< Luka 22 >

1 Yanzu fa, Bikin Burodi Marar Yistin da ake kira Bikin Ƙetarewa ya yi kusa,
Now the feast of unleavened bread, which is called the Passover, was approaching.
2 manyan firistoci da malaman dokoki kuma suna neman yadda za su kashe Yesu a ɓoye, don suna tsoron mutane.
The chief priests and the scribes sought how they might put him to death, for they feared the people.
3 Shaiɗan kuwa ya shiga Yahuda, wanda ake kira Iskariyot, ɗaya daga cikin Sha Biyun.
Satan entered into Judas, who was also called Iscariot, who was counted with the twelve.
4 Sai Yahuda ya je ya tattauna da manyan firistoci, da ma’aikatan’yan gadin haikali, a kan yadda zai ba da Yesu a gare su.
He went away and talked with the chief priests and captains about how he might deliver him to them.
5 Suka kuwa yi murna, suka yarda su ba shi kuɗi.
They were glad, and agreed to give him money.
6 Ya ko yarda, ya fara neman zarafin da zai ba da Yesu a gare su, sa’ad da taro ba sa nan tare da shi.
He consented and sought an opportunity to deliver him to them in the absence of the multitude.
7 Sai ranar Bikin Burodi Marar Yisti ta kewayo, wato, ranar hadayar ɗan ragon kafara na Bikin Ƙetarewa.
The day of unleavened bread came, on which the Passover must be sacrificed.
8 Sai Yesu ya aiki Bitrus da Yohanna, ya ce musu, “Ku je ku yi shirye-shiryen Bikin Ƙetarewar da za mu ci.”
Jesus sent Peter and John, saying, “Go and prepare the Passover for us, that we may eat.”
9 Suka tambaye shi suka ce, “Ina kake so mu je mu yi shirin?”
They said to him, “Where do you want us to prepare?”
10 Ya amsa ya ce, “Sa’ad da kuka shiga cikin gari, za ku sadu da wani mutum yana ɗauke da tulun ruwa. Ku bi shi zuwa gidan da zai shiga.
He said to them, “Behold, when you have entered into the city, a man carrying a pitcher of water will meet you. Follow him into the house which he enters.
11 Ku ce wa maigidan, Malam ya aike mu mu ce maka, ‘Ina ɗakin baƙi, inda ni da almajiraina za mu ci abincin Bikin Ƙetarewa?’
Tell the master of the house, ‘The Teacher says to you, “Where is the guest room, where I may eat the Passover with my disciples?”’
12 Zai nuna muku wani babban ɗakin sama a shirye. Nan za ku yi shirin.”
He will show you a large, furnished upper room. Make preparations there.”
13 Sai suka tafi, suka kuma iske kome kamar yadda Yesu ya faɗa musu. Sai suka shirya Bikin Ƙetarewa.
They went, found things as Jesus had told them, and they prepared the Passover.
14 Da lokaci ya yi, sai Yesu ya zauna tare da manzanninsa don cin abinci.
When the hour had come, he sat down with the twelve apostles.
15 Sai ya ce musu, “Na yi marmari ƙwarai don in ci wannan Bikin Ƙetarewa tare da ku, kafin in sha wahala.
He said to them, “I have earnestly desired to eat this Passover with you before I suffer,
16 Ina dai gaya muku, ba zan ƙara cinsa ba, sai ya sami cika a mulkin Allah.”
for I tell you, I will no longer by any means eat of it until it is fulfilled in God’s Kingdom.”
17 Bayan ya ɗauki kwaf ruwan inabi, ya yi godiya, sai ya ce, “Ku karɓa, ku rarraba wa junanku.
He received a cup, and when he had given thanks, he said, “Take this and share it among yourselves,
18 Ina dai gaya muku, ba zan ƙara sha daga’ya’yan inabi ba, sai mulkin Allah ya zo.”
for I tell you, I will not drink at all again from the fruit of the vine, until God’s Kingdom comes.”
19 Sai ya ɗauki burodi ya yi godiya, ya kakkarya ya ba su, da cewa, “Wannan jikina ne, da aka bayar dominku. Ku riƙa yin haka don tunawa da ni.”
