< Luka 24 >

1 Da sassafe a ranar farko ta mako, matan suka je kabarin, da kayan ƙanshin da suka shirya.
Now upon the first day of the week, very early in the morning, they came unto the sepulchre, bringing the spices which they had prepared, and certain others with them.
2 Suka iske an riga an gungurar da dutsen daga bakin kabarin.
And they found the stone rolled away from the sepulchre.
3 Amma da suka shiga ciki, ba su iske jikin Ubangiji Yesu ba.
And they entered in, and found not the body of the Lord Jesus.
4 Yayinda suna cikin tunani a kan wannan, nan take, ga waɗansu mutum biyu tsaye kusa da su, sanye da kaya masu ƙyalli, kamar walƙiya.
And it came to pass, as they were much perplexed thereabout, behold, two men stood by them in shining garments:
5 A cikin tsoro, matan suka fāɗi da fuskokinsu a ƙasa, amma mutanen suka ce musu, “Me ya sa kuke neman mai rai a cikin matattu?
And as they were afraid, and bowed down their faces to the earth, they said unto them, Why seek ye the living among the dead?
6 Ba ya nan, ya tashi! Ku tuna yadda ya gaya muku tun yana tare da ku a Galili cewa,
He is not here, but is risen: remember how he spake unto you when he was yet in Galilee,
7 ‘Dole a ba da Ɗan Mutum ga hannun masu zunubi, a kuma gicciye shi, a rana ta uku kuma a tashe shi.’”
Saying, The Son of man must be delivered into the hands of sinful men, and be crucified, and the third day rise again.
8 Sai suka tuna da maganarsa.
And they remembered his words,
9 Da suka dawo daga kabarin, sai suka faɗa wa Sha Ɗayan nan da sauransu, dukan waɗannan abubuwa.
And returned from the sepulchre, and told all these things unto the eleven, and to all the rest.
10 Matan da suka gaya wa manzannin waɗannan abubuwa su ne, Maryamu Magdalin, da Yowanna, da Maryamu uwar Yaƙub, da waɗansu da suke tare da su.
It was Mary Magdalene, and Joanna, and Mary the mother of James, and other women that were with them, which told these things unto the apostles.
11 Amma ba su gaskata matan ba, domin sun ɗauki kalmominsu wani zancen banza ne.
And their words seemed to them as idle tales, and they believed them not.
12 Duk da haka, Bitrus ya tashi a guje zuwa kabarin. Da ya sunkuya, sai ya ga ƙyallayen lilin kaɗai a kwance. Sai ya koma yana tunani a ransa, a kan abin da ya faru.
Then arose Peter, and ran unto the sepulchre; and stooping down, he beheld the linen clothes laid by themselves, and departed, wondering in himself at that which was come to pass.
13 A wannan rana kuma, biyu daga cikinsu suna tafiya zuwa wani ƙauye, da ake kira Emmawus, da suke kusan mil bakwai daga Urushalima.
And, behold, two of them went that same day to a village called Emmaus, which was from Jerusalem about threescore furlongs.
14 Suna magana da juna a kan dukan abubuwan da suka faru.
And they talked together of all these things which had happened.
15 Da suna magana, kuma suna tattauna waɗannan abubuwa da junansu, sai Yesu da kansa ya zo yana tafiya tare da su.
And it came to pass, that, while they communed together and reasoned, Jesus himself drew near, and went with them.
16 Amma ba a ba su ikon gane shi ba.
But their eyes were holden that they should not know him.
17 Sai ya tambaye, su ya ce, “Mene ne kuke tattaunawa da juna a cikin tafiyarku?” Suka tsaya shiru, da damuwa a fuskarsu.
And he said unto them, What manner of communications are these that ye have one to another, as ye walk, and are sad?
18 Ɗaya daga cikinsu, mai suna Kiliyobas, ya tambaye shi ya ce, “Ashe, kai baƙo ne a Urushalima, da ba ka san abubuwan da suka faru a can, a cikin kwanakin nan ba?”
