firgita, suka tsorota, suna tsammani fatalwa ce suka gani.
But they were terrified and filled with fear, and supposed that they had seen a spirit.
38 Sai ya ce musu, “Don me kuke damuwa, kuke kuma shakka a zuciyarku?
He said to them, “Why are you troubled? Why do doubts arise in your hearts?
39 Ku duba hannuwana da ƙafafuna. Ai, ni ne da kaina! Ku taɓa ni ku ji, ai, fatalwa ba ta da nama da ƙashi, yadda kuke gani nake da su.”
See my hands and my feet, that it is truly me. Touch me and see, for a spirit does not have flesh and bones, as you see that I have.”
40 Da ya faɗi haka, sai ya nuna musu hannuwansa da ƙafafunsa.
When he had said this, he showed them his hands and his feet.
41 Kuma har yanzu, suna cikin rashin gaskatawa, saboda murna da mamaki, sai ya tambaye su, “Kuna da abinci a nan?”
While they still didn’t trust for joy, and wondered, he said to them, “Do you have anything here to eat?”
42 Suka ba shi ɗan gasasshen kifi,
They gave him a piece of a broiled fish and some honeycomb.
43 ya karɓa ya ci a gabansu.
He took them, and ate in front of them.
44 Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da na gaya muku tun ina tare da ku cewa, dole a cika kome da aka rubuta game da ni, a cikin Dokar Musa, da Annabawa, da kuma Zabura.”
He said to them, “This is what I told you, while I was still with you, that all things which are written in the Torah ·Teaching· of Moses [Drawn out], the Prophets, and the Psalms [Praises], concerning me must be fulfilled.”
45 Sai ya wayar da tunaninsu don su fahimci Nassi.
Then he opened their minds, that they might understand the Scriptures.
46 Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da aka rubuta, cewa dole Kiristi yă sha wahala, a rana ta uku kuma yă tashi daga matattu.
He said to them, “Thus it is written, and thus it was necessary for the Messiah [Anointed one] to suffer and to rise from the dead the third day,
47 Kuma a cikin sunansa za a yi wa’azin tuba da gafarar zunubai, ga dukan ƙasashe. Za a kuwa fara daga Urushalima.
and in his name teshuvah ·complete repentance· and remission of abstract sins ·miss the marks· should be preached to all the nations, starting with Jerusalem [City of peace].
48 Ku ne shaidun waɗannan abubuwa.
You are witnesses of these things.
49 Zan aika muku da abin da Ubana ya yi alkawari. Amma ku dakata a birnin tukuna, sai an rufe ku da iko daga sama.”
Behold, I send out the promise of 'Avi ·my Father· on you. But wait in the city of Jerusalem [City of peace] until you are clothed with power from on high.”
50 Bayan ya kai su waje kusa da Betani, sai ya ɗaga hannuwansa ya sa musu albarka.
He led them out as far as Bethany [House of affliction], and he lifted up his hands, and blessed them.
51 Yana cikin sa musu albarka, sai ya rabu da su. Aka ɗauke shi zuwa cikin sama.
While he blessed them, he withdrew from them, and was carried up into heaven.
52 Sai suka yi masa sujada, suka koma Urushalima cike da murna sosai.
They worshiped him, and teshuvah ·completely returned· to Jerusalem [City of peace] with great joy,
53 Sai suka ci gaba da zama a cikin haikalin, suna yabon Allah.
and were continually in the temple, praising and blessing God. Amen ·So be it·.

< Luka 24 >