He took bread, and when he had given thanks, he broke and gave it to them, saying, “This is my body which is given for you. Do this in memory of me.”
20 Haka kuma, bayan abincin, ya ɗauki kwaf ruwan inabi ya ce, “Wannan kwaf ruwan inabi shi ne, na sabon alkawari cikin jinina, da aka zubar dominku.
Likewise, he took the cup after supper, saying, “This cup is the new covenant in my blood, which is poured out for you.
21 Amma hannun wanda zai ci amanata, yana cin abincin tare da ni.
But behold, the hand of him who betrays me is with me on the table.
22 Ɗan Mutum zai mutu kamar yadda aka ƙaddara, amma kaiton mutumin da zai bashe shi.”
The Son of Man indeed goes as it has been determined, but woe to that man through whom he is betrayed!”
23 Sai suka fara tambayar junansu, ko wane ne a cikinsu zai yi wannan.
They began to question among themselves which of them it was who would do this thing.
24 Gardama ta tashi a tsakaninsu, a kan ko wane ne a cikinsu ya fi girma.
A dispute also arose among them, which of them was considered to be greatest.
25 Yesu ya ce musu, “Sarakunan Al’ummai suna nuna iko a kan mutanensu, kuma waɗanda suke nuna iko a kansu, suna kiran kansu Masu Taimakon mutane.
He said to them, “The kings of the nations lord it over them, and those who have authority over them are called ‘benefactors.’
26 Amma ku, kada ku zama haka. A maimakon haka, sai dai wanda ya fi girma a cikinku, ya zama kamar wanda ya fi ƙanƙanta, wanda kuma ke mulki, ya zama kamar mai hidima.
But not so with you. Rather, the one who is greater among you, let him become as the younger, and one who is governing, as one who serves.
27 Wane ne ya fi girma? Wanda yake zaune a tebur ne, ko kuma shi da yake yin hidima? Ashe, ba wanda yake zaune a tebur ba ne? Amma ga ni, ni mai yin hidima ne a cikinku.
For who is greater, one who sits at the table, or one who serves? Is not it he who sits at the table? But I am among you as one who serves.
28 Ku ne kuka tsaya tare da ni a gwaje-gwajen da na sha.
“But you are those who have continued with me in my trials.
29 Daidai kamar yadda Ubana ya ba ni mulki, haka ni ma nake ba ku.
I confer on you a kingdom, even as my Father conferred on me,
30 Saboda ku ci, ku sha a teburina a cikin mulkina. Kuma ku zauna a kan gadon sarauta, ku yi wa kabilu goma sha biyu na Isra’ila shari’a.
that you may eat and drink at my table in my Kingdom. You will sit on thrones, judging the twelve tribes of Israel.”
31 “Siman, Siman, Shaiɗan ya nemi izini ya sheƙe kakamar alkama.
The Lord said, “Simon, Simon, behold, Satan asked to have all of you, that he might sift you as wheat,
32 Amma na yi maka addu’a, Siman, domin kada bangaskiyarka ta kāsa. Bayan ka juyo, ka ƙarfafa’yan’uwanka.”
but I prayed for you, that your faith would not fail. You, when once you have turned again, establish your brothers.”
33 Amma ya amsa ya ce, “Ubangiji, ina a shirye in tafi tare da kai har kurkuku, ko mutuwa ma.”
He said to him, “Lord, I am ready to go with you both to prison and to death!”
34 Yesu ya ce, “Ina gaya maka Bitrus, kafin zakara ya yi cara yau, za ka yi mūsun sanina sau uku.”
He said, “I tell you, Peter, the rooster will by no means crow today until you deny that you know me three times.”
35 Sai Yesu ya tambaye, su ya ce, “Lokacin da na aike ku ba tare da jakar kuɗi, ko jaka, ko takalma ba, kun rasa wani abu?” Suka amsa, “Babu.”
He said to them, “When I sent you out without purse, bag, and sandals, did you lack anything?” They said, “Nothing.”
36 Ya ce musu, “Amma yanzu, in kuna da jakar kuɗi, ko jaka, ku ɗauka. In kuma ba ku da takobi, ku sayar da rigarku, ku saya.
