< Luka 24 >

1 Da sassafe a ranar farko ta mako, matan suka je kabarin, da kayan ƙanshin da suka shirya.
Then on the first day of the week, at early dawn, they went to the tomb carrying the spices they had prepared, along with some others.
2 Suka iske an riga an gungurar da dutsen daga bakin kabarin.
They found the stone rolled away from the tomb,
3 Amma da suka shiga ciki, ba su iske jikin Ubangiji Yesu ba.
but upon entering they did not find the body of the Lord Jesus.
4 Yayinda suna cikin tunani a kan wannan, nan take, ga waɗansu mutum biyu tsaye kusa da su, sanye da kaya masu ƙyalli, kamar walƙiya.
And it happened, as they were greatly perplexed about this, that wow, two men stood by them in dazzling clothing!
5 A cikin tsoro, matan suka fāɗi da fuskokinsu a ƙasa, amma mutanen suka ce musu, “Me ya sa kuke neman mai rai a cikin matattu?
Then, as they were afraid and bowed their faces to the ground, they said to them: “Why do you seek the living One among the dead?
6 Ba ya nan, ya tashi! Ku tuna yadda ya gaya muku tun yana tare da ku a Galili cewa,
He is not here, but is risen! Remember how He told you while still in Galilee,
7 ‘Dole a ba da Ɗan Mutum ga hannun masu zunubi, a kuma gicciye shi, a rana ta uku kuma a tashe shi.’”
saying, ‘The Son of the Man must be delivered into the hands of sinful men, and be crucified, and the third day rise again.’”
8 Sai suka tuna da maganarsa.
And they remembered His words.
9 Da suka dawo daga kabarin, sai suka faɗa wa Sha Ɗayan nan da sauransu, dukan waɗannan abubuwa.
Then they returned from the tomb and reported all these things to the Eleven, and to all the rest.
10 Matan da suka gaya wa manzannin waɗannan abubuwa su ne, Maryamu Magdalin, da Yowanna, da Maryamu uwar Yaƙub, da waɗansu da suke tare da su.
They were Mary Magdalene, Joanna, Mary the mother of James, and the others with them, who told these things to the apostles.
11 Amma ba su gaskata matan ba, domin sun ɗauki kalmominsu wani zancen banza ne.
But their words seemed to them like nonsense, and they disbelieved them.
12 Duk da haka, Bitrus ya tashi a guje zuwa kabarin. Da ya sunkuya, sai ya ga ƙyallayen lilin kaɗai a kwance. Sai ya koma yana tunani a ransa, a kan abin da ya faru.
(But Peter had gotten up and run to the tomb, and stooping down he saw the linen strips lying by themselves; and he departed, marveling to himself at what had happened.)
13 A wannan rana kuma, biyu daga cikinsu suna tafiya zuwa wani ƙauye, da ake kira Emmawus, da suke kusan mil bakwai daga Urushalima.
And then that same day two of them were going to a village called Emmaus, which was about seven miles from Jerusalem.
14 Suna magana da juna a kan dukan abubuwan da suka faru.
And they were conversing with each other about all that had happened.
15 Da suna magana, kuma suna tattauna waɗannan abubuwa da junansu, sai Yesu da kansa ya zo yana tafiya tare da su.
And then, as they were conversing and discussing, Jesus Himself came up and started going with them.
16 Amma ba a ba su ikon gane shi ba.
But their eyes were restrained, in order that they not recognize Him.
17 Sai ya tambaye, su ya ce, “Mene ne kuke tattaunawa da juna a cikin tafiyarku?” Suka tsaya shiru, da damuwa a fuskarsu.
So He said to them, “What words are these that you are exchanging with one another as you walk, and are gloomy?”
18 Ɗaya daga cikinsu, mai suna Kiliyobas, ya tambaye shi ya ce, “Ashe, kai baƙo ne a Urushalima, da ba ka san abubuwan da suka faru a can, a cikin kwanakin nan ba?”
