< Luka 22 >

1 Yanzu fa, Bikin Burodi Marar Yistin da ake kira Bikin Ƙetarewa ya yi kusa,
Now the feast of unleavened bread, called the passover, being near,
2 manyan firistoci da malaman dokoki kuma suna neman yadda za su kashe Yesu a ɓoye, don suna tsoron mutane.
the chief priests and the scribes sought how they might kill him, for they feared the people.
3 Shaiɗan kuwa ya shiga Yahuda, wanda ake kira Iskariyot, ɗaya daga cikin Sha Biyun.
Then Satan entered into Judas, surnamed Iscariot, who was of the number of the twelve.
4 Sai Yahuda ya je ya tattauna da manyan firistoci, da ma’aikatan’yan gadin haikali, a kan yadda zai ba da Yesu a gare su.
And he went and concerted with the chief priests and officers, how he might deliver Jesus into their hands.
5 Suka kuwa yi murna, suka yarda su ba shi kuɗi.
And they were glad, and agreed to give him a certain sum,
6 Ya ko yarda, ya fara neman zarafin da zai ba da Yesu a gare su, sa’ad da taro ba sa nan tare da shi.
which Judas having accepted, watched an opportunity to deliver him up without tumult.
7 Sai ranar Bikin Burodi Marar Yisti ta kewayo, wato, ranar hadayar ɗan ragon kafara na Bikin Ƙetarewa.
Now, this day of unleavened bread being come, on which the passover must be sacrificed,
8 Sai Yesu ya aiki Bitrus da Yohanna, ya ce musu, “Ku je ku yi shirye-shiryen Bikin Ƙetarewar da za mu ci.”
Jesus sent Peter and John, saying, Go and prepare for us the passover, that we may eat it.
9 Suka tambaye shi suka ce, “Ina kake so mu je mu yi shirin?”
They asked him, Where shall we prepare it?
10 Ya amsa ya ce, “Sa’ad da kuka shiga cikin gari, za ku sadu da wani mutum yana ɗauke da tulun ruwa. Ku bi shi zuwa gidan da zai shiga.
He answered, When you enter the city, you will meet a man carrying a pitcher of water; follow him into the house which he shall enter,
11 Ku ce wa maigidan, Malam ya aike mu mu ce maka, ‘Ina ɗakin baƙi, inda ni da almajiraina za mu ci abincin Bikin Ƙetarewa?’
and say to the master of the house, The Teacher asks you, Where is the guest-chamber, where I may eat the passover with my disciples?
12 Zai nuna muku wani babban ɗakin sama a shirye. Nan za ku yi shirin.”
And he will show you a large upper room, furnished; make ready there.
13 Sai suka tafi, suka kuma iske kome kamar yadda Yesu ya faɗa musu. Sai suka shirya Bikin Ƙetarewa.
So they went, and having found everything as he had told them, prepared the passover.
14 Da lokaci ya yi, sai Yesu ya zauna tare da manzanninsa don cin abinci.
When the hour was come, he placed himself at table with the twelve Apostles,
15 Sai ya ce musu, “Na yi marmari ƙwarai don in ci wannan Bikin Ƙetarewa tare da ku, kafin in sha wahala.
and said to them, Much have I longed to eat this passover with you,
16 Ina dai gaya muku, ba zan ƙara cinsa ba, sai ya sami cika a mulkin Allah.”
that I will never partake of another, until it be accomplished in the kingdom of God.
17 Bayan ya ɗauki kwaf ruwan inabi, ya yi godiya, sai ya ce, “Ku karɓa, ku rarraba wa junanku.
Then, taking a cup, he gave thanks, and said, Take this, and share it amongst you;
18 Ina dai gaya muku, ba zan ƙara sha daga’ya’yan inabi ba, sai mulkin Allah ya zo.”
for I assure you, that I will not again drink of the product of the vine, until the Reign of God be come.
19 Sai ya ɗauki burodi ya yi godiya, ya kakkarya ya ba su, da cewa, “Wannan jikina ne, da aka bayar dominku. Ku riƙa yin haka don tunawa da ni.”
