< Luka 22 >

1 Yanzu fa, Bikin Burodi Marar Yistin da ake kira Bikin Ƙetarewa ya yi kusa,
Men de usyrede Brøds Højtid, som kaldes Påske, nærmede sig.
2 manyan firistoci da malaman dokoki kuma suna neman yadda za su kashe Yesu a ɓoye, don suna tsoron mutane.
Og Ypperstepræsterne og de skriftkloge søgte, hvorledes de kunde slå ham ihjel; thi de frygtede for Folket.
3 Shaiɗan kuwa ya shiga Yahuda, wanda ake kira Iskariyot, ɗaya daga cikin Sha Biyun.
Men Satan gik ind i Judas, som kaldes Iskariot og var en af de tolv.
4 Sai Yahuda ya je ya tattauna da manyan firistoci, da ma’aikatan’yan gadin haikali, a kan yadda zai ba da Yesu a gare su.
Og han gik hen og talte med Ypperstepræsterne og Høvedsmændene om, hvorledes han vilde forråde ham til dem.
5 Suka kuwa yi murna, suka yarda su ba shi kuɗi.
Og de bleve glade og lovede at give ham Penge.
6 Ya ko yarda, ya fara neman zarafin da zai ba da Yesu a gare su, sa’ad da taro ba sa nan tare da shi.
Og han tilsagde det; og han søgte Lejlighed til at forråde ham til dem uden Opløb.
7 Sai ranar Bikin Burodi Marar Yisti ta kewayo, wato, ranar hadayar ɗan ragon kafara na Bikin Ƙetarewa.
Men de usyrede Brøds Dag kom, på hvilken man skulde slagte Påskelammet.
8 Sai Yesu ya aiki Bitrus da Yohanna, ya ce musu, “Ku je ku yi shirye-shiryen Bikin Ƙetarewar da za mu ci.”
Og han udsendte Peter og Johannes og sagde: "Går hen og bereder os Påskelammet, at vi kunne spise det."
9 Suka tambaye shi suka ce, “Ina kake so mu je mu yi shirin?”
Men de sagde til ham: "Hvor vil du, at vi skulle berede det?"
10 Ya amsa ya ce, “Sa’ad da kuka shiga cikin gari, za ku sadu da wani mutum yana ɗauke da tulun ruwa. Ku bi shi zuwa gidan da zai shiga.
Men han sagde til dem: "Se, når I ere komne ind i Staden, skal der møde eder en Mand, som bærer en Vandkrukke; følger ham til Huset, hvor han går ind,
11 Ku ce wa maigidan, Malam ya aike mu mu ce maka, ‘Ina ɗakin baƙi, inda ni da almajiraina za mu ci abincin Bikin Ƙetarewa?’
og I skulle sige til Husbonden i Huset: Mesteren siger: Hvor er det Herberge, hvor jeg kan spise Påskelammet med mine Disciple?
12 Zai nuna muku wani babban ɗakin sama a shirye. Nan za ku yi shirin.”
Og han skal vise eder en stor Sal opdækket; der skulle I berede det."
13 Sai suka tafi, suka kuma iske kome kamar yadda Yesu ya faɗa musu. Sai suka shirya Bikin Ƙetarewa.
Og de gik hen og fandt det således, som han havde sagt dem; og de beredte Påskelammet.
14 Da lokaci ya yi, sai Yesu ya zauna tare da manzanninsa don cin abinci.
Og da Timen kom, satte han sig til Bords, og Apostlene med ham.
15 Sai ya ce musu, “Na yi marmari ƙwarai don in ci wannan Bikin Ƙetarewa tare da ku, kafin in sha wahala.
Og han sagde til dem: "Jeg har hjerteligt længtes efter at spise dette Påskelam med eder, førend jeg lider.
16 Ina dai gaya muku, ba zan ƙara cinsa ba, sai ya sami cika a mulkin Allah.”
Thi jeg siger eder, at jeg skal ingen Sinde mere spise det, førend det bliver fuldkommet i Guds Rige."
17 Bayan ya ɗauki kwaf ruwan inabi, ya yi godiya, sai ya ce, “Ku karɓa, ku rarraba wa junanku.
Og han tog en Kalk, takkede og sagde: "Tager dette, og deler det imellem eder!
18 Ina dai gaya muku, ba zan ƙara sha daga’ya’yan inabi ba, sai mulkin Allah ya zo.”
Thi jeg siger eder, at fra nu af skal jeg ikke drikke af Vintræets Frugt, førend Guds Rige kommer."
19 Sai ya ɗauki burodi ya yi godiya, ya kakkarya ya ba su, da cewa, “Wannan jikina ne, da aka bayar dominku. Ku riƙa yin haka don tunawa da ni.”