Then he said to them, “But now, whoever has a purse, let him take it, and likewise a bag. Whoever has none, let him sell his cloak, and buy a sword.
37 A rubuce yake cewa, ‘An lissafta shi tare da masu zunubi.’ Ina kuwa gaya muku, dole wannan ya cika a kaina. I, abin da aka rubuta a kaina yana kusan cikawa.”
For I tell you that this which is written must still be fulfilled in me: ‘He was counted with transgressors.’ For that which concerns me is being fulfilled.”
38 Almajiran suka ce, “Duba Ubangiji, ga takuba biyu.” Yesu ya ce, “Ya isa.”
They said, “Lord, behold, here are two swords.” He said to them, “That is enough.”
39 Yesu ya fita zuwa Dutsen Zaitun kamar yadda ya saba, almajiransa kuma suka bi shi.
He came out and went, as his custom was, to the Mount of Olives. His disciples also followed him.
40 Da ya kai wurin, sai ya ce musu, “Ku yi addu’a don kada ku fāɗi cikin jarraba.”
When he was at the place, he said to them, “Pray that you do not enter into temptation.”
41 Sai ya janye daga wurinsu, misalin nisan jifa, ya durƙusa a ƙasa ya yi addu’a,
He was withdrawn from them about a stone’s throw, and he knelt down and prayed,
42 “Uba, in ka yarda, ka ɗauke mini wannan kwaf, amma ba nufina ba, sai dai naka.”
saying, “Father, if you are willing, remove this cup from me. Nevertheless, not my will, but yours, be done.”
43 Wani mala’ika daga sama ya bayyana gare shi, ya ƙarfafa shi.
An angel from heaven appeared to him, strengthening him.
44 Domin tsananin azaba, sai ya ƙara himma cikin addu’a, zuffansa kuma na ɗigowa ƙasa kamar jini.
Being in agony, he prayed more earnestly. His sweat became like great drops of blood falling down on the ground.
45 Da ya tashi daga addu’a, ya koma inda almajiransa suke, sai ya iske su suna barci, daga gajiyar baƙin ciki.
When he rose up from his prayer, he came to the disciples and found them sleeping because of grief,
46 Ya tambaye su, “Don me kuke barci? Ku tashi ku yi addu’a, don kada ku fāɗi cikin jarraba.”
and said to them, “Why do you sleep? Rise and pray that you may not enter into temptation.”
47 Yana cikin magana sai ga taro sun zo. Mutumin nan da ake kira Yahuda, ɗaya daga cikin Sha Biyun, shi ya bi da su. Sai ya matso kusa da Yesu don yă yi masa sumba.
While he was still speaking, a crowd appeared. He who was called Judas, one of the twelve, was leading them. He came near to Jesus to kiss him.
48 Amma Yesu ya tambaye shi ya ce, “Yahuda, ashe, da sumba za ka bashe Ɗan Mutum?”
But Jesus said to him, “Judas, do you betray the Son of Man with a kiss?”
49 Da masu bin Yesu suka ga abin da zai faru, sai suka ce, “Ubangiji, mu yi sara da takubanmu ne?”
When those who were around him saw what was about to happen, they said to him, “Lord, shall we strike with the sword?”
50 Sai ɗayansu ya kai sara ga bawan babban firist, ya sare kunnen damansa.
A certain one of them struck the servant of the high priest, and cut off his right ear.
51 Amma Yesu ya amsa ya ce, “Kada a ƙara yin wannan!” Sai ya taɓa kunnen mutumin da aka sara, ya warkar da shi.
But Jesus answered, “Let me at least do this”—and he touched his ear and healed him.
52 Sai Yesu ya ce wa manyan firistoci, da ma’aikatan’yan gadin haikali, da dattawa, waɗanda suka zo don su kama shi, “Ina jagoran wani tawaye ne, da za ku zo da takuba da sanduna?
Jesus said to the chief priests, captains of the temple, and elders, who had come against him, “Have you come out as against a robber, with swords and clubs?
53 Kullum ina tare da ku a filin haikali, amma ba ku kama ni ba. Amma wannan ne sa’a naku, lokacin da duhu yake mulki.”
When I was with you in the temple daily, you did not stretch out your hands against me. But this is your hour, and the power of darkness.”