Then he took bread, and having given thanks, broke it, and gave it to them, saying, This is my body, which is given for you. Do this in commemoration of me.
20 Haka kuma, bayan abincin, ya ɗauki kwaf ruwan inabi ya ce, “Wannan kwaf ruwan inabi shi ne, na sabon alkawari cikin jinina, da aka zubar dominku.
He likewise gave the cup, after supper, saying, This cup is the new Institution in my blood, which is shed for you.
21 Amma hannun wanda zai ci amanata, yana cin abincin tare da ni.
Mark, however, that the hand of him who betrays me, is on the table with mine.
22 Ɗan Mutum zai mutu kamar yadda aka ƙaddara, amma kaiton mutumin da zai bashe shi.”
The Son of Man is going away, as has been determined: nevertheless, alas, for that man by whom he is betrayed!
23 Sai suka fara tambayar junansu, ko wane ne a cikinsu zai yi wannan.
Then they began to inquire among themselves, which of them it could be that would do this.
24 Gardama ta tashi a tsakaninsu, a kan ko wane ne a cikinsu ya fi girma.
There had been, also, a contention amongst them, which of them should be accounted the greatest.
25 Yesu ya ce musu, “Sarakunan Al’ummai suna nuna iko a kan mutanensu, kuma waɗanda suke nuna iko a kansu, suna kiran kansu Masu Taimakon mutane.
And he said to them, The king of the nations exercise dominion over them; and they who oppress them, are styled benefactors.
26 Amma ku, kada ku zama haka. A maimakon haka, sai dai wanda ya fi girma a cikinku, ya zama kamar wanda ya fi ƙanƙanta, wanda kuma ke mulki, ya zama kamar mai hidima.
But with you, it must be otherwise: nay, let the greatest amongst you be as the least; and him who governs, as he who serves.
27 Wane ne ya fi girma? Wanda yake zaune a tebur ne, ko kuma shi da yake yin hidima? Ashe, ba wanda yake zaune a tebur ba ne? Amma ga ni, ni mai yin hidima ne a cikinku.
For, which is greater, he who is at table, or he who serves? Is not he that is at table? Yet I am amongst you as one who serves.
28 Ku ne kuka tsaya tare da ni a gwaje-gwajen da na sha.
You are they who have continued with me in my trials.
29 Daidai kamar yadda Ubana ya ba ni mulki, haka ni ma nake ba ku.
And I grant to you, (forasmuch as my Father has granted me a kingdom, )
30 Saboda ku ci, ku sha a teburina a cikin mulkina. Kuma ku zauna a kan gadon sarauta, ku yi wa kabilu goma sha biyu na Isra’ila shari’a.
to eat, and to drink at my table, in my kingdom, and to sit on thrones, judging the twelve tribes of Israel.
31 “Siman, Siman, Shaiɗan ya nemi izini ya sheƙe kakamar alkama.
The Lord said, also, Simon, Simon, Satan has obtained permission to sift you as wheat;
32 Amma na yi maka addu’a, Siman, domin kada bangaskiyarka ta kāsa. Bayan ka juyo, ka ƙarfafa’yan’uwanka.”
but I have prayed for you, that your faith fail not; do you, therefore, when you have recovered yourself, confirm your brethren.
33 Amma ya amsa ya ce, “Ubangiji, ina a shirye in tafi tare da kai har kurkuku, ko mutuwa ma.”
He answered, Master, I am ready to accompany you, both to prison, and to death.
34 Yesu ya ce, “Ina gaya maka Bitrus, kafin zakara ya yi cara yau, za ka yi mūsun sanina sau uku.”
Jesus replied, I tell you, Peter, the cock shall not crow to-day, before you have thrice denied that you know me.
35 Sai Yesu ya tambaye, su ya ce, “Lokacin da na aike ku ba tare da jakar kuɗi, ko jaka, ko takalma ba, kun rasa wani abu?” Suka amsa, “Babu.”
Then he said to them, When I sent you without purse, and bag, and shoes, did you want anything?
36 Ya ce musu, “Amma yanzu, in kuna da jakar kuɗi, ko jaka, ku ɗauka. In kuma ba ku da takobi, ku sayar da rigarku, ku saya.