Og han tog Brød, takkede og brød det og gav dem det og sagde: "Dette er mit Legeme, det, som gives for eder; gører dette til min Ihukommelse!"
20 Haka kuma, bayan abincin, ya ɗauki kwaf ruwan inabi ya ce, “Wannan kwaf ruwan inabi shi ne, na sabon alkawari cikin jinina, da aka zubar dominku.
Ligeså tog han også Kalken efter Aftensmåltidet og sagde: "Denne Kalk er den nye Pagt i mit Blod, det, som udgydes for eder.
21 Amma hannun wanda zai ci amanata, yana cin abincin tare da ni.
Men se, hans Hånd, som forråder mig, er her på Bordet hos mig.
22 Ɗan Mutum zai mutu kamar yadda aka ƙaddara, amma kaiton mutumin da zai bashe shi.”
Thi Menneskesønnen går bort, som det er beskikket; dog ve det Menneske, ved hvem han bliver forrådt!"
23 Sai suka fara tambayar junansu, ko wane ne a cikinsu zai yi wannan.
Og de begyndte at spørge hverandre indbyrdes om, hvem af dem det dog kunde være, som skulde gøre dette.
24 Gardama ta tashi a tsakaninsu, a kan ko wane ne a cikinsu ya fi girma.
Men der opstod også en Trætte iblandt dem om, hvem at dem der måtte synes at være den største.
25 Yesu ya ce musu, “Sarakunan Al’ummai suna nuna iko a kan mutanensu, kuma waɗanda suke nuna iko a kansu, suna kiran kansu Masu Taimakon mutane.
Men han sagde til dem: "Folkenes Konger herske over dem, og de, som bruge Myndighed over dem, kaldes deres Velgørere.
26 Amma ku, kada ku zama haka. A maimakon haka, sai dai wanda ya fi girma a cikinku, ya zama kamar wanda ya fi ƙanƙanta, wanda kuma ke mulki, ya zama kamar mai hidima.
I derimod ikke således; men den ældste iblandt eder blive som den yngste, og Føreren som den, der tjener.
27 Wane ne ya fi girma? Wanda yake zaune a tebur ne, ko kuma shi da yake yin hidima? Ashe, ba wanda yake zaune a tebur ba ne? Amma ga ni, ni mai yin hidima ne a cikinku.
Thi hvem er størst: den, som sidder til Bords? eller den, som tjener? Mon ikke den, som sidder til Bords? Men jeg er iblandt eder som den, der tjener.
28 Ku ne kuka tsaya tare da ni a gwaje-gwajen da na sha.
Men I ere de, som have holdt ud med mig i mine Fristelser.
29 Daidai kamar yadda Ubana ya ba ni mulki, haka ni ma nake ba ku.
Og ligesom min Fader har tildelt mig Kongedømme, tildeler jeg eder
30 Saboda ku ci, ku sha a teburina a cikin mulkina. Kuma ku zauna a kan gadon sarauta, ku yi wa kabilu goma sha biyu na Isra’ila shari’a.
at skulle spise og drikke ved mit Bord i mit Rige og sidde på Troner og dømme Israels tolv Stammer."
31 “Siman, Siman, Shaiɗan ya nemi izini ya sheƙe kakamar alkama.
Men Herren sagde: "Simon, Simon! se, Satan begærede eder for at sigte eder som Hvede.
32 Amma na yi maka addu’a, Siman, domin kada bangaskiyarka ta kāsa. Bayan ka juyo, ka ƙarfafa’yan’uwanka.”
Men jeg bad for dig, at din Tro ikke skal svigte; og når du engang omvender dig, da styrk dine Brødre!"
33 Amma ya amsa ya ce, “Ubangiji, ina a shirye in tafi tare da kai har kurkuku, ko mutuwa ma.”
Men han sagde til ham: "Herre! jeg er rede til at gå med dig både i Fængsel og i Døden."
34 Yesu ya ce, “Ina gaya maka Bitrus, kafin zakara ya yi cara yau, za ka yi mūsun sanina sau uku.”
Men han sagde: "Peter! jeg siger dig: Hanen skal ikke gale i Dag, førend du tre Gange har nægtet, at du kender mig."
35 Sai Yesu ya tambaye, su ya ce, “Lokacin da na aike ku ba tare da jakar kuɗi, ko jaka, ko takalma ba, kun rasa wani abu?” Suka amsa, “Babu.”
Og han sagde til dem: "Da jeg udsendte eder uden Pung og Taske og Sko, manglede I da noget?" Og de sagde: "Intet."
36 Ya ce musu, “Amma yanzu, in kuna da jakar kuɗi, ko jaka, ku ɗauka. In kuma ba ku da takobi, ku sayar da rigarku, ku saya.