And the one of them, whose name was Cleopas, answering said unto him, Art thou only a stranger in Jerusalem, and hast not known the things which are come to pass there in these days?
19 Sai ya yi tambaya, “Waɗanne abubuwa?” Suka amsa suka ce, “Game da Yesu Banazare. Shi annabi ne, mai iko ne kuma cikin ayyukansa da maganarsa, a gaban Allah da kuma dukan mutane.
And he said unto them, What things? And they said unto him, Concerning Jesus of Nazareth, which was a prophet mighty in deed and word before God and all the people:
20 Manyan firistoci da masu mulkinmu sun ba da shi a yi masa hukuncin mutuwa, suka kuwa gicciye shi.
And how the chief priests and our rulers delivered him to be condemned to death, and have crucified him.
21 Amma da, muna sa zuciya cewa, shi ne wanda zai fanshi Isra’ila. Bugu da ƙari kuma yau kwana uku ke nan tun da wannan abin ya faru.
But we trusted that it had been he which should have redeemed Israel: and beside all this, to day is the third day since these things were done.
22 Har wa yau, waɗansu daga cikin matanmu sun ba mu mamaki. Sun je kabarin da sassafen nan,
Yea, and certain women also of our company made us astonished, which were early at the sepulchre;
23 amma ba su sami jikinsa ba. Sun dawo sun faɗa mana cewa, sun ga wahayi na mala’iku, da suka ce yana da rai.
And when they found not his body, they came, saying, that they had also seen a vision of angels, which said that he was alive.
24 Sa’an nan, waɗansu abokanmu suka je kabarin, suka kuma tarar da kome kamar yadda matan suka faɗa, amma shi, ba su gan shi ba.”
And certain of them which were with us went to the sepulchre, and found it even so as the women had said: but him they saw not.
25 Sai ya ce musu, “Ashe, ku marasa azanci ne, masu nauyin zuciyar gaskata, da dukan abin da annabawa suka faɗa!
Then he said unto them, O fools, and slow of heart to believe all that the prophets have spoken:
26 Ai, dole Kiristi yă sha waɗannan wahalolin, kafin yă shiga ɗaukakarsa.
Ought not Christ to have suffered these things, and to enter into his glory?
27 Sai ya fara bayyana musu daga Musa da dukan Annabawa, abin da dukan Nassi ya faɗa a kansa.”
And beginning at Moses and all the prophets, he expounded unto them in all the scriptures the things concerning himself.
28 Da suka yi kusa da ƙauyen da za su, sai Yesu ya yi kamar zai ci gaba.
And they drew nigh unto the village, whither they went: and he made as though he would have gone further.
29 Amma suka matsa masa suka ce, “Sauka wurinmu, don dare ya kusa, rana ta kusa fāɗuwa.” Sai ya sauka wurinsu.
But they constrained him, saying, Abide with us: for it is toward evening, and the day is far spent. And he went in to tarry with them.
30 Da ya zauna a tebur tare da su, sai ya ɗauki burodi, ya yi godiya, ya kakkarya ya fara ba su.
And it came to pass, as he sat at meat with them, he took bread, and blessed it, and brake, and gave to them.
31 Sa’an nan idanunsu suka buɗe, suka gane shi. Sai ya ɓace musu.
And their eyes were opened, and they knew him; and he vanished out of their sight.
32 Suka tambayi juna, “Ashe, shi ya sa zukatanmu suka kuna a cikinmu, sa’ad da yake magana da mu a hanya, yana bayyana mana Nassi.”
And they said one to another, Did not our heart burn within us, while he talked with us by the way, and while he opened to us the scriptures?
33 Suka tashi nan da nan suka koma Urushalima. A can suka sami Sha Ɗayan nan da waɗanda suke tare da su a wuri ɗaya,
And they rose up the same hour, and returned to Jerusalem, and found the eleven gathered together, and them that were with them,
34 suna cewa, “Gaskiya ne! Ubangiji ya tashi, ya kuma bayyana ga Siman”
Saying, The Lord is risen indeed, and hath appeared to Simon.