Then the one whose name was Cleopas answered and said to Him, “Are you the only one living in Jerusalem who doesn't know the things that have happened there in these days?”
19 Sai ya yi tambaya, “Waɗanne abubuwa?” Suka amsa suka ce, “Game da Yesu Banazare. Shi annabi ne, mai iko ne kuma cikin ayyukansa da maganarsa, a gaban Allah da kuma dukan mutane.
He said to them, “What things?” So they said to Him: “The things concerning Jesus the Natsorean, how the man was a prophet mighty in deed and word before God and all the people,
20 Manyan firistoci da masu mulkinmu sun ba da shi a yi masa hukuncin mutuwa, suka kuwa gicciye shi.
and how the chief priests and our rulers handed him over to be condemned to death, and they crucified him.
21 Amma da, muna sa zuciya cewa, shi ne wanda zai fanshi Isra’ila. Bugu da ƙari kuma yau kwana uku ke nan tun da wannan abin ya faru.
And we were hoping that it was He who was going to redeem Israel! Further, besides all this, today is the third day since these things happened.
22 Har wa yau, waɗansu daga cikin matanmu sun ba mu mamaki. Sun je kabarin da sassafen nan,
Moreover certain women of our group astonished us—arriving early at the tomb,
23 amma ba su sami jikinsa ba. Sun dawo sun faɗa mana cewa, sun ga wahayi na mala’iku, da suka ce yana da rai.
and not finding his body, they came saying that they had even seen a vision of angels, who said he was alive.
24 Sa’an nan, waɗansu abokanmu suka je kabarin, suka kuma tarar da kome kamar yadda matan suka faɗa, amma shi, ba su gan shi ba.”
And certain of those who were with us went to the tomb and found it just as the women had said; but him they did not see.”
25 Sai ya ce musu, “Ashe, ku marasa azanci ne, masu nauyin zuciyar gaskata, da dukan abin da annabawa suka faɗa!
Then He said to them: “O foolish ones, and slow of heart to believe in all that the Prophets have spoken!
26 Ai, dole Kiristi yă sha waɗannan wahalolin, kafin yă shiga ɗaukakarsa.
Was it really not necessary for the Christ to suffer these things, and to enter into His glory?”
27 Sai ya fara bayyana musu daga Musa da dukan Annabawa, abin da dukan Nassi ya faɗa a kansa.”
And beginning from Moses, and then all the Prophets, He explained to them in all the Scriptures the things concerning Himself.
28 Da suka yi kusa da ƙauyen da za su, sai Yesu ya yi kamar zai ci gaba.
Then they approached the village where they were going, and He made as though He would keep going.
29 Amma suka matsa masa suka ce, “Sauka wurinmu, don dare ya kusa, rana ta kusa fāɗuwa.” Sai ya sauka wurinsu.
But they constrained Him, saying, “Stay with us, because it is toward evening, and the day is far spent.” So He went in to stay with them.
30 Da ya zauna a tebur tare da su, sai ya ɗauki burodi, ya yi godiya, ya kakkarya ya fara ba su.
And then, as He was reclining with them, He took the bread, blessed and broke it, and gave it to them.
31 Sa’an nan idanunsu suka buɗe, suka gane shi. Sai ya ɓace musu.
Then their eyes were opened and they recognized Him; and He became invisible to them.
32 Suka tambayi juna, “Ashe, shi ya sa zukatanmu suka kuna a cikinmu, sa’ad da yake magana da mu a hanya, yana bayyana mana Nassi.”
They said to one another, “Were not our hearts burning within us while He talked to us on the road, and while He opened the Scriptures to us?”
33 Suka tashi nan da nan suka koma Urushalima. A can suka sami Sha Ɗayan nan da waɗanda suke tare da su a wuri ɗaya,
So they got up forthwith and returned to Jerusalem, where they found the Eleven gathered together; also those with them,
34 suna cewa, “Gaskiya ne! Ubangiji ya tashi, ya kuma bayyana ga Siman”
who said, “The Lord is risen indeed, and has appeared to Simon!”
