< Luka 21 >

1 Da Yesu ya ɗaga ido, sai ya ga waɗansu masu arziki suna sa baikonsu a ma’ajin haikalin.
[Ісус] дивився, як багатії клали свої дари в скарбницю [Храму].
2 Ya kuma ga wata gwauruwa matalauciya, ta saka anini biyu.
Побачив Він також і бідну вдову, яка поклала туди дві лепти.
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina faɗa muku, wacce nan gwauruwa matalauciya ta sa fiye da dukan sauran.
І промовив: «Істинно кажу вам: ця бідна вдова поклала більше, ніж усі інші,
4 Dukan mutanen nan sun ba da baikonsu daga cikin arzikinsu ne, amma ita daga cikin talaucinta, ta saka duk abin da take da shi na rayuwa.”
бо всі клали зі свого достатку, а вона зі своєї бідності поклала все, що в неї було на прожиток».
5 Waɗansu daga cikin almajiransa, suka fara magana a kan yadda aka yi wa haikalin ado da duwatsu masu kyau, da kuma kyautai da aka keɓe wa Allah. Amma Yesu ya ce,
Коли присутні заговорили про Храм, що він прикрашений дорогоцінним камінням та дарами, Він сказав:
6 “Wannan abin da kuke kallo a nan, lokaci yana zuwa da ba za a bar wani dutse a kan wani dutse ba. Kowannensu, za a rushe shi.”
―Прийдуть дні, коли з того, що бачите, не залишиться каменя на камені, який не був би зруйнований.
7 Suka tambaye shi suka ce, “Malam, yaushe waɗannan za su faru? Kuma wace alama za tă nuna cewa suna dab da faruwa?”
І запитали Його: ―Учителю, коли це станеться? І яка ознака того, що це має статися?
8 Ya amsa ya ce, “Ku lura, kada ku kuma a ruɗe ku. Gama da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ai, ni ne shi,’ da kuma, ‘Lokaci ya yi kusa.’ Kada ku bi su.
Він відповів: ―Дивіться, щоб ніхто не ввів вас в оману, бо багато хто прийде в ім’я Моє й казатиме: «Це Я!» і «Час наблизився!» Не йдіть за ними!
9 Sa’ad da kuka ji labarin yaƙe-yaƙe, da juye juyen mulki, kada ku tsorota. Dole ne waɗannan abubuwa su fara faruwa, amma ƙarshen ba zai zo nan da nan ba.”
Коли почуєте про війни та повстання, не лякайтеся: спочатку все це має статися, але кінець буде не відразу.
10 Sai ya ce musu, “Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki zai tasar wa mulki.
Тоді сказав їм: ―Повстане народ проти народу й царство проти царства.
11 Za a yi manyan girgizar ƙasa, da yunwa, da annoba a wurare dabam-dabam, da kuma abubuwa masu bantsoro, da manyan alamu daga sama.
Будуть сильні землетруси в різних місцях, голод та чума. Будуть відбуватися страшні події та великі знамення на небі.
12 “Amma kafin duk abubuwa nan, za a kama ku a tsananta muku. Za a kai ku majami’u, da kurkuku. Za a kuma kai ku gaban sarakuna da gwamnoni, kuma dukan waɗannan saboda sunana.
Але перед тим, як все це відбудеться, накладуть на вас руки та переслідуватимуть вас. Видаватимуть вас у синагоги та в’язниці, поведуть вас до царів та правителів через ім’я Моє.
13 Wannan zai sa ku zama shaidu a gare su.
І це дасть вам можливість свідчити.
14 Amma ku yi ƙuduri, wato, ku shirya zuciyarku, a kan ba za ku damu ba kafin lokacin, game da yadda za ku kāre kanku.
Отже, покладіть собі в серця не турбуватись завчасно, що говорити на свій захист,
15 Gama zan ba ku kalmomi, da hikima waɗanda ba ko ɗaya daga cikin maƙiyanku, za su iya tsayayya da ku, ko su ƙaryata.
бо Я дам вам слова й таку мудрість, якій не зможуть противитися й суперечити всі ваші противники.
16 Har iyayenku, da’yan’uwanku maza, da danginku, da abokanku ma, duk za su bashe ku, su kuma kashe waɗansunku.
Вас будуть зраджувати навіть ваші батьки, брати, родичі та друзі. Декого з вас вбиватимуть.
17 Duk mutane za su ƙi ku saboda ni.
І всі будуть ненавидіти вас через Моє ім’я.
18 Amma ko gashi ɗaya na kanku, ba zai hallaka ba.
Але жодна волосина з вашої голови не пропаде.
19 Ta wurin tsayawa da ƙarfi, za ku sami rai.
Терпінням вашим ви здобудете душі ваші.