But now, said he, let him that has a purse, take it, and likewise his bag; and let him who has no sword, sell his mantle, and buy one;
37 A rubuce yake cewa, ‘An lissafta shi tare da masu zunubi.’ Ina kuwa gaya muku, dole wannan ya cika a kaina. I, abin da aka rubuta a kaina yana kusan cikawa.”
for I tell you that this scripture, "He was ranked among malefactors," is now to be accomplished in me: for the things relating to me must be fulfilled.
38 Almajiran suka ce, “Duba Ubangiji, ga takuba biyu.” Yesu ya ce, “Ya isa.”
They said, Master, here are two swords. He replied, It is enough.
39 Yesu ya fita zuwa Dutsen Zaitun kamar yadda ya saba, almajiransa kuma suka bi shi.
Then he went out, and repaired, as he was wont, to the Mount of Olives, and his disciples followed him.
40 Da ya kai wurin, sai ya ce musu, “Ku yi addu’a don kada ku fāɗi cikin jarraba.”
Being arrived there, he said to them, Pray that you may not yield to temptation.
41 Sai ya janye daga wurinsu, misalin nisan jifa, ya durƙusa a ƙasa ya yi addu’a,
Then, being withdrawn from them about a stone's cast; he kneeled down and prayed,
42 “Uba, in ka yarda, ka ɗauke mini wannan kwaf, amma ba nufina ba, sai dai naka.”
saying, Father, if thou wilt, take this cup away from me; nevertheless, not my will, but thine be done.
43 Wani mala’ika daga sama ya bayyana gare shi, ya ƙarfafa shi.
And there appeared to him an angel from heaven, strengthening him.
44 Domin tsananin azaba, sai ya ƙara himma cikin addu’a, zuffansa kuma na ɗigowa ƙasa kamar jini.
And being in an agony of grief, he prayed the more fervently, and his sweat fell like clotted blood to the ground.
45 Da ya tashi daga addu’a, ya koma inda almajiransa suke, sai ya iske su suna barci, daga gajiyar baƙin ciki.
Having risen from prayer, and returned to the disciples, he found them sleeping, oppressed with grief;
46 Ya tambaye su, “Don me kuke barci? Ku tashi ku yi addu’a, don kada ku fāɗi cikin jarraba.”
and said to them, Why do you sleep? Arise, and pray, lest the trial overcome you.
47 Yana cikin magana sai ga taro sun zo. Mutumin nan da ake kira Yahuda, ɗaya daga cikin Sha Biyun, shi ya bi da su. Sai ya matso kusa da Yesu don yă yi masa sumba.
Before he had done speaking, he saw a multitude; and he who was called Judas, one of the twelve, walked before them, and came up to Jesus, to kiss him.
48 Amma Yesu ya tambaye shi ya ce, “Yahuda, ashe, da sumba za ka bashe Ɗan Mutum?”
Jesus said to him, Judas, do you betray the Son of Man with a kiss?
49 Da masu bin Yesu suka ga abin da zai faru, sai suka ce, “Ubangiji, mu yi sara da takubanmu ne?”
Now, those who were with him, foreseeing what would happen, said to him, Master, shall we strike with the sword?
50 Sai ɗayansu ya kai sara ga bawan babban firist, ya sare kunnen damansa.
And one of them struck the servant of the high priest, and cut off his right ear.
51 Amma Yesu ya amsa ya ce, “Kada a ƙara yin wannan!” Sai ya taɓa kunnen mutumin da aka sara, ya warkar da shi.
Jesus said, Let this suffice; and touching his ear, he healed him.
52 Sai Yesu ya ce wa manyan firistoci, da ma’aikatan’yan gadin haikali, da dattawa, waɗanda suka zo don su kama shi, “Ina jagoran wani tawaye ne, da za ku zo da takuba da sanduna?
Then Jesus said to the chief priests, and the officers of the temple-guard, and the elders, who were come to apprehend him, Do you come with swords and clubs, as in pursuit of a robber?