54 Sai suka kama shi suka kai shi gidan babban firist. Bitrus ya bi su daga nesa.
They seized him and led him away, and brought him into the high priest’s house. But Peter followed from a distance.
55 Amma da suka hura wuta a tsakiyar harabar gidan, kowa ya zauna, sai Bitrus ya zo ya zauna tare da su.
When they had kindled a fire in the middle of the courtyard and had sat down together, Peter sat among them.
56 Wata baiwa ta gan shi zaune kusa da wutar. Ta dube shi sosai sa’an nan, ta ce, “Ai, wannan mutum ma yana tare da shi.”
A certain servant girl saw him as he sat in the light, and looking intently at him, said, “This man also was with him.”
57 Amma ya yi mūsu ya ce, “Mace, ban san shi ba!”
He denied Jesus, saying, “Woman, I do not know him.”
58 Bayan ɗan lokaci kaɗan, wani dabam ya gan shi ya ce, “Kai ma ɗayansu ne.” Bitrus ya amsa ya ce, “Kai, ba na cikinsu!”
After a little while someone else saw him and said, “You also are one of them!” But Peter answered, “Man, I am not!”
59 Bayan kamar sa’a ɗaya, sai wani mutum ya ce, “Ba shakka, mutumin nan ma yana tare da shi, don shi mutumin Galili ne.”
After about one hour passed, another confidently affirmed, saying, “Truly this man also was with him, for he is a Galilean!”
60 Bitrus ya amsa ya ce, “Kai, ban ma san abin da kake magana a kai ba!” Yana cikin magana, sai zakara ya yi cara.
But Peter said, “Man, I do not know what you are talking about!” Immediately, while he was still speaking, a rooster crowed.
61 Ubangiji kuma ya juya ya kafa wa Bitrus ido. Sai Bitrus ya tuna da maganar da Ubangiji ya ce masa, “Kafin zakara ya yi cara yau, za ka yi mūsun sanina sau uku.”
The Lord turned and looked at Peter. Then Peter remembered the Lord’s word, how he said to him, “Before the rooster crows you will deny me three times.”
62 Sai ya fita waje, ya yi kuka mai zafi.
He went out, and wept bitterly.
63 Mutanen da suke gadin Yesu suka fara masa ba’a da dūka.
The men who held Jesus mocked him and beat him.
64 Suka rufe masa idanu suna tambaya cewa, “Ka yi annabci! Wa ya mare ka?”
Having blindfolded him, they struck him on the face and asked him, “Prophesy! Who is the one who struck you?”
65 Suka kuma yi masa waɗansu baƙaƙen maganganu masu yawa.
They spoke many other things against him, insulting him.
66 Da gari ya waye, sai majalisar dattawa na mutane, da manyan firistoci, da malaman dokoki, suka taru wuri ɗaya. Sai aka kawo Yesu a gabansu.
As soon as it was day, the assembly of the elders of the people were gathered together, both chief priests and scribes, and they led him away into their council, saying,
67 Suka ce, “Ka faɗa mana, ko kai ne Kiristi?” Yesu ya amsa ya ce, “Ko na gaya muku, ba za ku gaskata ni ba,
“If you are the Christ, tell us.” But he said to them, “If I tell you, you will not believe,
68 in kuma na yi muku tambaya ba za ku iya ba ni amsa ba.
and if I ask, you will in no way answer me or let me go.
69 Amma daga yanzu, Ɗan Mutum zai zauna a hannun dama na Allah Mai Iko.”
From now on, the Son of Man will be seated at the right hand of the power of God.”
70 Sai dukansu suka yi tambaya suka ce, “Wato, kai Ɗan Allah ke nan?” Ya amsa ya ce, “Kun faɗa daidai, ni ne.”
They all said, “Are you then the Son of God?” He said to them, “You say it, because I am.”
71 Sai suka ce, “Wace shaida kuma muke nema? Ai, mun ji abin da ya ce da bakinsa.”
They said, “Why do we need any more witness? For we ourselves have heard from his own mouth!”

< Luka 22 >