Men han sagde til dem: "Men nu, den, som har en Pung, tage den med, ligeså også en Taske; og den, som ikke har noget Sværd, sælge sin Kappe og købe et!
37 A rubuce yake cewa, ‘An lissafta shi tare da masu zunubi.’ Ina kuwa gaya muku, dole wannan ya cika a kaina. I, abin da aka rubuta a kaina yana kusan cikawa.”
Thi jeg siger eder: Det, som er skrevet, bør opfyldes på mig, dette: "Og han blev regnet iblandt Overtrædere;" thi også med mig har det en Ende."
38 Almajiran suka ce, “Duba Ubangiji, ga takuba biyu.” Yesu ya ce, “Ya isa.”
Men de sagde: "Herre! se, her er to Sværd." Men han sagde til dem: "Det er nok."
39 Yesu ya fita zuwa Dutsen Zaitun kamar yadda ya saba, almajiransa kuma suka bi shi.
Og han gik ud og gik efter sin Sædvane til Oliebjerget; men også Disciplene fulgte ham.
40 Da ya kai wurin, sai ya ce musu, “Ku yi addu’a don kada ku fāɗi cikin jarraba.”
Men da han kom til Stedet, sagde han til dem: "Beder om ikke at falde i Fristelse."
41 Sai ya janye daga wurinsu, misalin nisan jifa, ya durƙusa a ƙasa ya yi addu’a,
Og han rev sig løs fra dem, så meget som et Stenkast, og faldt på Knæ, bad og sagde:
42 “Uba, in ka yarda, ka ɗauke mini wannan kwaf, amma ba nufina ba, sai dai naka.”
"Fader, vilde du dog tage denne Kalk fra mig! dog ske ikke min Villie, men din!"
43 Wani mala’ika daga sama ya bayyana gare shi, ya ƙarfafa shi.
Men en Engel fra Himmelen viste sig for ham og styrkede ham.
44 Domin tsananin azaba, sai ya ƙara himma cikin addu’a, zuffansa kuma na ɗigowa ƙasa kamar jini.
Og da han var i Dødsangst, bad han heftigere; men hans Sved blev som Blodsdråber, der faldt ned på Jorden.
45 Da ya tashi daga addu’a, ya koma inda almajiransa suke, sai ya iske su suna barci, daga gajiyar baƙin ciki.
Og da han stod op fra Bønnen og kom til Disciplene, fandt han dem sovende af Bedrøvelse.
46 Ya tambaye su, “Don me kuke barci? Ku tashi ku yi addu’a, don kada ku fāɗi cikin jarraba.”
Og han sagde til dem: "Hvorfor sove I? Står op og beder, for at I ikke skulle falde i Fristelse."
47 Yana cikin magana sai ga taro sun zo. Mutumin nan da ake kira Yahuda, ɗaya daga cikin Sha Biyun, shi ya bi da su. Sai ya matso kusa da Yesu don yă yi masa sumba.
Medens han endnu talte, se, da kom der en Skare; og han, som hed Judas, en af de tolv, gik foran dem og nærmede sig til Jesus for at kysse ham.
48 Amma Yesu ya tambaye shi ya ce, “Yahuda, ashe, da sumba za ka bashe Ɗan Mutum?”
Men Jesus sagde til ham: "Judas! forråder du Menneskesønnen med et Kys?"
49 Da masu bin Yesu suka ga abin da zai faru, sai suka ce, “Ubangiji, mu yi sara da takubanmu ne?”
Men da de, som vare omkring ham, så, hvad der vilde ske, sagde de: "Herre! skulle vi slå til med Sværd?"
50 Sai ɗayansu ya kai sara ga bawan babban firist, ya sare kunnen damansa.
Og en af dem slog Ypperstepræstens Tjener og afhuggede hans højre Øre.
51 Amma Yesu ya amsa ya ce, “Kada a ƙara yin wannan!” Sai ya taɓa kunnen mutumin da aka sara, ya warkar da shi.
Men Jesus tog til Orde og sagde: "Lad dem gøre også dette!" Og han rørte ved hans Øre og lægte ham.
52 Sai Yesu ya ce wa manyan firistoci, da ma’aikatan’yan gadin haikali, da dattawa, waɗanda suka zo don su kama shi, “Ina jagoran wani tawaye ne, da za ku zo da takuba da sanduna?
Men Jesus sagde til Ypperstepræsterne og Høvedsmændene for Helligdommen og de ældste, som vare komne til ham: "I ere gåede ud som imod en Røver med Sværd og Knipler.
53 Kullum ina tare da ku a filin haikali, amma ba ku kama ni ba. Amma wannan ne sa’a naku, lokacin da duhu yake mulki.”
Da jeg var daglig hos eder i Helligdommen, udrakte I ikke Hænderne imod mig; men dette er eders Time og Mørkets Magt."
