< Luka 21 >
1 Da Yesu ya ɗaga ido, sai ya ga waɗansu masu arziki suna sa baikonsu a ma’ajin haikalin.
Pogledavši pa gor, videl je bogatine, da mečejo darove svoje v zakladnico.
2 Ya kuma ga wata gwauruwa matalauciya, ta saka anini biyu.
Videl je pa tudi eno vdovo ubogo, da je vrgla dva vinarja.
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina faɗa muku, wacce nan gwauruwa matalauciya ta sa fiye da dukan sauran.
Ter reče: Resnično vam pravim, da je ta uboga vdova vrgla več od vseh:
4 Dukan mutanen nan sun ba da baikonsu daga cikin arzikinsu ne, amma ita daga cikin talaucinta, ta saka duk abin da take da shi na rayuwa.”
Kajti vsi ti so vrgli od obilnosti svoje v dar Bogu, a ta je od uboštva svojega vrgla ves živež svoj, kterega je imela.
5 Waɗansu daga cikin almajiransa, suka fara magana a kan yadda aka yi wa haikalin ado da duwatsu masu kyau, da kuma kyautai da aka keɓe wa Allah. Amma Yesu ya ce,
In ko so nekteri pravili za tempelj, da je olepšan z lepim kamenjem in dragocenostmi, reče:
6 “Wannan abin da kuke kallo a nan, lokaci yana zuwa da ba za a bar wani dutse a kan wani dutse ba. Kowannensu, za a rushe shi.”
Prišli bodo dnevi, ko od tega, kar vidite, ne bo ostal kamen na kamenu, kteri ne bi razpadel.
7 Suka tambaye shi suka ce, “Malam, yaushe waɗannan za su faru? Kuma wace alama za tă nuna cewa suna dab da faruwa?”
In vprašajo ga, govoreč: Učenik, kedaj pa bo to? in kaj bo znamenje, kedar se ima to zgoditi?
8 Ya amsa ya ce, “Ku lura, kada ku kuma a ruɗe ku. Gama da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ai, ni ne shi,’ da kuma, ‘Lokaci ya yi kusa.’ Kada ku bi su.
On pa reče: Varujte se, da vas ne premotijo! kajti veliko jih bo prišlo v ime moje, in porekó: Jaz sem! in: Čas se je približal! Ne hodite torej za njimi.
9 Sa’ad da kuka ji labarin yaƙe-yaƙe, da juye juyen mulki, kada ku tsorota. Dole ne waɗannan abubuwa su fara faruwa, amma ƙarshen ba zai zo nan da nan ba.”
Kedar boste pa slišali vojske in vstaje, ne uplašite se; kajti to se mora najprej zgoditi: ali konca ne bo precej.
10 Sai ya ce musu, “Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki zai tasar wa mulki.
Tedaj jim je pravil: Vstal bo narod na narod, in kraljestvo na kraljestvo;
11 Za a yi manyan girgizar ƙasa, da yunwa, da annoba a wurare dabam-dabam, da kuma abubuwa masu bantsoro, da manyan alamu daga sama.
In veliki potresi bodo po krajih in lakote in kuge, groza in znamenja velika bodo na nebu.
12 “Amma kafin duk abubuwa nan, za a kama ku a tsananta muku. Za a kai ku majami’u, da kurkuku. Za a kuma kai ku gaban sarakuna da gwamnoni, kuma dukan waɗannan saboda sunana.
A pred vsem tem bodo položili roke svoje na vas, in preganjali vas bodo in izdajali v shajališča in ječe, in vodili pred kralje in poglavarje, za voljo imena mojega.
13 Wannan zai sa ku zama shaidu a gare su.
A to vam se bo zgodilo na pričevanje.
14 Amma ku yi ƙuduri, wato, ku shirya zuciyarku, a kan ba za ku damu ba kafin lokacin, game da yadda za ku kāre kanku.
Položite torej v srce svoje, da ne skrbite naprej, kako se boste zagovarjali;
15 Gama zan ba ku kalmomi, da hikima waɗanda ba ko ɗaya daga cikin maƙiyanku, za su iya tsayayya da ku, ko su ƙaryata.
Kajti jaz vam bom dal usta in modrost, kterej ne bodo mogli nasprotovati, ne upirati se vsi nasprotniki vaši.
16 Har iyayenku, da’yan’uwanku maza, da danginku, da abokanku ma, duk za su bashe ku, su kuma kashe waɗansunku.
Izdajali vas bodo pa tudi roditelji in bratje in sorodniki in prijatelji, in nektere od vas bodo umorili.
17 Duk mutane za su ƙi ku saboda ni.
In sovražili vas bodo vsi za voljo imena mojega.
18 Amma ko gashi ɗaya na kanku, ba zai hallaka ba.
Pa las z glave vam ne bo poginil.
19 Ta wurin tsayawa da ƙarfi, za ku sami rai.
H potrpljenjem svojim pridobivajte duše svoje.