35 Sai su biyun nan suka ba da labarin abin da ya faru a hanya, da kuma yadda suka gane Yesu yayinda ya kakkarya burodin.
Then they described what happened on the road, and how He was known to them in the breaking of the bread.
36 Suna cikin wannan zance, sai ga Yesu da kansa tsaye a tsakiyarsu. Sai ya ce musu, “Salama a gare ku!”
As they were saying these things, indeed, Jesus Himself stood in their midst, and He said to them, “Peace to you.”
37 Suka firgita, suka tsorota, suna tsammani fatalwa ce suka gani.
But they, terrified, supposed they were seeing a ghost, and were becoming fearful.
38 Sai ya ce musu, “Don me kuke damuwa, kuke kuma shakka a zuciyarku?
And He said to them: “Why are you troubled?” and “Why do doubts arise in your hearts?
39 Ku duba hannuwana da ƙafafuna. Ai, ni ne da kaina! Ku taɓa ni ku ji, ai, fatalwa ba ta da nama da ƙashi, yadda kuke gani nake da su.”
Look at my hands and feet; it is I myself! Feel me and see; a spirit does not have flesh and bones, as you see I have.”
40 Da ya faɗi haka, sai ya nuna musu hannuwansa da ƙafafunsa.
And saying this He showed them His hands and His feet.
41 Kuma har yanzu, suna cikin rashin gaskatawa, saboda murna da mamaki, sai ya tambaye su, “Kuna da abinci a nan?”
But as they were still disbelieving and marveling, because of the joy, He said to them, “Do you have any food here?”
42 Suka ba shi ɗan gasasshen kifi,
So they gave Him a piece of broiled fish and some honeycomb.
43 ya karɓa ya ci a gabansu.
And taking it He ate in their presence.
44 Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da na gaya muku tun ina tare da ku cewa, dole a cika kome da aka rubuta game da ni, a cikin Dokar Musa, da Annabawa, da kuma Zabura.”
Then He said to them, “These are the words that I spoke to you while I was still with you, that everything that is written in the Law of Moses and the Prophets and the Psalms concerning me must be fulfilled.”
45 Sai ya wayar da tunaninsu don su fahimci Nassi.
Then He opened their understanding so as to comprehend the Scriptures.
46 Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da aka rubuta, cewa dole Kiristi yă sha wahala, a rana ta uku kuma yă tashi daga matattu.
And He said to them: “Thus it is written, and thus it was necessary for the Christ to suffer and to rise from the dead the third day,
47 Kuma a cikin sunansa za a yi wa’azin tuba da gafarar zunubai, ga dukan ƙasashe. Za a kuwa fara daga Urushalima.
and that repentance and forgiveness of sins should be proclaimed in His name to all the nations, beginning from Jerusalem.
48 Ku ne shaidun waɗannan abubuwa.
You are witnesses of these things.
49 Zan aika muku da abin da Ubana ya yi alkawari. Amma ku dakata a birnin tukuna, sai an rufe ku da iko daga sama.”
Take note, I am sending the Promise of my Father upon you; but you must stay in the city of Jerusalem until you are clothed with power from on High.”
50 Bayan ya kai su waje kusa da Betani, sai ya ɗaga hannuwansa ya sa musu albarka.
He led them out as far as Bethany, and lifting up His hands He blessed them.
51 Yana cikin sa musu albarka, sai ya rabu da su. Aka ɗauke shi zuwa cikin sama.
And it happened, as He was blessing them, that He left them and was carried up into heaven.
52 Sai suka yi masa sujada, suka koma Urushalima cike da murna sosai.
Worshiping Him, they returned to Jerusalem with great joy;
53 Sai suka ci gaba da zama a cikin haikalin, suna yabon Allah.
and they were continually in the temple, praising and blessing God. Amen.

< Luka 24 >