35 Sai su biyun nan suka ba da labarin abin da ya faru a hanya, da kuma yadda suka gane Yesu yayinda ya kakkarya burodin.
And they told what things were done in the way, and how he was known of them in breaking of bread.
36 Suna cikin wannan zance, sai ga Yesu da kansa tsaye a tsakiyarsu. Sai ya ce musu, “Salama a gare ku!”
And as they thus spake, Jesus himself stood in the midst of them, and saith unto them, Peace be unto you.
37 Suka firgita, suka tsorota, suna tsammani fatalwa ce suka gani.
But they were terrified and affrighted, and supposed that they had seen a spirit.
38 Sai ya ce musu, “Don me kuke damuwa, kuke kuma shakka a zuciyarku?
And he said unto them, Why are ye troubled? and why do thoughts arise in your hearts?
39 Ku duba hannuwana da ƙafafuna. Ai, ni ne da kaina! Ku taɓa ni ku ji, ai, fatalwa ba ta da nama da ƙashi, yadda kuke gani nake da su.”
Behold my hands and my feet, that it is I myself: handle me, and see; for a spirit hath not flesh and bones, as ye see me have.
40 Da ya faɗi haka, sai ya nuna musu hannuwansa da ƙafafunsa.
And when he had thus spoken, he shewed them his hands and his feet.
41 Kuma har yanzu, suna cikin rashin gaskatawa, saboda murna da mamaki, sai ya tambaye su, “Kuna da abinci a nan?”
And while they yet believed not for joy, and wondered, he said unto them, Have ye here any meat?
42 Suka ba shi ɗan gasasshen kifi,
And they gave him a piece of a broiled fish, and of an honeycomb.
43 ya karɓa ya ci a gabansu.
And he took it, and did eat before them.
44 Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da na gaya muku tun ina tare da ku cewa, dole a cika kome da aka rubuta game da ni, a cikin Dokar Musa, da Annabawa, da kuma Zabura.”
And he said unto them, These are the words which I spake unto you, while I was yet with you, that all things must be fulfilled, which were written in the law of Moses, and in the prophets, and in the psalms, concerning me.
45 Sai ya wayar da tunaninsu don su fahimci Nassi.
Then opened he their understanding, that they might understand the scriptures,
46 Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da aka rubuta, cewa dole Kiristi yă sha wahala, a rana ta uku kuma yă tashi daga matattu.
And said unto them, Thus it is written, and thus it behoved Christ to suffer, and to rise from the dead the third day:
47 Kuma a cikin sunansa za a yi wa’azin tuba da gafarar zunubai, ga dukan ƙasashe. Za a kuwa fara daga Urushalima.
And that repentance and remission of sins should be preached in his name among all nations, beginning at Jerusalem.
48 Ku ne shaidun waɗannan abubuwa.
And ye are witnesses of these things.
49 Zan aika muku da abin da Ubana ya yi alkawari. Amma ku dakata a birnin tukuna, sai an rufe ku da iko daga sama.”
And, behold, I send the promise of my Father upon you: but tarry ye in the city of Jerusalem, until ye be endued with power from on high.
50 Bayan ya kai su waje kusa da Betani, sai ya ɗaga hannuwansa ya sa musu albarka.
And he led them out as far as to Bethany, and he lifted up his hands, and blessed them.
51 Yana cikin sa musu albarka, sai ya rabu da su. Aka ɗauke shi zuwa cikin sama.
And it came to pass, while he blessed them, he was parted from them, and carried up into heaven.
52 Sai suka yi masa sujada, suka koma Urushalima cike da murna sosai.
And they worshipped him, and returned to Jerusalem with great joy:
53 Sai suka ci gaba da zama a cikin haikalin, suna yabon Allah.
And were continually in the temple, praising and blessing God. Amen.

< Luka 24 >