< Luka 23 >
1 Sai dukan majalisa suka tashi, suka kai shi gaban Bilatus.
And the assembly broke up, and conducted Jesus to Pilate:
2 Suka fara zarginsa suna cewa, “Mun sami wannan mutum yana rikitar da al’ummarmu. Yana hana a biya haraji ga Kaisar. Yana kuma cewa, shi Kiristi ne, sarki kuma.”
and they accused him, saying, We found this man perverting the nation, and forbidding to give tribute to Cesar, calling himself Messiah the King.
3 Sai Bilatus ya tambayi Yesu ya ce, “Kai ne sarkin Yahudawa?” Yesu ya amsa ya ce, “I, haka yake, kamar yadda ka faɗa.”
Then Pilate, asking him, said, You are the King of the Jews? He answered, You say right.
4 Sai Bilatus ya sanar wa manyan firistoci da taron ya ce, “Ni fa, ban sami wani ainihin abin zargi game wannan mutum nan ba.”
Pilate said to the chief priests and the multitude, I find nothing criminal in this man.
5 Amma suka nace, suna cewa, “Yana tā da hankulan mutane, ko’ina a Yahudiya da koyarwarsa. Ya fara daga Galili, ga shi har ya kai nan.”
But they became more vehement, adding, He raised sedition among the people, by the doctrine which he spread through all Judea, from Galilee, where he began, to this place.
6 Da Bilatus ya ji haka, sai ya yi tambaya, “Ko shi mutumin Galili ne?”
When Pilate heard them mention Galilee, he asked, whether the man were a Galilean.
7 Da ya ji cewa, Yesu yana ƙarƙashin mulkin Hiridus ne, sai ya aika da shi zuwa wurin Hiridus, don a lokacin Hiridus yana Urushalima.
And finding that he belonged to Herod's jurisdiction, he sent him to Herod, who was also then at Jerusalem.
8 Da Hiridus ya ga Yesu, sai ya yi murna ƙwarai, don tun dā ma yana marmari ya gan shi a kan abin da ya ji game da shi. Ya yi fata ya ga Yesu, yă kuma yi waɗansu ayyukan banmamaki.
And Herod was very glad to see Jesus: it was what he had long desired; having heard much of him, and hoping to see him perform some miracle.
9 Ya yi masa tambayoyi masu yawa, amma Yesu bai ba shi ko amsa ba.
He, therefore, asked him many questions, but Jesus returned him no answer.
10 Manyan firistoci da malaman dokoki suna tsaye a wurin, suna kawo zargi masu ƙarfi a kansa.
Yet the chief priests and the scribes, who were present, accused him with eagerness.
11 Sai Hiridus da sojojinsa suka wulaƙanta shi, suka yi masa ba’a. Sa’an nan, suka sa masa babban riga, suka mai da shi wurin Bilatus.
But Herod and his military train despised him: and having, in derision, arrayed him in a splendid robe, remanded him to Pilate.
12 A ranar, Hiridus da Bilatus suka zama abokan juna, don tun dā ma, su abokan gāba ne.
On that day, Pilate and Herod became friends; for, before, they had been at enmity.
13 Bilatus ya tara manyan firistoci, da masu mulki, da mutane,
Pilate, having convened the chief priests, the magistrates and the people,
14 ya ce musu, “Kun kawo mini wannan mutum, a matsayin wanda yana zuga mutane su yi tawaye. Na bincike shi a gabanku, ban ga a kan me kuka kawo kararsa ba.
said to them, You have brought this man before me, as one who excites the people to revolt; yet, having examined him in your presence, I have not found him guilt of any of those crimes of which you accuse him.
15 Haka ma Hiridus, shi ya sa ya dawo da shi nan wurinmu. Kamar yadda ku ma kun gani, ba abin da mutumin nan ya yi, da ya isa mutuwa.
Neither has Herod; for I referred you to him. Be assured, then, that he has done nothing to deserve death.
16 Saboda haka, zan yi masa bulala, in sāke shi.”
I will therefore chastise him, and release him.
For it was necessary that he should release one to them at the festival.
18 Suka yi ihu gaba ɗaya suka ce, “A yi gaba da wannan mutum! A sake mana Barabbas!”
Then all cried out together, Away with this man, and release to us Barabbas.
19 (Barabbas yana kurkuku saboda laifin tā da hankali a birnin, da kuma don kisankai.)
Now Barabbas had been imprisoned for raising sedition in the city, and for murder.
20 Sai Bilatus ya sāke yin musu magana don yana so ya saki Yesu.
Pilate, willing to release Jesus, again, expostulated.