20 “In kuka ga mayaƙa sun kewaye Urushalima, za ku sani rushewarta ya yi kusa.
Коли ж побачите Єрусалим, оточений військами, тоді знайте, що його спустошення наблизилось.
21 A lokacin nan, bari waɗanda suke Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu. Bari waɗanda suke cikin birnin kuma su fita, bari kuma waɗanda suke ƙauye kada su shiga birnin.
Тоді ті, що в Юдеї, нехай тікають у гори; ті, що в Єрусалимі, нехай виходять із нього; а ті, що будуть на полях, нехай до нього не входять.
22 Gama wannan shi ne lokacin hukunci, saboda a cika duk abin da aka rubuta.
Бо це буде час помсти, коли все написане здійсниться.
23 Zai zama abin kaito ga mata masu ciki, da mata masu renon’ya’ya, a waɗancan kwanakin! Za a yi baƙin ciki mai tsanani a ƙasar, da kuma fushi mai tsanani a kan mutanen nan.
Горе вагітним і тим, що будуть годувати грудьми в ті дні, бо велике лихо буде на землі та гнів на цьому народі.
24 Za a kashe su da takobi, a kuma ɗauke su’yan kurkuku, zuwa dukan al’ummai. Al’ummai za su tattaka Urushalima, har sai lokacin Al’ummai ya cika.
[Люди] будуть гинути від меча, їх заберуть у полон поміж усі народи. Єрусалим топтатимуть язичники, аж доки час язичників не закінчиться.
25 “Za a yi alamu a cikin rana, da cikin wata, da cikin taurari. A duniya, al’ummai za su yi baƙin ciki, su kuma rikice don tsoro, saboda ruri da kuma tafasar teku.
І будуть знамення на сонці, місяці та зірках, а на землі буде жах між народами та розгубленість від ревіння морських хвиль.
26 Mutane za su suma don tsoro, za su kuma yi fargaba, a kan abin da yake zuwa a bisan duniya, gama za a girgiza duniyar taurarin sararin sama.
Люди вмиратимуть від страху в очікуванні подій, що насуваються на людство, бо сили небесні захитаються.
27 A lokacin ne za su ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin girgije, da iko, da ɗaukaka mai girma.
І тоді [люди] побачать Сина Людського, Який приходить на хмарі з великою силою та славою.
28 Sa’ad da waɗannan abubuwa sun fara faruwa, ku tashi tsaye, ku ɗaga kawunanku, domin fansarku yana matsowa kusa.”
Коли ці речі почнуть збуватися, ви встаньте та підійміть ваші голови, бо наближається визволення ваше.
29 Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Ku dubi itacen ɓaure da dukan itatuwa.
Потім сказав їм цю притчу: ―Дивіться на смоковницю та на всі дерева:
30 A duk lokacin da sun fara fitar da ganye, za ku gani da kanku, ku san cewa, damina ta yi kusa.
коли на них з’являється листя, знаєте, що літо вже близько.
31 Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku sani mulkin Allah ya yi kusa.
Так і ви, коли побачите, що це збувається, знайте: Царство Боже вже близько.
32 “Gaskiya nake gaya muku, ba shakka, wannan zamani ba zai shuɗe ba, sai dukan waɗannan abubuwa sun cika.
Істинно кажу вам: не мине цей рід, поки все це не станеться.
33 Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.
Небо та земля проминуть, але слова Мої не проминуть.
34 “Ku lura fa don kada son jin daɗi na banza, da shaye-shaye, da damuwa na rayuwa su rinjayi zuciyarku, har ranar ta auko muku ba tsammani kamar tarko.
Будьте уважні, щоб ваші серця не обтяжували ненажерство, п’янство та життєві турботи і щоб день той не застав вас зненацька,
35 Gama za tă zo a kan kowa da yake kan dukan duniya.
як пастка. Бо він прийде несподівано для всіх, хто живе на землі.
36 Ku yi tsaro kullum, ku yi addu’a don ku iya kuɓuta daga dukan waɗannan abubuwa da suke kusan faruwa, don ku iya tsayawa a gaban Ɗan Mutum.”
Завжди пильнуйте та моліться, щоб мати змогу уникнути всього того, що має відбутися, і стати перед Сином Людським.
37 Kowace rana, Yesu yakan je haikalin ya yi koyarwa, da kowace yamma kuma, ya je ya kwana a kan tudun da ake kira Dutsen Zaitun.
Кожен день [Ісус] навчав у Храмі, а вночі виходив та перебував на горі, що зветься Оливною.
38 Da sassafe kuma, dukan mutanen suka zo haikalin, don su saurare shi.
Увесь народ збирався зранку в Храмі, аби слухати Його.

< Luka 21 >