< Luka 21 >
1 Da Yesu ya ɗaga ido, sai ya ga waɗansu masu arziki suna sa baikonsu a ma’ajin haikalin.
Och han såg till, aktandes på huru de rike lade sina gåfvor uti offerkistona.
2 Ya kuma ga wata gwauruwa matalauciya, ta saka anini biyu.
Så fick han ock se ena fattiga enko, som lade der två skärfvar in.
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina faɗa muku, wacce nan gwauruwa matalauciya ta sa fiye da dukan sauran.
Och han sade: Sannerliga säger jag eder: Denna fattiga enkan lade mer in, än alle de andre;
4 Dukan mutanen nan sun ba da baikonsu daga cikin arzikinsu ne, amma ita daga cikin talaucinta, ta saka duk abin da take da shi na rayuwa.”
Ty de hafva alle inlagt, till Guds offer, af det dem till öfverlopps är; men hon hafver, af sin fattigdom, inlagt allt det hon ägde.
5 Waɗansu daga cikin almajiransa, suka fara magana a kan yadda aka yi wa haikalin ado da duwatsu masu kyau, da kuma kyautai da aka keɓe wa Allah. Amma Yesu ya ce,
Och då somlige sade om templet, att det var prydt med härliga stenar och klenodier, sade han:
6 “Wannan abin da kuke kallo a nan, lokaci yana zuwa da ba za a bar wani dutse a kan wani dutse ba. Kowannensu, za a rushe shi.”
De dagar varda kommande, att utaf allt, det I sen, skall icke låtas sten uppå sten, den icke skall afbruten varda.
7 Suka tambaye shi suka ce, “Malam, yaushe waɗannan za su faru? Kuma wace alama za tă nuna cewa suna dab da faruwa?”
Då frågade de honom, och sade: Mästar, när skall detta ske? Och hvad tecken är, när detta ske skall?
8 Ya amsa ya ce, “Ku lura, kada ku kuma a ruɗe ku. Gama da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ai, ni ne shi,’ da kuma, ‘Lokaci ya yi kusa.’ Kada ku bi su.
Sade han: Ser till, att I icke varden förförde; ty månge skola komma under mitt Namn, och säga: Jag äret; och tiden instundar. Följer dem icke efter.
9 Sa’ad da kuka ji labarin yaƙe-yaƙe, da juye juyen mulki, kada ku tsorota. Dole ne waɗannan abubuwa su fara faruwa, amma ƙarshen ba zai zo nan da nan ba.”
Men när I hören örlig och uppror, varer icke förfärade; ty sådant måste först ske, men det är icke straxt änden.
10 Sai ya ce musu, “Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki zai tasar wa mulki.
Och han sade till dem: Folk skall resa sig upp emot folk, och rike emot rike.
11 Za a yi manyan girgizar ƙasa, da yunwa, da annoba a wurare dabam-dabam, da kuma abubuwa masu bantsoro, da manyan alamu daga sama.
Och stor jordbäfning skall varda mångastäds, och hunger, och pestilentier; och förskräckelse, och stor tecken skola ske utaf himmelen.
12 “Amma kafin duk abubuwa nan, za a kama ku a tsananta muku. Za a kai ku majami’u, da kurkuku. Za a kuma kai ku gaban sarakuna da gwamnoni, kuma dukan waɗannan saboda sunana.
Men för allt detta skola de taga fatt på eder, och förfölja eder och öfverantvarda eder in på sin Råd, och i häktelse; dragande eder för Konungar och Förstar, för mitt Namns skull.
13 Wannan zai sa ku zama shaidu a gare su.
Och det skall eder vederfaras till ett vittnesbörd.
14 Amma ku yi ƙuduri, wato, ku shirya zuciyarku, a kan ba za ku damu ba kafin lokacin, game da yadda za ku kāre kanku.
Så håller det fast uti edor hjerta, att I ingen omsorg hafven, huru I skolen försvara eder;
15 Gama zan ba ku kalmomi, da hikima waɗanda ba ko ɗaya daga cikin maƙiyanku, za su iya tsayayya da ku, ko su ƙaryata.
Ty jag skall gifva eder mun och visdom, der alle de, som sätta sig emot eder, icke skola kunna emotsäga, ej heller emotstå.
16 Har iyayenku, da’yan’uwanku maza, da danginku, da abokanku ma, duk za su bashe ku, su kuma kashe waɗansunku.
I skolen ock öfverantvardas af föräldrar, och af bröder, fränder och vänner; och de skola döda somliga af eder.
17 Duk mutane za su ƙi ku saboda ni.
Och I skolen varda hatade af allom, för mitt Namns skull;
18 Amma ko gashi ɗaya na kanku, ba zai hallaka ba.
Och ett hår af edart hufvud skall icke förgås.
19 Ta wurin tsayawa da ƙarfi, za ku sami rai.
I skolen behålla edra själar genom edart tålamod.