21 Amma sai suka ci gaba da ihu, suna cewa, “A gicciye shi! A gicciye shi!”
But they cried, saying, Crucify! crucify him!
22 Ya sāke ce musu, sau na uku, “Don me? Wane laifi wannan mutum ya yi? Ni dai ban same shi da wani dalilin da ya isa a kashe shi ba. Saboda haka, zan sa a hore shi, sa’an nan in sāke shi.”
A third time he repeated, Why? What evil has this man done? I do not find him guilty of any capital crime; I will therefore chastise him, and release him.
23 Amma suna ihu, suna nacewa, suna cewa, dole a gicciye shi, har ihunsu ya rinjaye shi.
But they persisted, demanding, with much clamor, that he might be crucified. At last, their clamors, and those of the chief priests, prevailed:
24 Sai Bilatus ya biya bukatarsu da ya ji roƙonsu.
and Pilate pronounced sentence, that it should be as they desired.
25 Ya saki mutumin da aka jefa a kurkuku saboda tā da hankali, da kisankai, shi wanda suka roƙa. Sa’an nan ya ba da Yesu ga nufinsu.
Accordingly, he released a man who had been imprisoned for sedition and murder; whom they required; and gave up Jesus to their will.
26 Sa’ad da suna tafiya da Yesu, sai wani da ake kira Siman, mutumin Sairin, yana zuwa daga ƙauye. Suka kama shi, suka aza masa gicciyen, suka tilasta shi ya ɗauki gicciyen, ya bi Yesu a baya.
As they led him away, they laid hold of one Simon, a Cyrenian, coming from the country, and laid the cross on him, that he might bear it after Jesus.
27 Mutane da yawa sosai suka bi shi, a cikinsu ma da mata waɗanda suka yi makoki da kuka dominsa.
And a great multitude followed him, amongst whom were many women, who lamented and bewailed him.
28 Yesu ya juya, ya ce musu, “’Yan matan Urushalima, kada ku yi kuka saboda ni, amma ku yi kuka saboda kanku, da kuma saboda’ya’yanku.
But Jesus, turning to them, said, Daughters of Jerusalem, weep not for me, but weep for yourselves, and for your children:
29 Gama lokaci yana zuwa da za ku ce, ‘Masu albarka ne bakararru, wato, mata marasa haihuwa, da mahaihuwar da ba su taɓa haihuwa ba, da kuma mama da ba su taɓa shayar da nono ba!’
for the days are coming, in which they shall say, Happy the barren, the wombs which never bare, and the breasts which never gave suck!
30 Sa’an nan “‘za su ce wa duwatsu, “Ku fāɗi a kanmu!” Za su ce wa tuddai kuma, “Ku rufe mu!”’
Then they shall cry to the mountains, Fall on us; and to the hills, Cover us:
31 Gama in mutane suna yin waɗannan abubuwa a lokacin da itace na ɗanye, me zai faru in ya bushe?”
for if it fare thus with the green tree, how shall it fare with the dry?
32 Tare da shi akwai mutum biyu masu laifi, da aka tafi da su don a gicciye.
And two malefactors were also led with him to execution.
33 Da suka isa wurin da ake kira “Ƙoƙon Kai,” nan suka gicciye shi, tare da masu laifin nan, ɗaya a hannun damansa, ɗayan kuma a hagunsa.
When they came to the place called Calvary, they there nailed him to a cross, and the malefactors also; one at his right hand, the other at his left.
34 Yesu ya ce, “Ya Uba ka yi musu gafara, don ba su san abin da suke yi ba.” Suka rarraba tufafinsa ta wurin jefa ƙuri’a.
And Jesus said, Father, forgive them, for they know not what they do. And they parted his garments by lot.
35 Mutanen suka tsaya suna kallo. Har masu mulki ma suka yi masa ba’a, suna cewa, “Ya ceci waɗansu, to, ya ceci kansa in shi ne Kiristi na Allah, Zaɓaɓɓe.”
While the people stood gazing, even their rulers joined them in ridiculing him, and saying, This man saved others; let him save himself, if he be the Messiah, the elect of God.
36 Sojoji su ma, suka zo suka yi masa ba’a. Suka miƙa masa ruwan tsami.
The soldiers likewise mocked him, coming and offering him vinegar,
37 Suka ce, “In kai ne sarkin Yahudawa, ka ceci kanka mana.”
and saying, If you be the King of the Jews, save yourself.