53 Kullum ina tare da ku a filin haikali, amma ba ku kama ni ba. Amma wannan ne sa’a naku, lokacin da duhu yake mulki.”
While I was daily with you in the temple, you did not attempt to arrest me. But this is your hour, and the power of darkness.
54 Sai suka kama shi suka kai shi gidan babban firist. Bitrus ya bi su daga nesa.
Then they seized him, and led him away to the high priest's house. And Peter followed at a distance.
55 Amma da suka hura wuta a tsakiyar harabar gidan, kowa ya zauna, sai Bitrus ya zo ya zauna tare da su.
When they had kindled a fire in the middle of the court, and were sitting round it, Peter sat down among them.
56 Wata baiwa ta gan shi zaune kusa da wutar. Ta dube shi sosai sa’an nan, ta ce, “Ai, wannan mutum ma yana tare da shi.”
And a maid servant, having observed him sitting by the fire, and viewed him attentively, said, This man also was with him.
57 Amma ya yi mūsu ya ce, “Mace, ban san shi ba!”
But he disowned him, saying, Woman, I know him not.
58 Bayan ɗan lokaci kaɗan, wani dabam ya gan shi ya ce, “Kai ma ɗayansu ne.” Bitrus ya amsa ya ce, “Kai, ba na cikinsu!”
A little while after, another seeing him, said, You, also, are one of them. Peter answered, Man, I am not.
59 Bayan kamar sa’a ɗaya, sai wani mutum ya ce, “Ba shakka, mutumin nan ma yana tare da shi, don shi mutumin Galili ne.”
About an hour after, another averred the same thing, saying, This man was surely with him, for he is a Galilean.
60 Bitrus ya amsa ya ce, “Kai, ban ma san abin da kake magana a kai ba!” Yana cikin magana, sai zakara ya yi cara.
Peter answered, Man, I know nothing of this matter. And just as he spoke the word, a cock crew.
61 Ubangiji kuma ya juya ya kafa wa Bitrus ido. Sai Bitrus ya tuna da maganar da Ubangiji ya ce masa, “Kafin zakara ya yi cara yau, za ka yi mūsun sanina sau uku.”
Then the Lord, turning, looked upon Peter, and Peter called to mind the word which the Lord had said to him, Before the cock crow, you will disown me thrice.
62 Sai ya fita waje, ya yi kuka mai zafi.
And he went out and wept bitterly.
63 Mutanen da suke gadin Yesu suka fara masa ba’a da dūka.
Meantime, they who had Jesus in charge, mocked and beat him;
64 Suka rufe masa idanu suna tambaya cewa, “Ka yi annabci! Wa ya mare ka?”
and having blindfolded him, struck him on the face, and asked him, saying, Divine who it is that smote you.
65 Suka kuma yi masa waɗansu baƙaƙen maganganu masu yawa.
And many other abusive things they said against him.
66 Da gari ya waye, sai majalisar dattawa na mutane, da manyan firistoci, da malaman dokoki, suka taru wuri ɗaya. Sai aka kawo Yesu a gabansu.
As soon as it was day, the national senate, with the chief priests and scribes, were assembled, and having caused him to be brought into their council-chamber, said to him,
67 Suka ce, “Ka faɗa mana, ko kai ne Kiristi?” Yesu ya amsa ya ce, “Ko na gaya muku, ba za ku gaskata ni ba,
If you be the Messiah, tell us. He answered, If I tell you, you will not believe:
68 in kuma na yi muku tambaya ba za ku iya ba ni amsa ba.
and if put a question, you will neither answer me, nor acquit me.
69 Amma daga yanzu, Ɗan Mutum zai zauna a hannun dama na Allah Mai Iko.”
Hereafter the Son of Man shall be seated at the right hand of Almighty God.
70 Sai dukansu suka yi tambaya suka ce, “Wato, kai Ɗan Allah ke nan?” Ya amsa ya ce, “Kun faɗa daidai, ni ne.”
They all replied, You are, then, the Son of God? He answered, You say the truth.
71 Sai suka ce, “Wace shaida kuma muke nema? Ai, mun ji abin da ya ce da bakinsa.”
Then they cried, What further need have we of evidence? We have heard enough ourselves, from his own mouth.

< Luka 22 >