20 “In kuka ga mayaƙa sun kewaye Urushalima, za ku sani rushewarta ya yi kusa.
När I nu sen, att Jerusalem varder belagdt med en här, då skolen I veta, att dess förödelse är för handen.
21 A lokacin nan, bari waɗanda suke Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu. Bari waɗanda suke cikin birnin kuma su fita, bari kuma waɗanda suke ƙauye kada su shiga birnin.
De då äro i Judeen, de fly upp åt bergen; och de der midt inne äro, de gånge ut; och de som ute i landet äro, de gånge icke derin;
22 Gama wannan shi ne lokacin hukunci, saboda a cika duk abin da aka rubuta.
Ty att då äro hämndadagarne, att fullbordas skall allt det som skrifvet är.
23 Zai zama abin kaito ga mata masu ciki, da mata masu renon’ya’ya, a waɗancan kwanakin! Za a yi baƙin ciki mai tsanani a ƙasar, da kuma fushi mai tsanani a kan mutanen nan.
Men ve dem som hafvande äro, och dem som dia gifva i de dagar; ty stor plåga varder på jordene, och vrede öfver detta folk.
24 Za a kashe su da takobi, a kuma ɗauke su’yan kurkuku, zuwa dukan al’ummai. Al’ummai za su tattaka Urushalima, har sai lokacin Al’ummai ya cika.
Och de skola falla för svärdsegg, och fångne bortförde varda till allahanda folk; och Jerusalem skall förtrampadt varda af Hedningom, tilldess Hedningarnes tid fullkomnad varder.
25 “Za a yi alamu a cikin rana, da cikin wata, da cikin taurari. A duniya, al’ummai za su yi baƙin ciki, su kuma rikice don tsoro, saboda ruri da kuma tafasar teku.
Och skola ske tecken i solen, och i månan, och i stjernorna; och på jordene varder folkena ångest, och de skola förtvifla. Och hafvet och vågen skola mycket bullra;
26 Mutane za su suma don tsoro, za su kuma yi fargaba, a kan abin da yake zuwa a bisan duniya, gama za a girgiza duniyar taurarin sararin sama.
Och menniskorna borttorkas, för räddhågas skull, deraf att de förbida det som hela verldena öfvergå skall; ty himmelens krafter skola bäfva.
27 A lokacin ne za su ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin girgije, da iko, da ɗaukaka mai girma.
Och då skola de få se menniskones Son komma i skyn, med magt och stora härlighet.
28 Sa’ad da waɗannan abubuwa sun fara faruwa, ku tashi tsaye, ku ɗaga kawunanku, domin fansarku yana matsowa kusa.”
Men då detta begynner ske, ser upp, och lyfter edor hufvud upp; ty då nalkas edor förlossning.
29 Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Ku dubi itacen ɓaure da dukan itatuwa.
Och han sade dem en liknelse: Ser på fikonaträt och all trä.
30 A duk lokacin da sun fara fitar da ganye, za ku gani da kanku, ku san cewa, damina ta yi kusa.
När de nu knoppas, kunnen I då se och veta af eder sjelf, att sommaren är när.
31 Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku sani mulkin Allah ya yi kusa.
Alltså ock I, när I sen detta ske, skolen I veta, att Guds rike är när.
32 “Gaskiya nake gaya muku, ba shakka, wannan zamani ba zai shuɗe ba, sai dukan waɗannan abubuwa sun cika.
Sannerliga säger jag eder: Detta slägtet skall icke förgås, förr än det allt skedt är.
33 Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.
Himmel och jord skola förgås; men min ord skola icke förgås.
34 “Ku lura fa don kada son jin daɗi na banza, da shaye-shaye, da damuwa na rayuwa su rinjayi zuciyarku, har ranar ta auko muku ba tsammani kamar tarko.
Men vakter eder, att edor hjerta icke förtungad varda med svalg och dryckenskap, och med detta lefvernes omsorg, så att den dagen kommer eder för hastigt uppå.
35 Gama za tă zo a kan kowa da yake kan dukan duniya.
Ty han varder kommandes, såsom en snara, öfver alla som bo på jordene.
36 Ku yi tsaro kullum, ku yi addu’a don ku iya kuɓuta daga dukan waɗannan abubuwa da suke kusan faruwa, don ku iya tsayawa a gaban Ɗan Mutum.”
Så vaker nu alltid, och beder, att I mågen undfly allt detta som komma skall, och stå för menniskones Son.
37 Kowace rana, Yesu yakan je haikalin ya yi koyarwa, da kowace yamma kuma, ya je ya kwana a kan tudun da ake kira Dutsen Zaitun.
Och han lärde om dagen i templet; men om natten gick han ut, och vistades på Oljoberget.
38 Da sassafe kuma, dukan mutanen suka zo haikalin, don su saurare shi.
Och allt folket var bittida uppe till honom i templet, till att höra honom.