38 Bisa da shi kuma akwai rubutun da ya ce, Wannan shi ne Sarkin Yahudawa.
There was also an inscription over his head in Greek, Latin, and Hebrew, THIS IS THE KING OF THE JEWS.
39 Ɗaya daga cikin masu laifin da aka gicciye a wurin ya zazzage shi ya ce, “Shin, ba kai ne Kiristi ba? To, ka ceci kanka, ka kuma cece mu mana!”
Now, one of the malefactors who suffered with him, reviled him, saying, If you be the Messiah, save yourself and us.
40 Amma ɗayan mai laifi ya kwaɓe shi ya ce, “Ba ka da tsoron Allah ne, wai saboda kana ƙarƙashin hukunci ɗaya tare da shi?
The other, rebuking him, answered, Have you no fear of God, you who are undergoing the same punishment?
41 Horonmu, daidai aka yi mana, sakamakon abin da muka yi ne. Amma wannan mutum, bai yi wani laifi ba.”
And we, indeed, justly; for we receive the due reward of our deeds: but this man has done nothing amiss.
42 Sai ya ce, “Yesu, ka tuna da ni sa’ad da ka shiga mulkinka.”
And he said to Jesus, Remember me, Lord, when thou comest to thy kingdom.
43 Yesu ya amsa, ya ce masa, “Gaskiya nake faɗa maka, yau ɗin nan, za ka kasance tare da ni, a mulkina a sama.”
Jesus answered, Indeed, I say to you, To-day you shall be with me in paradise.
44 Yanzu kuwa wajen sa’a ta shida ne, kuma duhu ya rufe ko’ina a ƙasar, har zuwa sa’a ta tara,
And, about the sixth hour, there was darkness over all the land, which lasted till the ninth.
45 domin rana ta daina haskakawa. Labulen da yake cikin haikali kuma ya yage kashi biyu.
The sun was darkened, and the vail of the temple was rent in the midst.
46 Yesu ya yi kira da babbar murya ya ce, “Ya Uba, na danƙa ruhuna a hannunka.” Da ya faɗi haka, sai ya ja numfashi na ƙarshe.
And Jesus said with a loud voice, Father, into thy hands I commit my spirit; and having thus said, he expired.
47 Da jarumin ya ga abin da ya faru, sai ya yabi Allah ya ce, “Gaskiya, wannan mutum mai adalci ne.”
Then, the centurion, observing what had happened, gave glory to God; saying, Assuredly, this was a righteous man.
48 Da dukan mutanen da suka taru, domin shaidar waɗannan abubuwa, suka ga abin da ya faru, sai suka buga ƙirjinsu suka tafi.
Nay, all the people who were present at this spectacle, and saw what had passed, returned, beating their breasts.
49 Amma dukan mutanen da suka san Yesu, tare da mata da suka bi shi daga Galili, suka tsaya daga nesa suna kallon abubuwan nan.
And all his acquaintance, and the women who had followed him from Galilee, standing at a distance, beheld these things.
50 Akwai wani mutum mai suna Yusuf, ɗan Majalisa, wanda shi nagari ne, mai adalci,
Now, there was a senator, named Joseph, a good and just man,
51 shi dā ma bai yarda da shawararsu, da kuma abin da suka yi ba. Shi daga Arimateya ne wani garin Yahudiya. Yana kuma jiran zuwa mulkin Allah.
from Arimathea, a city of Judea, who had not concurred in the resolutions and proceedings of the rest; and who himself, also expected the Reign of God.
52 Sai ya je wurin Bilatus ya roƙa a ba shi jikin Yesu.
This man went to Pilate, and begged the body of Jesus.
53 Sai ya saukar da jikin, ya nannaɗe shi a cikin zanen lilin, ya sa shi a wani kabari da aka fafe a cikin dutse, wadda ba a taɓa sa kowa ba.
And having taken it down, he wrapped it in linen, and laid it in a tomb cut in stone, in which no man had ever been deposited.
54 An yi haka ne a Ranar Shirye-shirye, ranar Asabbaci kuma yana dab da farawa.
Now that day was the preparation, and the Sabbath approached.
55 Matan da suka zo tare da Yesu, daga Galili suka bi Yusuf suka ga kabarin, da kuma yadda aka ajiye jikin.
And the women, who had accompanied Jesus from Galilee, followed Joseph, and observed the tomb, and how the body was laid.
56 Sa’an nan, suka koma gida, suka shirya kayan ƙanshi da turare. Amma suka huta a ranar Asabbaci don kiyaye doka.
When they returned, they provided spices and ointments, and then rested the Sabbath, according to the commandment.