54 Sai suka kama shi suka kai shi gidan babban firist. Bitrus ya bi su daga nesa.
Og de grebe ham og førte ham bort og bragte ham ind i Ypperstepræstens Hus; men Peter fulgte efter i Frastand.
55 Amma da suka hura wuta a tsakiyar harabar gidan, kowa ya zauna, sai Bitrus ya zo ya zauna tare da su.
Og de tændte en Ild midt i Gården og satte sig sammen, og Peter sad midt iblandt dem.
56 Wata baiwa ta gan shi zaune kusa da wutar. Ta dube shi sosai sa’an nan, ta ce, “Ai, wannan mutum ma yana tare da shi.”
Men en Pige så ham sidde i Lysskæret og stirrede på ham og sagde: "Også denne var med ham."
57 Amma ya yi mūsu ya ce, “Mace, ban san shi ba!”
Men han fornægtede ham og sagde: "Jeg kender ham ikke. Kvinde!"
58 Bayan ɗan lokaci kaɗan, wani dabam ya gan shi ya ce, “Kai ma ɗayansu ne.” Bitrus ya amsa ya ce, “Kai, ba na cikinsu!”
Og lidt derefter så en anden ham og sagde: "Også du er en af dem." Men Peter sagde: "Menneske! det er jeg ikke."
59 Bayan kamar sa’a ɗaya, sai wani mutum ya ce, “Ba shakka, mutumin nan ma yana tare da shi, don shi mutumin Galili ne.”
Og omtrent en Time derefter forsikrede en anden det og sagde: "I Sandhed, også denne var med ham; han er jo også en Galilæer."
60 Bitrus ya amsa ya ce, “Kai, ban ma san abin da kake magana a kai ba!” Yana cikin magana, sai zakara ya yi cara.
Men Peter sagde: "Menneske! jeg forstår ikke, hvad du siger." Og straks, medens han endnu talte. galede Hanen.
61 Ubangiji kuma ya juya ya kafa wa Bitrus ido. Sai Bitrus ya tuna da maganar da Ubangiji ya ce masa, “Kafin zakara ya yi cara yau, za ka yi mūsun sanina sau uku.”
Og Herren vendte sig og så på Peter; og Peter kom Herrens Ord i Hu, hvorledes han havde sagt til ham: "Førend Hanen galer i Dag, skal du fornægte mig tre Gange."
62 Sai ya fita waje, ya yi kuka mai zafi.
Og han gik udenfor og græd bitterligt.
63 Mutanen da suke gadin Yesu suka fara masa ba’a da dūka.
Og de Mænd, som holdt Jesus, spottede ham og sloge ham;
64 Suka rufe masa idanu suna tambaya cewa, “Ka yi annabci! Wa ya mare ka?”
og de kastede et Klæde over ham og spurgte ham og sagde: "Profeter! hvem var det, som slog dig?"
65 Suka kuma yi masa waɗansu baƙaƙen maganganu masu yawa.
Og mange andre Ting sagde de spottende til ham.
66 Da gari ya waye, sai majalisar dattawa na mutane, da manyan firistoci, da malaman dokoki, suka taru wuri ɗaya. Sai aka kawo Yesu a gabansu.
Og da det blev Dag, samlede Folkets Ældste sig og Ypperstepræsterne og de skriftkloge, og de førte ham hen for deres Råd
67 Suka ce, “Ka faɗa mana, ko kai ne Kiristi?” Yesu ya amsa ya ce, “Ko na gaya muku, ba za ku gaskata ni ba,
og sagde: "Er du Kristus, da sig os det!" Men han sagde til dem: "Siger jeg eder det, tro I det ikke.
68 in kuma na yi muku tambaya ba za ku iya ba ni amsa ba.
Og om jeg spørger, svare I mig ikke, ej heller løslade I mig.
69 Amma daga yanzu, Ɗan Mutum zai zauna a hannun dama na Allah Mai Iko.”
Men fra nu af skal Menneskesønnen sidde ved Guds Krafts højre Hånd."
70 Sai dukansu suka yi tambaya suka ce, “Wato, kai Ɗan Allah ke nan?” Ya amsa ya ce, “Kun faɗa daidai, ni ne.”
Men de sagde alle: "Er du da Guds Søn?" Og han sagde til dem: "I sige det; jeg er det."
71 Sai suka ce, “Wace shaida kuma muke nema? Ai, mun ji abin da ya ce da bakinsa.”
Men de sagde: "Hvad have vi længere Vidnesbyrd nødig? vi have jo selv hørt det af hans Mund!"

< Luka 22 >