20 “In kuka ga mayaƙa sun kewaye Urushalima, za ku sani rushewarta ya yi kusa.
Kedar boste pa videli, da Jeruzalem oblega vojska, tedaj vedite, da se je približalo razdejanje njegovo.
21 A lokacin nan, bari waɗanda suke Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu. Bari waɗanda suke cikin birnin kuma su fita, bari kuma waɗanda suke ƙauye kada su shiga birnin.
Tedaj naj, kteri so v Judeji, odbežé na gore: in kteri so sredi njega, izidejo naj na polje; in kteri so na polji, naj ne hodijo va-nj.
22 Gama wannan shi ne lokacin hukunci, saboda a cika duk abin da aka rubuta.
Kajti ti dnevi bodo dnevi maščevanja, da se izpolnijo vsa pisma.
23 Zai zama abin kaito ga mata masu ciki, da mata masu renon’ya’ya, a waɗancan kwanakin! Za a yi baƙin ciki mai tsanani a ƙasar, da kuma fushi mai tsanani a kan mutanen nan.
Gorjé pa nosečim in doječim v tistih dnéh; kajti velika nadloga bo na zemlji, in jeza nad tem narodom.
24 Za a kashe su da takobi, a kuma ɗauke su’yan kurkuku, zuwa dukan al’ummai. Al’ummai za su tattaka Urushalima, har sai lokacin Al’ummai ya cika.
In padali bodo od ostrice meča, in gonili jih bodo v sužnost po vseh narodih, in Jeruzalem bodo gazili pogani, dokler se ne izpolnijo časi poganov.
25 “Za a yi alamu a cikin rana, da cikin wata, da cikin taurari. A duniya, al’ummai za su yi baƙin ciki, su kuma rikice don tsoro, saboda ruri da kuma tafasar teku.
In znamenja bodo v solncu, in mesecu in zvezdah, in narodom na zemlji žalost od obupa, šuma morskega in valovja;
26 Mutane za su suma don tsoro, za su kuma yi fargaba, a kan abin da yake zuwa a bisan duniya, gama za a girgiza duniyar taurarin sararin sama.
Ludjé bodo mrli od strahu in pričakovanja tega, kar ima na zemljo priti: kajti sile nebeške se bodo pregibale.
27 A lokacin ne za su ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin girgije, da iko, da ɗaukaka mai girma.
In tedaj bodo ugledali sina človečjega, da gre na oblaku z veliko močjó in slavo.
28 Sa’ad da waɗannan abubuwa sun fara faruwa, ku tashi tsaye, ku ɗaga kawunanku, domin fansarku yana matsowa kusa.”
Ko se bo pa to jelo goditi, ozrite se gor in povzdignite glave svoje, ker se približuje odrešenje vaše.
29 Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Ku dubi itacen ɓaure da dukan itatuwa.
In pové jim priliko: Poglejte smokvo in vse drevje.
30 A duk lokacin da sun fara fitar da ganye, za ku gani da kanku, ku san cewa, damina ta yi kusa.
Kedar vidite, da je uže pognalo, sami véste, da je pomlad uže blizu.
31 Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku sani mulkin Allah ya yi kusa.
Tako tudi vi, ko boste videli, da se to godí, védite, da je blizu kraljestvo Božje.
32 “Gaskiya nake gaya muku, ba shakka, wannan zamani ba zai shuɗe ba, sai dukan waɗannan abubuwa sun cika.
Resnično vam pravim, da ne bo prešel ta rod, dokler se vse ne zgodí.
33 Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.
Nebo in zemlja bosta prešla, a besede moje ne bodo prešle.
34 “Ku lura fa don kada son jin daɗi na banza, da shaye-shaye, da damuwa na rayuwa su rinjayi zuciyarku, har ranar ta auko muku ba tsammani kamar tarko.
Varujte se pa, da vam ne otežajo srca s požrešnostjo in pijanstvom in skrbmí tega sveta, in vam ne pride ta dan iznenada.
35 Gama za tă zo a kan kowa da yake kan dukan duniya.
Kajti prišel bo kakor zanka na vse, kteri prebivajo na lici vse zemlje.
36 Ku yi tsaro kullum, ku yi addu’a don ku iya kuɓuta daga dukan waɗannan abubuwa da suke kusan faruwa, don ku iya tsayawa a gaban Ɗan Mutum.”
Čujte torej vsak čas, in molite, da bi bili vredni ubežati vsemu temu, kar se ima zgoditi, in pred sinom človečjim stati.
37 Kowace rana, Yesu yakan je haikalin ya yi koyarwa, da kowace yamma kuma, ya je ya kwana a kan tudun da ake kira Dutsen Zaitun.
In po dnevi je učil v tempeljnu; a po noči je izhajal prenočevat na goro, ktera se imenuje Oljska.
38 Da sassafe kuma, dukan mutanen suka zo haikalin, don su saurare shi.
In dohajalo je vse ljudstvo zgodaj k njemu v tempelj poslušat ga.